Tsofaffin furodusoshin Kannywood da aka daina jin ɗuriyarsu
Published: 18th, March 2025 GMT
Masana’antar Kannywood ta dade tana nishaɗantar da al’umma, musamman Hausawa da sauran kabilun Arewacin Najeriya.
A makon jiya Aminiya ta ruwaito a cewa kasuwancin fina-finan ya samu koma-baya matuƙa, wanda hakan ya sa wasu suke nuna yatsa ga furodusohin yanzu kan gaza shirya fim ɗin da za a iya haskawa a Netflix da sauran manyan hanyoyin nuna fina-finai da za su samar wa masana’antar kuɗin shiga.
Wannan ya sa Aminiya ta yi waiwayen wasu furodusohin da aka daina jin ɗuriyarsu a masana’antar.
Salisu Galadanchi – Shi ne Daraktan Fim din Turmin Danya, fim na farko a Kannywood, ya yi ritaya daga aikin gwamnati a Gidan Talabijin na CTV, yana zaune a Kano.
Umar Sheikh Mohammed: Shi ne mai Kamfanin Godiya and Dan Hassan wanda ya shirya fina-finan barkwanci, shi ma ya yi nukusani.
Bala Ahmed: Ana kiransa da Bala Sarauniya saboda rawar da ya taka wajen shiryawa da gabatar da finafinan Kamafanin Sarauniya Films a Kano.
Auwalu Mohammed Sabo shi ne Furodusan Kamfanin Sarauniya Films wanda suka yi finafinan gargajiya irin su Sangaya da Daskindaridi da Linzami da Wuta da sauransu. Yanzu yana aiki a Majalisar Dokokin Jihar Kano.
Ali Jindos Aneesa: Tsohon mai daukar hoto na masana’antar, wanda ya koma shirya fim. Shi ya kawo Saratu Daso Kannywood a inda ya sa ta a fim din sa Feleke.
Habibu Sani: Tsohon mai shirya finafinai na Kamfanin K Films Multi Services, kuma tsohon ma’aikacin Hukumar Tarihi da Al’adun Gargajiya ta Jihar Kano, shi ne Furodusan Saki Reshe 2 da Reshe Ya Juye da Mujiya 1 da na 2. Shi ne kuma ya jagoaranci Kungiyar AHFIP a zamanin Abubakar Rabo.
Auwalu Isma’il Marshal: Tsohon Shugaban Kungiyar Tumbin Giwa da ta koma Tumbin Giwa Films, ya jagoranci shirin finafinai, yanzu kuma Shugaban Kungiyar Dattawan Kannywood.
Adamu Mohammed. Shi ne mai Kamfanin Kwabo Films, wanda ya yi fim din Kwabon Masoyi daga littafinsa mai wannan suna da kuma Dan Almajiri na 1 da na 2.
Umar Bawa Dukku: Shi ne mai Kamfanin Dukku Productions wanda ya shirya finafinan barkwannci da dama. Shi ne kuma wanda ya fara buga fim a faifan SIDI da fim din sa mai suna Zainab a lokacin ana sakin finafinai a kaset.
Hamisu Lamido Iyan Tama: Shi ne mai Kamfanin Iyan Tama Multimedia, finafinan Gashin Kuma da Kilu Ta Ja Bau, na daga cikin finafinan da kamfaminsa ya shirya, baya ga buga wakoki na sauran finafinai da kuma fito da Ali Baba Yakasai wanda ya fara buga wa Rarara kida.
Abubakar A. S. Mai Kwai: Shi ne mai Kamfanin Mai Kwai Mobies, inda ya shirya kuma ya dauki nauyin finafinai irinsu Kona Gari, Munafikin Mata da sauransu.
Abdullahi Maikano: Mazaunin garin Kaduna ne, ya yi suna a shirya finafinai a baya, ya taba zama Shugaba Kungiyar MOPPAN
Yakubu Lere: Fitaccen furodusa da ya yi fim din Wasila na 1 da na 2 a karkashin kamfaninsa na Lerawa Films da kuma wasu finafinan. Ya taba zama mai ba Gwamnan Jihar Kaduna Shawara kan Harkar Yada Labarai.
Aminu Hudu: Mai Kamfanin ALMAH Productions, tsohon furodusa ne da ke garin Jos ya yi suna a harkar sayar da kaset kafin ya koma shirin fim a shekarun 1990.
Rabi’u HRB: Shi ne mai Kamfanin HRB Films mai ofishi a Kano daga baya ya koma Kaduna. Ya yi finafinai da yawa a ciki har Gyale da kuma Abin Sirri Ne.
Ibrahim Dahiru: Shi ne mai Kamfanin 3SP a Jos, ya yi finafinai da dama a karkashin kulawar Abubakar da kuma Shehu.
Bala Anas Babinlata: Koda yake an fi saninsa a harkar rubutu da kuma bayar da umarni, amma ya yi finafinai na kansa a karkashin kamfaninsa Babinlata Films Sarma-Sarma na daya daga cikinsu.
Hajiya A’isha Halilu: Tana daya daga cikin furudusoshi mata da ake ji da su a da.fim din Sahnafahna, daya daga cikin finafinanta da suka yi tashe a karkashin kamfaninta na Kumbo Productions.
