Aminiya:
2025-03-17@10:45:58 GMT

Gidauniyar Dangote ta ƙaddamar da rabon abincin N16bn ga talakawan Nijeriya

Published: 17th, March 2025 GMT

Gidauniyar Aliko Dangote, a cikin shirye-shiryenta na 2025, na bayar da tallafin abinci ga ‘yan Nijeriya, ta ƙaddamar da rabon abinci, inda ta ware kimanin Naira Biliyan 16 domin tallafa wa talakawa ‘yan Nijeriya masu ƙaramin ƙarfi da kuma masu nakasa.

Shirin da fiye da mutum miliyan ɗaya ne za su rabauta da tallafin buhunhunan shinkafa mai nauyin kilo 10 daga wannan tsarin na gidauniyar Aliko Dangote.

NAJERIYA A YAU: Guraben Ayyukan Da Aka Kasa Cikewa A Najeriya El-Rufai ya nemi afuwa ko mu maka shi a kotu — Gidauniyar Ɗahiru Bauchi

Da yake jawabi a wajen taron kaddamarwar, Shugaban gidauniyar Aliko Dangote, Alhaji Aliko Dangote, ya ce an tsara yin rabon shinkafar buhu miliyan ɗaya ne ga ‘yan Nijeriya a ƙananan hukumomi 774 na faɗin kasar nan, kamar yadda yake a tsarin kamfani da kuma gidauniyarsa na nuna jin-kai ga al’umma ƙasar nan.

Dangote, wanda ya samu wakilcin yarsa, Hajiya Mariya Aliko Dangote, ya ce: shirin na wannan shekara, an yi shi ne da nufin nuna tausayi da jinkai da nuna kulawa wajen taimakon jama’a bisa la’akari da halin da ake ciki na matsin rayuwa da durkushewar tattalin arziki.

Ya ce gidauniyar ta fara kaddamar da rabon tallafin ne a Jihar Kano, sannan nan gaba za a ci gaba da rabawa sauran jihohi, domin tabbatar da ganin cewa abincin ya isa hannun wadanda aka yi domin su a daukacin kananan hukumomin kasar nan.

Alhaji Dangote, ya ce sun hada kai da gwamnatin jihar ne wajen tabbatar da ganin an raba abincin ga mabukata a kowace jiha dake fadin Nijeriya.

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf wanda ya jagoranci kaddamar da rabon tallafin abincin a matakin kasa na wannan shekara, ya ce aiwatar da wannan shiri ya nuna tsantsar halin nuna jinkai da kulawar da Alhaji Aliko Dangote yake yi,wajen kawar da yunwa da fatara a Nijeriya.

Gwamnan wanda mataimakinsa, Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo ya wakilta, ya ce za a raba buhun shinkafar guda dubu 120, mai nauyin kilo 10 a ɗaukacin ƙananan hukumomi 44 da ke faɗin Jihar Kano.

Da take jawabi ga manema labarai, Babbar Darakta kuma Babbar jami’ar gudanarwar gidauniyar Aliko Dangote, Zouera Youssoufou ta ce an tsara shirin ne a matsayin wata hanya ta tallafa wa gwamnatoci wajen yaƙi da talauci da yunwa a Nijeriya.

Mukaddashin Babban Kwamandan Hisbah na Jihar Kano, Dokta Mujahid Aminudden ya gode wa gidauniyar ta Dangote kan bijiro da wannan shiri, inda ya roki sauran ‘yan Nijeriya da suyi koyi da halin Dangote.

Ya ce Hukumar Hisbah za ta tsaya tsayin daka wajen ganin tallafin yaje hannun waɗanda suka cancanta.

Wani da ya yi magana a madadin wadanda suka ci gajiyar tallafin mai suna Malam Ibrahim Ahmed ya yaba wa Alhaji Aliko Dangote, inda ya yi addu’ar Allah Ya ci gaba da taimakonsa a harkokinsa na kasuwanci.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gidauniyar Dangote Jihar Kano gidauniyar Aliko Dangote yan Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Cikar FRCN Shekaru 63: An Bukaci Gwamnonin Jihohin Arewa Su Tabbatar Da Dorewar Gidan Rediyon

An yi kira ga gwamnatocin jihohin Arewacin Najeriya da su tabbatar da dorewar tashar Rediyon Nigeria (FRCN) Kaduna a matsayin abim tunawa da marigayi Firimiyan  tsohuwar jihar Arewa, Alhaji Sir Ahmadu Bello, Sardaunan Sokoto, ya bari.

Masu sauraron tashar sun yi wannan kira a cikin bayanai daban-daban yayin da suke tsokaci kan bikin cika shekaru 63 da kafuwar gidan rediyon a watan Maris na shekarar 1962.

Sun bayyana godiyarsu ga rawar da FRCN Kaduna ya taka tsawon shekaru duk da kalubalen aiki, wanda suka bukaci mahukunta su magance.

A sakon taya murna daban da suka aiko, Sanata Salisu Musa Matori, da Alhaji Umar Dembo, da Alhaji Umar Iya Gulak, da Alhaji Garba Baba da Alhaji Muhammad Damak Abubakar, sun jinjinawa gidan rediyon  bisa bajintar da ya nuna, inda suka jaddada bukatar Gwamnatin Tarayya ta cika alkawuran da ta dauka na farfado da tashar.

Jami’in hulɗa da jama’a na Kungiyar Manoma ta Najeriya, Alhaji Muhammad Magaji, ya nuna matukar jin dadinsa kan yadda tashar ke tallafawa harkokin noma, zaman lafiya, hadin kai, da cigaban kasa. Yana mai kira da a cigaba da wannan yunkuri don cimma manufofin da aka sanya a gaba.

 

Daga Suleiman Kaura.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • El-Rufai ya nemi afuwa ko mu maka shi a kotu — Gidauniyar Ɗahiru Bauchi
  • Cikar FRCN Kaduna Shekaru 63: An Bukaci Gwamnonin Arewa Su Tabbatar Da Dorewar Gidan Rediyon
  • Cikar FRCN Shekaru 63: An Bukaci Gwamnonin Jihohin Arewa Su Tabbatar Da Dorewar Gidan Rediyon
  • Sojoji sun hallaka shugabannin ’yan bindiga 2 da wasu a Katsina 
  • Fitar Da Nama Zuwa Saudiyya: Mayankar Dabbobi Ta Jurassic Ta Yi Hadin-gwiwa Da Shirin CDI
  • NPA Za Ta Yunkuro Don Zamanantar Da Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya – Dantsoho
  • Na Cire Tallafin Mai Ne Domin Kare Makomar Matasan Nijeriya —Tinubu
  • Dangote Da NNPCL Sun Koma Teburin Tattaunawa Kan Cinikin Danyen Mai A Kan Naira
  • Gidauniyar Dangote Ta Kaddamar Da Rabon Abinci Na Naira Biliyan 16 Ga Talakawan Nijeriya