HausaTv:
2025-04-15@07:23:17 GMT

Babban Kusa A Kungiyar Hamas Salah Al-Bardawil Ya Yi Shahada

Published: 24th, March 2025 GMT

Kungiyar gwagwarmayar Falastinawa ta Hamas ta fitar da wata sanarwa dangane da shahadar Salah al-Bardawil, mamba a ofishin siyasa na kungiyar kuma wakilin majalisar dokokin Falasdinu.

A rahoton tashar Al-Alam, bayanin Hamas yana cewa: Dr. Salah Al-Bardawil, wanda ya yi fice a fagen siyasa, kafofin watsa labarai, da fagage na kasa da kasa, kuma ake kallonsa a matsayin daya daga cikin manyan kusoshin Hamas, wanda yake a kan gaba wajen gwagwarmaya da  sadaukarwa, ya yi shahada a kan tafarkin gaskiya.

Bayanin ya ci gaba da cewa: Bai taba gazawa wajen gudanar da ayyukansa na jihadi da hidima ga al’ummar Palastinu ba, ya kuma ci gaba da yin gwagwarmaya kan turba ta gaskiya da neman ‘yanci har zuwa karshen rayuwarsa.

Hamas ta jaddada cewa,  jinin Dakta Al-Bardawil da matarsa ​​da sauran shahidai wata fitila ce da za ta haskaka hanyar samun ‘yanci ga al’ummar Falastinu, kuma laifuffukan makiya ba za su taba raunana azama da jajircewar ‘yan gwagwarmaya a Falastinu ba.

A karshen wannan sanarwa da ta fitar a wannan Lahadi 23 ga Maris, 2025, kungiyar Hamas ta yi fatan samun rahama da aljannah ga Dr. Salah Bardawil da matarsa, tare da sauran wadanda suka yi shahada a kan tafarkin gaskiya.

Salah Al-Bardawil da matarsa ​​sun yi shahada ne a daren ranar 23 ga watan Ramadan, bayan wani hari da yahudawan sahyuniya suka kai a kan tantin su da suke a  yankin Al-Mawasi da ke yammacin birnin Khan Yunus.

Wannan harin dai wani bangare ne na kisan gilla da yahudawan Haramtacciyar Kasar Isra’ila  suke ci gaba da yi kan al’ummar Gaza marasa kariya, tare da samun cikakken goyon baya da karfin gwiwa da dukkanin taimako kan hakan daga gwamnatin kasar Amurka.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Salah al Bardawil Salah Al Bardawil

এছাড়াও পড়ুন:

Al’ummar Mauritaniya Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Nuna Adawa Da Yakin Gaza

Al’ummar Mauritaniya sun gudanar da zanga-zangar nuna adawa da yakin da ake yi a Gaza

A karkashin taken “An rusa Gaza” kuma goyon bayan al’umma ga Falasdinawa abu ne da ya zama wajibi, ba zabi ba, mazauna birnin Nouakchott fadar mulkin kasar Mauritaniya sun gudanar da zanga-zanga domin jaddada bukatar musulmi a ko’ina a duniya su goyi bayan gwagwarmayar da ake yi a Zirin Gaza.

Zanga-zangar dai ta samu halartar kungiyoyin ‘yan jaridu da sauran kungiyoyi da dama, wadanda suka bayyana Allah wadai da shirun da manyan kasashen duniya suka yi, tare da sukar su kan goyon bayan sojojin mamayar Isra’ila.

Wani sheikhin malami dan kasar Mauritaniya ya ce: “Sun sanar da mu irin wannan gagarumin aiki, Allah Ya saka musu da alheri kan irin wannan zanga-zangar da suke yi na goyon bayan wadanda ake zalunta ta hanyar kashe mata da yara da kuma tsofaffi da suke yunkurin kare hakkokinsu.

Masu zanga-zangar sun yi kira da a yanke alaka tsakanin kasarsu da Amurka da duk masu goyon bayan yahudawan sahayoniyya a yakin da suke yi na neman shafe Falasdinawa daga kan doron kasa tare da azabtar da su da masifar yunwa a zirin Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Babban Daraktan Hukumar IAEA, Zai Ziyarci Iran ranar Laraba
  • Hamas ta ce a shirye take ta sako dukkan fursunonin Isra’ila da suka rage, domin musanya fursunoni”
  • Gaza: Mutane 38 Sun Yi Shahada A Yau Litinin
  • Kasashen Larabawa Na Yankin Tekun Farisa Sun Yi Fatan Al-Khairi Ga Iran Da Amurka A Tattaunawar Shirin Nukliyar Kasar
  • Salah Ya Kafa Tarihi Yayin Da Liverpool Ke Dab Da Lashe Gasar Firimiya
  • Al’ummar Mauritaniya Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Nuna Adawa Da Yakin Gaza
  • Inganta Rayuwar Al’umma: Amurka Da Ƙungiyar Kasuwanci Ta Nijeriya Sun Karrama Gwamna Lawal
  • Gaza: Sojojin HKI Sun Sake Kai Wa Asibitin “Ma’amadani Hari
  • Sama da mutane 1,560 ne sukayi shahada tun bayan da Isra’ila ta koma kai farmaki Gaza
  • MDD: Mafi Yawancin Wadanda Yaki Ya Ci A Gaza Mata Ne Da Kananan Yara