Sani Mu’azu: Koda yake ya yi fice a shirye-shiryen talabijin inda yake fitowa a matsayin jarumi, Kamfaninsa na Lenscope Media da ke Jos ya kwanta dama a harkokin Kannywood. A baya sun yi finafinai da kuma samar da mawaka a masana’antar.
Alhaji Ibrahim Mandawari: Shi ne shugaban Kamfanin Mandawari Enterprises da ya shirya finafinai da dama irin su Zakaran Gwajin Dafi da Marainiya da Gaskiya Dokin Karfe.
Aminu Mirror: Aminu Mirror fitaccen furodusa ne a Zaria, wanda ya yi fice musamman a tsakanin 2000s, sai dai an dain jin ɗuriyarsa tun rasuwar abokinsa Ahmed S. Nuhu. Daga cikin finafinan da ya shira a Kamfanin Ijaba Productions akwai Ibro Police da Sirri ne.
Sai ya sake dawowa a fim din Gidan Badamasi mai dogon zango a matsayin Malam Zaidu.
Aminu Bizi: Shi ne Shugaban Kamfanin Bizi Productions, kuma ya shirya finafinai irinsu tsohon dan siyasa da Baba Ari ya ja da sauransu.
Ahmed Bifa: Shugaban Kamfanin Bifa Productions. Ya shirya finafinai irinsu Kyandir da Bakar fuska.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: fina finan Kannywood Hamisu Iyantama Ibrahim Mandawari kannywood a shirya finafinai a masana antar da ya shirya a karkashin
এছাড়াও পড়ুন:
Tsohuwar ɗaliba ta kai ƙarar makarantar da ta kammala
Wata matashiya mai suna Aleysha Ortiz ’yar shekara 19 da ke Jihar Connecticut a Amurka ta dauki matakin shari’a a kan tsohuwar makarantar sakandaren gwamnatin da ta yi saboda gazawarta ta hanyar ba ta damar kammala karatu “da sakamako mai daraja” duk da ta kasance maras ƙoƙari.
A watan Yunin shekarar bara ce, Aleysha Ortiz ta kammala karatu a Makarantar Hartford Public High School da ke Hartford, a Jihar Connecticut, inda aka karama ta, har ma ta samu gurbin karatu a kwaleji, amma yanzu ta kai karar tsohuwar makarantarta saboda sakacinta.
Gidauniyar Dangote ta ƙaddamar da rabon abincin N16bn ga talakawan Nijeriya EFCC ta kama Murja Kunya kan wulaƙanta takardun NairaMatashiyar mai shekara 19 tana zargin makarantar da ta kammala da yin watsi da karatunta, tana mai cewa da ƙyar za ta iya riƙe fensir a hannunta kuma ƙoƙarin karatunta ya yi kama da na dalibi ɗan aji daya.
An haife ta a garin Puerto Rico, Aleysha tana fama da matsalolin koyo tun tana karama, kuma dabi’arta ta ci gaba bayan ta yi ƙaura zuwa Amurka tana ’yar shekara 5.
Ta yi iƙirarin cewa, makarantarta da kuma malaminta na musamman da aka ba ta ba su da wani amfani har sai wata guda kafin ta kammala karatunta a zango na ƙarshe lokacin da suka gudanar da ƙarin gwajin da take nema kuma suka gane cewa ba ta da ƙoƙari.
Jami’an hukumar makarantar sun shaida wa matashiyar cewa, za ta iya jinkirta karɓar takardar shaidar kammala karatunta na difiloma don sauya su da wasu ayyuka. Amma ta ƙi amincewa.
Ortiz ta bayyana wa CNN cewa, “Na yanke shawarar shigar da ƙara, yanzu lokacina ne,” inda ta ƙara da cewa, kammala karatunta da karramawa daga makarantar sakandare Hartford Public High School, wanda yawanci yana nufin ɗalibi ya nuna ƙwarewa a fannin ilimi.
Amma ta yaya Aleysha Ortiz za ta kammala karatun sakandare tare da karramawa yayin da ba ta iya karatu da rubutu ba? Ta yaya aka karɓe ta zuwa Jami’ar Connecticut?
Ta yi iƙirarin cewa, manhajojin zamani suna matuƙar taimakawa. Tana amfani da manhajojin wayar hannu don fassara rubutu zuwa murya da murya zuwa rubutu, har ma ta yi amfani da su wajen aikace-aikacen kwalejin da rubuce-rubucen da ake bukata. Kasancewarta ɗalibai kwalejin ya saka ta cikin yanayi na daban-daban.
Aleysha ta yarda cewa, inda ta daina zuwa ajin karatu a farkon Fabrairu. Ta so ta ɗauki lokaci don kula da lafiyar ƙwaƙwalwarta, amma tana fatan komawa azuzuwa nan ba da jimawa ba.
Aleysha ta ce, ta kai ƙarar tsohuwar makarantarta ce saboda tana son a tuhumi shugabanninta kan abin da ta fuskanta.
Ta yi ikirarin cewa, “ba su san abin da suke yi ba kuma ba su damu ba,” kuma tana fatan cewa, fafutukar da take yi a shari’ar zai hana wasu matasa rashin samun cikakken ilimi.
“Ni mutum ce mai matukar sha’awar karatu kuma ina son koyo,” in ji Ortiz.
“Mutane sun yi amfani da wannan damar don koyo, kuma yanzu ina kwaleji kuma ina so in yi amfani da wannan.”