An gudanar da Sallar Juma’a a mako na uku na watan Ramadan a Masallacin Al-Aqsa, duk kuwa da tsauraran takunkumin da gwamnatin yahudawan sahyoniya ta dauka, tare da halartar Palasdinawa 80,000.

Kamfanin dillancin labaran Al-Naba y bayar da rahoton  cewa, dubun dubatar Falasdinawa ne suka gudanar da sallar Juma’a ta uku na watan Ramadan a masallacin Al-Aqsa, duk da matakai na kawo cikas da sojojin mamaya na Haramtacciyar Kasar Isra’ila suka dauka da kuma yanayin sanyi da ruwan sama a birnin Kudus.

Hukumar kula da lamurran addinin Musulunci a birnin Kudus ta bayar da bayanin cewa, masallata 80,000 ne suka gudanar da sallar Juma’a ta uku na watan Ramadan a masallacin Al-Aqsa.

Sheikh Khalid Abu Juma, limamin masallacin Al-Aqsa, ya ce a cikin hudubar sallar: “Watan Ramadan yana kawo azama da azama a cikinmu; Musulmai sun bar al’adun da suka saba a cikin saurin watanni; Suna nisantar da kansu daga al’adun da suka saba, tare da karfafa ayyukan tsarkeke ruhi da kusanci ga Allah.

Abu Juma ya jaddada cewa azumi yana karfafa nufi da kuma inganta azama, ya kara da cewa: Imani da azama suna da alaka da ruhi.

Ya ce: Yunkurin da makiya suke yi na rusa zaman lafiya da kwanciyar hankali ya sabawa koyarwar addinin muslunci da dukkanin addinai da aka saukar daga sama.

Sannan kuma ya yi ishara da abin da ke faruwa a Gaza, yana bayyana shi a matsayin aiwatar da wani mummunan kudiri na makiya a kan al’ummar musulmi na Gaza da ma Falastinu baki daya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Ramadan a masallacin Al Aqsa sallar Juma a

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Zata Yaye Labulen Ire-Iren Makamanta Na Musamman Da Ta Mallaka Domin Kare Kai

Kwamandan rundunar sojojin kasa ta Iran ya bayyana cewa: Nan ba da jimawa ba za a yaye labulen ire-iren makamai na musamman da Iran ta mallaka

Kwamandan rundunar sojin kasa ta Iran Birgediya Janar Kiomars Heidari ya yi nuni da shirin rufe kan iyakar kasar da ke gabashin Iran, yana mai cewa: Wannan ba kawai wata katanga ba ce mai tsayin mita 4, saboda an tanadar da ita ce da nau’o’in makamai masu kwaloluwar ci gaba na zamani a duniya, wannan shiri an gudanar da shi ne tsawon shekaru hudu kuma za a kammala shi nan da shekaru uku masu zuwa.

Kwamandan rundunar sojin kasa ta Iran ya jaddada haka ne a wani taron manema labarai da ya gudanar a yau Lahadi cewa, yana mai cewa; An bullo da sauye-sauye ne ga tsarin rundunar sojojin kasa baki daya, don ba da damar wuce tsohon tsari saboda kai wa ga tsari na zamani da zai iya tunkarar kalubalen da ake fuskanta a yau.

Birgediya Janar Haidari ya yi jawabi kan muhimman sauye-sauye a cikin tsari da makaman da sojojin kasa suka samar, yana mai cewa, “Sun mayar da bukatu na yau da kullum zuwa wani rundunar kai hari cikin gaggawa mai saurin mayar da martani.

Ya kara da cewa, “Wannan runduna ta mallaki karfin motsawa 100%, da karfin kai hari 100%, da kuma juriya 100%. Don cimma wannan buri, suna bukatar makamai na musamman wadanda ke dauke da wadannan siffofi guda biyu.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Ce Za’a Gudanar Da Zagaye Na Gaba Tsakaninta Da Amurka Ne A Birnin Roma Na Kasar Italiya
  • Hukumar OCHA Ta Bayyana Cewa Yahudawan Sahyoniyya Sun Ninninka Ayyukan Korar Falasdinawa A Yamma Da Kogin Jordan
  • Iran Zata Yaye Labulen Ire-Iren Makamanta Na Musamman Da Ta Mallaka Domin Kare Kai
  • Al’ummar Mauritaniya Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Nuna Adawa Da Yakin Gaza
  • ’Yan bindiga sun kona masallacin Juma’a da asibiti da gidaje da Zamfara
  • Dagewa Iran Takunkuman Zalunci Na Daga Cikin Manufofin Tattaunawa Da Amurka: Aref
  • Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya godewa ministan harkokin wajen kasar Omman
  • Kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa na fatan nasara ga tattaunawar Amurka da Iran
  • Iran da Amurka zasu ci gaba da tattaunawa a mako mai zuwa
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 108