A shekarar 2024 da ta gabata, kamfanonin kasar Sin da masu bincike na kasar, sun gabatar da sabbin bukatun neman ikon mallakar fasaha har 20,081 ga ofishin rajistar ikon mallakar fasaha na Turai ko EPO, kamar dai yadda alkaluman shekarar 2024 da ofishin ya fitar a yau Talata suka nuna.

Wannan adadi ya kai kaso 10.

1 bisa dari na jimillar neman izini da ofishin na EPO ya karba a bara, wanda hakan ya tabbatar da Sin a matsayi na 4 cikin jerin kasashe mafiya gabatar da bukatar ga ofishin a duniya baki daya.

A jerin kamfanoni dake cikin jadawalin na EPO, kamfanin Huawei na Sin na matsayi na biyu, da bukatun neman ikon mallakar fasaha har 4,322. Baya ga Huawei, akwai kuma wasu kamfanonin Sin 5 da su ma ke cikin kamfanoni 50 na sahun farko a jadawalin, wanda hakan ke nuni ga yadda Sin ke samun karin tagomashi a fannin kirkire-kirkire, da shiga a dama da ita wajen neman ikon mallakar fasahohi a Turai. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: neman ikon mallakar

এছাড়াও পড়ুন:

Kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa na fatan nasara ga tattaunawar Amurka da Iran

Kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa na fatan nasara ga tattaunawar Iran da kuma Amurka.

Kasar Iraki ta bayyana fatan tattaunawar za ta aifar da kwanciyar hankali a yankin

Ministan harkokin wajen Iraki ya bayyana goyon bayansa ga tattaunawar tsakanin Iran da Amurka, yana mai bayyana fatan Bagadaza na ganin cewa hakan zai samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

A wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen Iraki ta fitar ta ce “Hussein ya karbi bakuncin mataimakin ministan harkokin wajen Iran Saeed Khatibzadeh a ranar Juma’a a gidansa da ke birnin Antalya na Turkiyya.

Sanarwar ta kara da cewa “a yayin ganawar, an tattauna dangantakar da ke tsakanin kasashen dake makobtaka da juna da kuma hanyoyin karfafa su a fannoni daban-daban.”

“Hussein ya yi maraba da tattaunawar ta tsakanin Jamhuriyar Musulunci ta Iran da Amurka, yana mai bayyana fatansa na cewa a wannan shawarwarin za a samu sakamako mai kyau da zai taimaka wajen samun kwanciyar hankali a yankin.”

Shi ma babban daraktan hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA Rafael Grossi ya bayyana fatansa na ganin an cimma yarjejeniyar nukiliyar tsakanin Iran da Amurka cikin gaggawa.

Grossi ya ce yana da kwarin gwiwar cewa bangarorin biyu za su iya warware sabanin ra’ayi a fannin tattalin arziki da cinikayya ta hanyar yin shawarwari kafada-da-kafada da hadin gwiwa don cin moriyar juna.

Stephane Dujarric, mai magana da yawun babban sakataren MDD Antonio Guterres, ya bayyana fatansa game da tattaunawar ta tsakanin Amurka da kuma Iran.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yaƙin Neman Zaɓe A 2027: Ƙungiya Ta Nemi A Maye Gurbin Mai Magana Da Yawun Shugaban Ƙasa
  • Kamata Ya Yi Amurka Ta Kara Kokarin Gyara Kuskurenta 
  • Sin Na Maraba Da Masu Zuba Jari Domin Su More Damammakin Bunkasarta
  • Aljeriya ta yi barazanar korar jami’an diflomasiyyar Faransa 12
  • Rigima: Mawaƙi Portable ya kwana a hannun ’yan sanda
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Siyo Tan Tan 360 Ga Manoma
  • Gwamnatin Amurka Ta Yi Da’war Cewa; Ba Ta Neman Tashin Hankali Tsakaninta Da Iran
  • Firaministan Kasar Laos: Kasar Sin Abar Koyi Ce a Fannin Kawar Da Talauci
  • Sin Da Sifaniya Sun Daga Matsayin Hadin Gwiwa A Fannin Shirya Fina-finai
  • Kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa na fatan nasara ga tattaunawar Amurka da Iran