Leadership News Hausa:
2025-04-14@16:55:27 GMT

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [15]

Published: 23rd, March 2025 GMT

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [15]

● Ta biyu, yana nuna rashin ladabi ga Allah, domin ainihin hassada ita ce jin haushin yadda Allah Ya ba wa wani ni’ima, kuma hakan yana nufin yana sukar hukuncin Allah.

● Ta uku, zuciyarsa tana shan wahala saboda yawan damuwa da baƙin ciki.”

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [14] Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [13]

Fashin Baƙi:

Ibn Juzai Allah Ya ji ƙan sa, ya yi cikakken bayani kan illolin hassada ga mai hassada ta hanyoyi guda uku: samun zunubi, da rashin ladabi ga Allah, da wahalar da zuciya.

Zan ɗan yi bayani a kan waɗan gaɓoɓi guda uku da malam ya ambata, tare da hujjoji daga Alƙur’ani, da Hadisi, da mahangar masana ilimi. Ga maganar kamar haka:

Hassada Zunubi Ce Kuma Haramun Ce a Shari’a:

A Musulunci, hassada tana daga cikin manyan zunubai. Dalili kuwa shi ne cewa tana ƙunshe da ƙiyayya da kishi mara dalili. Allah Maɗaukakin Sarki Ya ce:” Shin yanzu za su riƙa yi wa mutane hassada ne a kan abin da Allah Ya ba su na falalarsa?” Suratun Nisã’i aya ta 54. Ma’anar wannan aya ita ce: idan mutum yana jin haushin wani saboda wata ni’ima da Allah Ya ba shi, to yana fuskantar hukuncin Allah da kishi maras tushe. Haka nan Annabi (SAW) ya fadi a cikin hadisi cewa: “Kada ku yi hassada“ Bukhari da Muslim ne ya ruwaito.

Me Yasa Hassada Take Zama Zunubi?

Hassada ta zama zunubi ne ta fuskoki masu yawa.

• Akwai saɓa wa Allah da Manzonsa (S.A.W) na hani a kan hassada.
• Hassada tana sa mutum ya yi mummunan zato ga Allah, yana ganin kamar bai dace Allah Ya ba wani wata ni’ima ba.
• Hassada tana iya sa mutum ya aikata mugun aiki, kamar cutar da wanda yake yi wa hassada.
• Hassada tana hana mutum mai da hankali kan nasararsa, tare da an giza shi yana riƙa jin haushin wasu maimakon yin aikin da zai amfane shi.
• Hassada tana hana mutum gode wa Allah da abin da yake da shi.

Mafita:
Maimakon haka, Musulunci ya na koyar da yin gibḍa (kishi mai kyau), wato yin burin yin abin da wani yake yi ba tare da fatan sharri gare shi ba. Misali, idan mutum yana ganin wani ya fi shi ilimi, maimakon yin hassada, yana da kyau ya yi addu’a Allah Ya ba shi ilimi kamar nasa.

Hassada Rashin Ladabi Ce Ga Allah:

Idan mutum yana jin haushin yadda wani ya samu wata ni’ima, hakan yana nufin yana ƙin hukuncin Allah ne. Wannan kuwa yana iya jefa mutum cikin shakka ko rashin yarda da Allah. Allah Ta’ala Ya ce a cikin Alƙur’ani: ”Kuma Allah Yana bayar da mulkinsa ga wanda Ya ga dama, kuma Allah Mai Yalwa ne, Masani” Suratul Baƙara aya ta 247.

A ma’anar wannan aya ita ce, Allah ne yake rarraba arziki, da ilimi, da kyau, da sauran ni’imomi ga wanda Ya ga dama. Idan mutum yana jin haushin wannan, to yana sukar hukuncin Allah ne. Misali a rayuwa, Idan mutum yana jin haushin wani saboda yana da dukiya, wannan yana nuna cewa bai gamsu da yadda Allah ke bayar da arziki ba. Idan mutum yana jin haushin wani saboda yana da kyau ko hikima, yana nufin yana ƙin tsarin Allah ne. Hassada tana sa mutum ya yi tambayoyi marasa amfani, kamar:

○ Me yasa Allah Ya ba wane, amma ni bai ba ni ba?”
○ Me yasa ni ban samu kaza ba alhali na fi shi ƙoƙari?
Waɗannan tunani suna iya jefa mutum cikin gaba da ƙaddara, wanda hakan yana daga cikin munanan al’amura a Musulunci da suke taɓa imanin bawa.

Hassada Tana Jefa Mai Yi Cikin Wahalar Zuciya da Damuwa:

Baya ga kasancewar hassada zunubi, hassada tana cutar da zuciyar mai yi. Wannan yana da nasaba da ilimin halayyar dan ɗan’adam (wato psychology), wanda ya tabbatar da cewa hassada tana jefa mutum cikin damuwa da ciwon zuciya.

Yadda Hassada Take Hana Jin Daɗi:

Hassada tana hana mai hassada jin daɗi ta fuskoki masu yawa da suka haɗa da:

● Mai hassada yana rayuwa cikin baƙin ciki, saboda yana kallon wasu yana jin haushinsu.
Yana cike da damuwa, saboda yana son a cire wa wani wata ni’ima a maimakon ya mai da hankali kan kansa.
● Mai hassada yana ƙin farin cikin wasu, idan wani ya yi nasara, sai ya ji haushi a maimakon ya taya su murna.

