Aminiya:
2025-04-13@09:47:05 GMT

An ayyana zaman makoki na kwana uku bayan kashe mutum 44 a Nijar

Published: 22nd, March 2025 GMT

Gwamnatin Nijar ta ayyana zaman makoki na kwana uku bayan an kashe fararen hula 44 a kudu maso yammacin ƙasar a wani hari da “yan ta’adda” da ke da alaƙa da ƙungiyar ta’addanci ta Daesh suka kai.

Ma’aikatar harkokin cikin gida ta ƙasar ce ta bayyana hakan a wata sanarwa da ta fitar a gidan talabijin na ƙasar a ranar Juma’a.

An yi wa wata karya tiyatar ceton rai Za a hukunta ma’auratan da suka ci zarafin yarinya a kan mangwaro — Zulum

Sanarwar ta ce ‘yan ta’addan sun kashe fararen hular ne a lokacin da suka afka cikin wani masallaci a ƙauyen Fombita da ke Kokorou inda suka far wa masallata.

Ma’aikatar ta yi Allah-wadai da harin inda ta kira shi da hari na “rashin imani” tare da shan alwashin ƙara matsa ƙaimi domin yaƙi da ta’addanci a yankin.

Zaman makokin da gwamnatin ta Nijar ta sanar na awa 72 zai fara aiki ne daga ranar Asabar domin girmama waɗanda suka rasu.

Za a ɗaga tutocin Nijar rabi a faɗin ƙasar, haka kuma za a dakatar da taruka a daidai lokacin da ƙasar ke cikin makoki.

Yankin kudu maso yammacin Jamhuriyar Nijar, musamman yankunan da ke kusa da kan iyaka da Mali da Burkina Faso, na fuskantar tashe-tashen hankula a ‘yan shekarun nan, inda ƙungiyoyi irin su Daesh ke amfani da rashin zaman lafiya wajen kai munanan hare-hare kan ƙauyuka da jami’an tsaro.

Harin dai ya nuna ƙalubalen tsaro da ƙasar da ke yankin Sahel ke fuskanta, duk kuwa da ƙoƙarin da gwamnati da ƙawayenta na ƙasa da ƙasa suke yi na daƙile ayyukan tada ƙayar baya.

Kawo yanzu dai babu wata kungiya da ta ɗauki alhakin kai harin, ko da yake ma’aikatar harkokin cikin gidan ƙasar ta danganta shi da Daesh saboda kasancewar ƙungiyar a yankin.

Hukumomin ƙasar dai sun yi alƙawarin gudanar da cikakken bincike tare da ɗaukar ƙwararan matakai domin gurfanar da waɗanda suka aikata laifin a gaban kuliya.

Kashe-kashen na baya-bayan nan na ƙara yawan asarar rayukan fararen hula a Nijar, inda al’ummomi ke ci gaba da fuskantar barazanar tashe-tashen hankula.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: fararen hula Nijar

এছাড়াও পড়ুন:

An kashe ƙasurgumin ɗan bindiga Gwaska da mayaƙa 100 a Katsina

Jami’an tsaro sun samu nasarar kashe wani ƙasurgumin ɗan bindiga da ake kira Gwaska Ɗan Ƙarami da wasu mayaƙa 100 a Jihar Katsina.

Kwamishinan Harkokin Cikin Gida na Jihar Katsina, Dokta Nasir Mu’azu ya bayyana matakin a matsayin wata gagarumar nasara a yaƙi da ’yan bindiga ake yi a jihar.

An kama mutum 8 kan faɗan daba a Kano Ziyarar da Atiku ya kai wa Buhari ba ta dami APC ba — Ganduje

“Abin farin ciki ne ga jihar, domin wannan nasara ta taimaka wajen wargaza ayyukan ’yan bindigar da ke addabar garuruwa da ƙauyukan da ke ƙananan hukumomin Faskari da Kankara da Bakori da Malumfashi da kuma Kafur,” in ji Kwamishinan.

Ya bayyana cewa runduna ta 17 ta sojin Nijeriya tare da ɓangaren sojin saman ƙasar ne suka ƙaddamar da hare-haren a ranar 10 ga watan Afrilun shekarar 2025 a dabar ɓarayin daji a Mununu Bakai da Zango da Jeka Arera da Malali, da kuma Ruwan Godiya duka a cikin ƙananan hukumomin Kankara da Faskari.

Haɗin gwiwar jami’an tsaron ƙasar ne suka ƙaddamar da harin a ranar Juma’a wanda ya yi sanadin kisan Gwaska — wanda ya kasance mataimakin shahararren ɗan bindiga Malan, shugaban ISWAP a yankin Arewa Maso Yamma.

“Hare-haren da suka yi daidai kan ɓarayin, bisa bayanan sirrin da aka samu, sun yi silar kashe wani wanda ake nema ruwa-a-jallo da aka fi sani da Gwaska, wanda mataimaki ne ga wani shugaban ’yan bindiga mai alaƙa da ISWAP,” in ji shi.

“Bayanan sirri sun tabbatar da cewa kwanan nan ne Gwaska ya yi ƙaura daga Ƙaramar Hukumar Danmusa zuwa dajin Munumu.

Rahotonni sun ce sojojin sun lalata maɓoyar ’yan bindigar da dama a sassan jihar a lokacin harin, tare da ƙwato da kuma lalata wasu manyan bindigogi masu jigida da waɗanda aka ƙera a cikin gida.

Harin na zuwa ne bayan da a farkon mako ’yan bindigar suka yi garkuwa da mutum 43 mazauna ƙauyukan Maigora da ke yankin Ƙaramar Hukumar Dandume.

Kazalika, dakarun tsaro sun ƙaddamar da wani aiki da sanyin safiyar ranar 10 ga watan Afrilun shekarar 2025, a hanyar da ɓarayin daji ke bi a Dutsen Wori gefen hanyar Dandume zuwa Kandamba, da ke wajen garin Dandume a kan iyaka da ƙananan hukumomin Faskari da Sabuwa.

Aikin da aka aiwatar da misalin ƙarfe 3:45 na dare ya yi silar kashe ɓarayi shida ciki har da shugabansu, yayin da sauran ɓarayin suka tsere da raunukan bindiga.

Bayanai sun nuna cewa dakarun sun ƙwace mashina bakwai yayin da saura huɗu suka tsere cikin daji.

An bi sawun ɓarayin ne daga dabarsu da ke Maigora/Doroyi cikin Ƙaramar Hukumar Faskari.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fashewar bam a mota ta kashe mutum takwas a Borno
  • Sama da mutane 1,560 ne sukayi shahada tun bayan da Isra’ila ta koma kai farmaki Gaza
  • ‘Tell Your Papa’: NBC ta haramta amfani da waƙar da ke sukar Tinubu
  • An kashe ƙasurgumin ɗan bindiga Gwaska da mayaƙa 100 a Katsina
  • An kama mutum 8 kan faɗan daba a Kano
  • Yadda bom ya tashi da ɗan gwangwan a Legas
  • Mutane Da Yawa Sun Jikkata Bayan Fashewar Bam A Wata Kasuwa A Ikeja
  • Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro
  • NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi
  • An kashe mutum kan zargin satar kare a Bauchi