Sallah: Yadda ake shirin caɓa ado duk da tsadar kaya
Published: 27th, March 2025 GMT
A yayin da ake tunkarar bikin ƙaramar sallah, hankalin Musulmi a ko ina a duniya, ya karkata zuwa ga hidimar wannan rana ta musamman, musamman a fannin ado da sabbin kaya.
A wata ziyarar da Aminiya ta kai babbar kasuwar tufafi da kayan ado ta Kwari da ke Kano, ta tarar da kasuwa cike maƙil da mata da maza, kowanne na ƙoƙarin sayen sabbin kaya.
Kayayyakin da aka fi saya sun haɗa da atamfofi, mayafai, adire, dogayen riguna, leshi, sarƙoƙi, yadi, da sauran kayan ado.
Kasuwanni sun cika maƙil da masu sayayya
A yayin da ya rage saura kwanaki kaɗan a yi sallah, kasuwanni sun cika maƙil, inda jama’a ke shirin sayan sabbin tufafi da za su yi ƙawa da su a ranar.
A kasuwar Kwari da ke Kano, dandazon mata da maza ne suke sayen kayan ado da tufafi da sauransu.
Wasu na sayen atamfofi da mayafai, wasu kuma sun fi mayar da hankali kan dogayen riguna, leshi, sarƙoƙi, da yadi, sai dai tsadar kaya a gefe guda ta sauya shirin da dama daga cikinsu.
Aisha Idris, uwa ce da ta fito domin yi wa iyalinta sayayyar kayan sallah. Ta shirya saya wa kanta sabon kaya guda ɗaya da kuma guda biyu-biyu ga ’ya’yanta mata da maza.
Amma kuma tana shiga kasuwa sai ta tarar da farashin kaya ya yi tsada fiye da yadda ta yi tsammani.
Ta ce: “Da na shiga kasuwa sai na tarar kayan da za a yi yayi ne suka fi yawa. Amma kowanne idan za a saye shi sai an daure.”
A cewarta, yanzu haka dogayen riguna na yara sun kai Naira 19,000 zuwa Naira 20,000, na manya kuma daga Naira 40,000 zuwa Naira 50,000, har ma akwai wasu da suka haura Naira 50,000.
Hijabin da ake kira ‘Matar Gwamna’ shi ma ana sayar da yadinsa kan Naira 2,500, yayin da na ɗinkakke ya kai Naira 15,000.
Takalmin da ake kira ‘Gidan Sarauta’ mai manyan duwatsu kuwa yana tsakanin Naura 14,000 zuwa Naira 15,000.
Aisha Idris ta ce: “Ban iya siya wa kaina komai ba. Sai dai na saya wa ’ya’yana atamfa mai kyau a kan kuɗi Naira 11,000.”
Yadda mata ke shirin caɓa ado da sallahAmina Yakubu, wata matashiya da Aminiya ta tattauna da ita, ta ce tana shirin yin ado da sabbin kaya a sallar bana.
“Sallar bana ta zo da yayi kala-kala daidai da ajin da kike da shi da kuma aljihunki. Ni dai na yi ɗinki, na kuma sayi doguwar riga.”
Ta bayyana cewa ɗinkin da ake yi yayi a bana shi ne ɗinkin ‘Kufta’, wanda ake yi masa ado da duwatsu masu walwali.
Ana fara ɗinkin daga Naira 20,000 zuwa sama, ko da yake akwai wasu da ba su da adon sosai da ake iya samun su a ƙasa da haka.
“Ranar idi kuma yayin hijabi za a yi, don haka na sayi ‘Matar Gwamna’ na adana ina jiran ranar.”
Teloli na cin karensu ba babbakaDuk da koke-koken tsadar kaya, teloli na cin alfanun kasuwar bana, domin suna samun ɗinki sosai fiye da na bara.
Mujahid Sallari, wani tela da muka tattauna da shi, ya ce: “Bana ana ɗinki sosai fiye da bara. Ɗinkin manya kuma ya fi yawa fiye da na yara, musamman ’yan mata.”
Ya ce akwai mata da suke bayar da ɗinki har guda uku zuwa biyar, wanda a shekarar bara ba haka abin yake ba.
Ɗinkin da aka fi yayi a banaMujahid ya bayyana cewa ɗinkin da aka fi yi a bana sun haɗa da Buba, Kaftan da kuma Abaya.
Wasu mata sun fi sayen rigunan Abaya na ƙasashen Larabawa, yayin da wasu ke siyan yadi su ɗinka na gida saboda farashin doguwar riga ya yi tsada.
Me ya sa teloli suka ƙara kuɗin ɗinki?Dangane da koken da aka yi cewar teloli sun ƙara farashi, Mujahid ya bayyana cewa matsalar ba daga wajensu take ba.
“Gaskiya ba ma za a kwatanta farashin kayan ɗinkin bara da bana ba. Tun da azumi ya zo, aka ƙara kuɗin ɗinki.
“Yayin da azumi ya zo sai kuma abin ya ƙara tashi, har zuwa bikin Sallah.”
Ya ƙara da cewa tsadar kayan ɗinkin ita ce ta sa su ma dole suka ƙara farashin aikinsu.
Yadda ake yayin lalle da ƙunshi a sallar banaKwalliyar sallah ba ta cika a wajen mata, idan aka ce babu lalle ko ƙunshi. Kamar kowace shekara wannan sallar ma mata na yi wa gidajen masu ƙunshi da lalle ƙawanya domin kece raini.
A bana, matan sun bayyana cewa lallen ‘salatif’ da fulawa baƙa ne ake yi yayi.
“Ko dai samari sun bayar da kuɗin lalle, ko ba su bayar ba, dole a yi.”
A taƙaice, sallar bana ta zo da sabbin ɗinkuna, hijabai, takalma da adon lalle, duk da cewa farashi ya tashi sosai.
Yayin da mutane ke shirye-shiryen Sallah, kasuwanni sun cika, kayan ado sun mamaye kasuwanni, teloli na warkajaminsu, amma kuma tsadar kaya ta sauya tsarin sayayya.
Waɗanda suka saba sayan kaya masu yawa, yanzu sun taƙaita; wasu kuma sun mayar da hankali kan hijabai da dogayen riguna. Duk da haka, ana sa ran za a gudanar da bikin Smsallah cikin farin ciki da jin daɗi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: abaya Kasuwar Kwari kwalliya Rahoto dogayen riguna bayyana cewa sallar bana tsadar kaya
এছাড়াও পড়ুন:
Makarantar Bare: Shekara 20 dalibai na karatu a matsanancin yanayi
Ilimi na da muhimmanci wajen gina al’umma, amma ga daliban Makarantar Firamare ta Bare a karamar Hukumar billiri, Jihar Gombe, wannan lamari ya zama kamar mafarki mai wahalar tabbatuwa.
Duk da ikirarin da Gwamnatin Jihar Gombe ke yi na cewa, tana fifita ilimi ta hanyar manyan ayyuka kamar gine-ginen makarantu masu hawa biyu a kowace mazabar Sanata, a halin da ake ciki a Makarantar Firamare ta Bare ba ta san da hakan ba. Wannan makaranta tana nuna sakaci da gazawar masu mulki.
An kafa makarantar ce a shekarar 2005 karkashin shirin Hukumar Kula da Ilimin Firamare ta Jihar Gombe (SUBEB). Tun daga lokacin har zuwa yanzu, ba a taba samun gyara ko ci-gaba ba. Maimakon zama alamar ci-gaba, makarantar ta koma kamar wani gida da aka watsar.
Wakilinmu ya yi tattaki zuwa wannan makaranta da take cikin mummunan yanayi. Ban da ofishin shugabar makarantar, babu wani dakin karatu a makarantar da ke da kofofi ko tagogi ko sili mai kyau.
Dalibai suna zama ne a kasa, saboda babu kujeru da tebura ko kayan karatu na zamani. Malamai kuma na fama da irin wannan matsa, wadda take hana su bayar da ingantaccen ilimi.
Makarantar tana da azuzuwan karatu biyu ne kadai a gini daya da kuma wani gini da aka ba su aro, daga bisani aka mallaka wa makarantar, wanda shi ma ya lalace, babu kofofi babu tagogi.
A halin yanzu, makarantar na da dalibai sama da 400, adadi mai yawa idan aka kwatanta da karancin kayan aiki da take da su.
Don shawo kan wannan matsala, ana hade daliban firamare na Aji 1A, 1B, da 1C cikin aji daya. Wannan cunkoso ya sa koyarwa da karatu suka zama cikin mawuyacin yanayi.
Wani dalibi ya bayyana cewa, “saboda mu ‘ya’yan talakawa ne, gwamnati ba ta damu da gyara makarantarmu ba. Da iyayenmu suna da hali, da sun kai mu makarantu masu inganci.”
Wannan kalamai sun bayyana halin da marasa galihu ke ciki, inda makomarsu take fuskantar barazana saboda rashin kulawar gwamnati.
Bugu da kari, al’ummar unguwar sun kasa tashi tsaye wajen neman gyara makarantar,
sai dai wani mazaunin garin ya ce, gyaran azuzuwan makarantar ba zai bukaci kudade masu yawa ba. Amma duk da haka, kusan shekara 20 ke ann ba tare da wani yunkurin gyara ba.
Da wakilinmu ya nemi jin ta bakin Kwamishiniyar Ilimi ta Jihar Gombe, Hajiya Aishatu Umar Maigari, sai ta ce, makarantar ba a karkashinta take ba, tana karkashin Hukumar SUBEB ce don haka SUBEB za a tuntuba, ita ba ta da ta cewa a kai.
Da muka tunubi Sakataren SUBEB, Babaji Babadidi ta wayar salula, ya bayyana cewa, bai san halin da makarantar ke ciki ba, domin bai da cikakken rahoto a kanta kasancewar a tunaninsa wai makarantar almajirai ce saboda lalacewarta.
Amma ya jinjina wa wakilinmu na ankarar da shi da ya yi kan yanayin da makarantar take ciki, inda ya yi alkawarin bincike tare da hadin gwiwar Sakataren Ilimi na karamar Hukumar billiri.
Yanayin Makarantar Firamare ta Bare na nuna rashin daidaito cikin tsarin ilimi a Gombe. Duk da ikirarin da gwamnati ta yi na inganta ilimin firamare, makarantu irin su Bare na ci gaba da kasancewa cikin halin kaka-naka-yi.
Ya kamata gwamnati ta gaggauta gyaran makarantar, ta samar da kayan aiki da kuma daukar karin malamai. Hakazalika, al’ummar yankin ya zama wajibi su tsaya tsayin daka wajen sa ido kan hukumomi domin ganin an samu ci gaba mai dorewa.
daliban makarantar sun fi bukatar ganin gyara fiye da alkawuran da ba a cika su ba, domin suna bukatar makoma mai kyau ta hanyar samun ingantaccen ilimi, ba wanda ake lalatawa ba saboda sakaci.
Koken iyaye kan matsaloli da bukatar gaggauta gyaran makarantar
Malam Yusuf Abdullahi, tsohon malamin makarantar da yanzu ke aiki a wani wuri daban, ya bayyana cewa, malamai suna iyakar kokarinsu duk da mawuyacin yanayin da suke fuskanta.
Ya ce, yaransa biyu suna karatu a makarantar, suna kokari a bangaren karatu, amma rashin kujeru da kayan koyarwa yana rage wa dalibai sha’awa.
“Yara suna zama ne a kasa yayin darussa, wasu kuma suna barin makarantar gaba daya saboda munin yanayin karatun,” in ji Yusuf cikin damuwa.
Ya kara da cewa, wasu iyaye na cire ‘ya’yansu zuwa makarantu masu kayan aiki, irin su Central Primary School ko Ibinola, inda yanayin karatu ya fi inganci.
Malama Maryam Shu’aibu, mahaifiyar yara uku da ke karatu a makarantar ta bayyana takaicinta, “ina son mayar da ‘ya’yana wata makaranta, amma rashin kudi ya hana ni. Kodayake ba mu biyan kudin makaranta, sai dai Naira 200 na kudin PTA, amma makarantar ba ta da muhimman kayan aiki,” in ji ta
Ta roki gwamnati da ta samar da kujeru da littattafai da sauran kayan koyarwa domin tabbatar da yara na samun yanayin karatu mai kyau kafin su shiga makarantar sakandare.
Ita ma Shugabar makarantar, Misis Talatu Idi, ta bayyana halin da ake ciki a makarantar cikin bakin ciki. “Makarantar ba ta da kujeru da tagogi da kofofi, har ma da rufin kwano mai kyau a dakunan karatu. dalibai na zama a kasa, suna korafin kullum kayansu suna datti da ta sa wasu ba sa zuwa makarantar.
A wasu lokuta, mutanen gari suna yin bayan gida a cikin dakunan karatun makarantar, sai yara sun fito karatu a sa su kwashe, saboda rashin kofofi da tagogi da cikakken tsaro a makarantar, wanda hakan ke kara tabarbarbara yanayin makarantar’’.
Misis Talatu ta kara da cewa, kayan koyarwa sun yi karanci, kuma ita take biyan mai musu gadin makarantar a aljihunta Naira dubu 3,000 wani lokaci 2,500 saboda babu wani tanadi daga kasafin kudin gwamnati.
Hakimin Bare, Galadiman Tangale, Alhaji Yunusa Adamu Galadima, wanda shi ne Shugaban Hukumar Makarantar (SBMC) ya ce, an sha kokarin ganin an gyara makarantar, amma ba a samu nasara ba.
Ya ce, sun rubuta takardu zuwa hukumomin da abin ya shafa, ciki har da SUBEB da sashen ilimi na karamar hukuma, amma ba tare da wani sakamako ba.
Acewarsa, yana zargin ko idan aka tashi gyaran makarantar ana karkatar da aikin zuwa wani waje ne ba su sani, domin akwai wata makaranta mai suna BORE su kuma BARE ne, sunansu ya yi kama da Bare. wanda tun bayan gina azuzuwan farko guda biyu har yanzu ba a sake aza tubali ko wane iri ba.
Da muka tuntubi Sakataren Ilimi na karamar Hukumar billiri, Mista Titus Ladoji ya tabbatar da cewa, makarantar ba ta taba samun gyara ba tun da aka gina ta a 2005.
Ya yarda cewa, Makarantar Firamare ta Bare tana cikin makarantu da ke cikin mawuyacin hali, amma ba a sa ta cikin jerin makarantun da za a gyara ba tukuna.
Duk da kokarin da hakimin ya yi na samar da fitilu a makarantar, domin hana sata da lalata kayan makarantar, yanayin makarantar yana bukatar
daukar matakin gwamnati na gaggawa.