Ga Wa su Misali a Rayuwa:
1. Idan mutum yana jin haushin wani saboda ya sami aiki, yana iya shafe kwanaki yana tunanin hakan a maimakon neman na kansa.
2. Idan mutum yana jin haushin abokin karatunsa saboda ya fi shi kyau, yana iya jin ƙunci da matsin lamba a maimakon ƙoƙarin kyautata halinsa. Allah Ya tsare mu daga hassada, Ya sa mu kasance cikin masu gode Masa da kyawawan halaye! Amin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Abu Razina Nuhu Ubale Paki Ramadan Idan mutum yana jin haushin wani saboda a Allah Ya ba saboda yana wata ni ima

এছাড়াও পড়ুন:

Rigima: Mawaƙi Portable ya kwana a hannun ’yan sanda

’Yan sanda sun kama shahararren mawaƙin zamani a Najeriya Habeeb Okikiola Badmus, wanda aka fi sani da Portable, bayan ƙazancewar rikicinsa da fitaccen ƙwararren mawakin Fuji, Okunola Saheed “Osupa.”

A ranar Lahadi da dare ne ’yan sanda daga Jihar Kwara suka yi takakkiya suka kamo Portable mai waƙar “Zazu Zeh” a garin Abeokuta, Jihar Ogun

Kakakin ’yan sanda na Jihar Kwara, SP Adetoun Ejire-Adeyemi, ya ce an kama Portable bayan samun takardar ƙorafin da Osupa ya aike ɗauke da jerin manyan zarge-zarge da yake yi wa mawakin na “Zazu Zeh,” na ɓata suna, barazanar kisa, tunzura jama’a, zubar da da mutum da gangan, neman tayar da fitina, da kuma amfani da zagi da munanan kalamai.

“Saboda girman waɗannan zarge-zarge da kuma ingantattun shaidun da aka gabatar, rundunar ta samu sammacin kame daga Kotun Majiatare da ke zamanta a Ilorin, inda jami’anmu suka je Abeokuta, suka kamo wanda ake zargin suka kawo shi Ilorin domin ci gaba da bincike.”

Jami’in ya ce da kawo Portable jihar Kwara, nan take aka fara yi masa Portable tambayoyi da ɗaukar bayanansa a gaban lauyoyi daga bangarorin biyu.

Ya tabbatar da cewa Portable zai ci gaba da kasancewa a tsare kuma nan ba da komawa ba za a gurfanar da shi a gaban kotu.

Rigimar mai zafi, tsakanin Portable da Osupa, ta samo asali ne daga rashin jituwa kan keta haƙƙin mallakar waƙa. Wannan rashin jituwa ta ɓarke ne a bainar jama’a lokacin da Portable ya yi amfani da zagi ga fitaccen mawakin na Fuji mai shekaru 55 a wani bidiyo da ya yaɗu, wanda ya jawo caccaka a kafafen sada zumunta.

A cikin bidiyo, Portable ya bayyana cewa, “Kuɗi ne ya jawo faɗan!” yana ƙoƙarin bayyana ɓacin ransa. Ya ce “Raina ya ɓaci ne saboda ina so a ba ni kuɗina, kuma na ji suna ƙoƙarin sauke waƙar.”

Bayan shan caccaka daga bisani ya saki wani bidiyo yana neman afuwar Osupa cikin girmamawa. Ya ce, “Sarki Saheed Osupa, babana, don Allah kada ka yi fushi. Ka ɗauke ni kamar ɗanka ka horar da ni.”

A wani yanayi mai ban mamaki kuma, Portable ya nuna cewa rigimar tasu wani salon neman magoya baya ne, har ma ya nemi a ba shi damar gudanar da wasanni. “Dukkanmu muna tallata kanmu… don Allah a ba ni aiki.”

Sai dai, Saheed Osupa ya yi watsi da neman afuwar a matsayin wanda bai isa ba, yana mai cewa dole Portable ya samu sakamakon abin da ya aikata.

Ƙi amincewar tasa ba ta yi wa Portable daɗi ba, har ya ƙi janyewa, inda a ƙarshe ya kai ga matakin da Osupa ya ɗauka na shigar da ƙara ga hukumar ’yan sanda.

Yanzu, duniyar nishaɗi ta zura ido tana kallon yadda za a ƙare a wannan rikici  manyan mawaka da ya tashi daga kafafen sada zumunta zuwa zauren kotu.

Shin Portable zai fuskanci cikakken hukuncin doka bisa ga zarge-zargen da ake yi masa, ko kuwa za a samu sasanci ne?

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutum 45 Sun Rasa Rayukansu A Wani Sabon Hari A Filato 
  • Rigima: Mawaƙi Portable ya kwana a hannun ’yan sanda
  • Dagewa Iran Takunkuman Zalunci Na Daga Cikin Manufofin Tattaunawa Da Amurka: Aref
  • Sin Ta Yi Allah-wadai Da Karin Harajin Amurka Ta Kuma Jaddada Goyon Bayanta Ga Ka’idojin WTO 
  • Tsohon Kocin Super Eagles, Christian Chukwu, Ya Rasu Yana Da Shekaru 74
  • Kallo Daya Mutum Za Yi Min Ya Gane Masana’antar Kannywood Ta Canza Rayuwata -Farida Abdullahi
  • Axios: Makomar Tsarin Jarin Hujja A Duniya  Tana Girgiza
  • Najeriya Tana Fatan Samun Dalar Amurka Biliyan $200 A Ayyukan Sararin Samaniya
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 108
  • NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi