Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranar Litinin, 31 ga watan Maris, da Talata, 1 ga watan Afrilu, a matsayin ranakun hutun ƙaramar salla.

Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo ne, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da sakataren ma’aikatar, Magdalene Ajani, ya fitar a ranar Laraba.

Ahmad Lawan ya raba tallafin N27m da buhun shinkafa 300 a Yobe Tsohon hadimin gwamnan Kano, Abdullahi Tanka Galadanci, ya rasu

Ya taya al’ummar Musulmi murnar kammala azumin watan Ramadan cikin nasara, tare da yin kira a gare su da su ci gaba da halaye nagari da suka koya a watan.

Haka kuma ya jaddada muhimmancin soyayya, yafiya, da haɗin kai wajen gina al’umma.

Tunji-Ojo, ya buƙaci ’yan Najeriya da su yi amfani da wannan lokaci wajen yin addu’a domin samun zaman lafiya, kwanciyar hankali, da ci gaban ƙasa.

Ya yi fatan cewa bukukuwan salla za su ƙara haɗin kai tsakanin mutane duk da bambancin addini da ƙabilanci da ake da su.

Haka kuma, ya yi kira ga jama’a da su yi bukukuwan ta hanyar tunawa da mabuƙata, ta yadda za a taimake su.

A madadin Gwamnatin Tarayya, ministan ya aike da saƙon fatan alheri ga dukkanin Musulmi tare da addu’ar Allah Ya sanya farin ciki a zukatan kowa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Bukukuwa Gwamnatin tarayya Karamar Sallah Ranaku Gwamnatin Tarayya

এছাড়াও পড়ুন:

Ina Fatan Ci Gaba Da Kasancewa A Manchester United – Onana

Tom Heaton da Altay Bayindir ba su samu lokacin da suke bukata a United ba, Bayindir ya buga kananan wasanni a kakar wasa ta bana, amma kuma tsohon mai tsaron ragar na Fenerbahce na fatan ganin ya samu karin lokacin buga wasanni kamar sauran yan wasa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Abin da ya sa nake jin daɗin yadda Tinubu yake tafiyar da gwamnatinsa — Buhari
  • An Tabbatar Da Ganin Watan Shawwal A Nijeriya
  • An Ga Watan Sallah A Ƙasar Saudiyya
  • Rikici Ya Turnuke Jam’iyyar SDP A Yayin Da Aka Samu Shugabanni Bangare Biyu A Kogi
  • MDD Ta Yi Gargadi Akan Mummunan Yanayin A Sudan Ta Kudu
  • Gwamnatin Kaduna Ta Jadadda Kudurin Ta Wajen Samarda Tsaftatacen Ruwan Sha Ga Al’umma 
  • Ina Fatan Ci Gaba Da Kasancewa A Manchester United – Onana
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Hana Baƙin Haure Shigowa Nijeriya Ba Bisa Ƙa’ida Ba
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bada Hutun Sallah Karama Ta 2025/1446
  • Sallah: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Litinin Da Talata A Matsayin Hutu