Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [20]
Published: 28th, March 2025 GMT
Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [18] Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [17]
Fashin Baƙi:
Maganar Ibn Juzai tana nuni ne ga girman tasirin salatin Annabi (S.A.W)i a rayuwar Musulumi, musamman dangane da ƙaunar Annabi Muhammad (S.A.W) da bin sunnarsa. Domin cikakken bayani kan wannan batu, bari na ɗan zurfafa bincike a cikin abubuwan da ke cikinsa.
Ma’anar Salati
A fagen ilimi, salati ga Annabi (S.A.W) na da fassarori da dama:
Idan Allah ne Yake yin Salati: Yana nufin yabo da ɗaukaka ga Annabi (S.A.W) da Allah Yake yi masa a wajen mala’iku. Idan Mala’iku ne Suka yi Salati: Yana nufin nema wa Annabi (S.A.W) rahama da ɗaukaka, da daraja da martaba a wurin Allah. Idan Musulumi Suka yi Salati: Yana nufin nema wa Annabi (S.A.W) albarka da gafara, da ɗaukakar daraja da girma da matsayi wurin Allah.
Allah Ya barta mana cewa:” Lalle Allah da mala’ikunsa suna yin salati ga Annabi. Ya ku mummunai! Ku yi salati a gare shi, kuma ku yi sallama mai yawa” Suratul Ahzãbi aya ta 56.
Wannan aya tana nuna cewa yin salati wajibi ne, kuma yana da babbar lada.
Salatin Annabi Yana Kawo Ƙaunar Annabi(S.A.W):
Domin a fahimci wannan batu, sai mu tambayi kanmu: Ta yaya mutum yake ƙaunar wani? Amsa a nan ita ce: Yana ƙaunar wanda yake yawan tunawa ne, kuma yana ƙaunar wanda yake amfana da shi ne a rayuwa, ya kuma ƙaunar wanda yake tare da shi a zuciya. Salati ga Annabi (S.A.W) yana ƙara ƙaunarsa domin Ya na yawan tunatar da Musulumi Annabi (S.A.W).
Yayin da mutum yake yawan yin salati, hakan yana sa zuciyarsa ta cika da tunanin Annabi (S.A.W), har ya zama yana ƙaunar sa fiye da kansa. Annabi (S.A.W) ya bayyana cewa: ”Ɗayanku ba zai zama cikakken mummuni ba har sai na zamnto Ni ne na fi soyuwa a gare sa sama ɗansa da mahaifinsa da mutane baki ɗaya.” Bukhari da Muslim ne suka ruwaito.
Salati Yana Jawo Amsawar Annabi (S.A.W):
Annabi (S.A.W) ya ce: “ Babu wani da zai yi min salati face Allah Ya dawo min da ruhina har sai na amsa masa” Hadisi ne ingantacce Abū Dãwūd da Ahmad ne suka ruwaito.
Wannan yana nuna cewa salatin da Musulumi yake yi yana isa ga Annabi (S.A.W), kuma yana jin sa. Idan Musulumi yana da wannan fahimta, tabbas ƙaunarsa ga Annabi (S.A.W) za ta ƙaru.
Salati Yana Ƙara Fahimtar Rayuwar Annabi (S.A.W):
Duk wanda yake yawan yin salati, zai shiga neman ilimi game da halayen Annabi (S.A.W), da maganganunsa da ayyukansa. Wannan zai sa ƙaunarsa ta ƙaru, kamar yadda mutum ke ƙaunar wanda ya san halinsa.
Salati Hanya ce Ta Shiga Aljanna:
Manzon Allah (S.A.W) ya ce:” Duk wanda ya manta yi min salati, to ya kuskure hanyar shiga Aljanna “ Hadisi ne ingantacce Ibnu Maja ne ya ruwaito. Wannan yana nuna yin salati ga Manzon Allah (S.A.W) hanya ce ɗoɗar ta shiga Aljanna.
Salati Na Sanya Mutum Ruƙo da Sunna:
Bin sunna yana nuna ingantacciyar ƙaunar Annabi (S.A.W). Idan mutum ya san cewa yin salati yana ƙara masa kusanci da shi, zai so yin koyi da shi a aikace. Allah Ya ce:” Ka ce: In kun kasance kuna son Allah, to ku yi min biyayya, sai Allah Ya so ku, kuma Ya gafarta muku zunubanku. Kuma Allah Mai gafara ne, Mai jin ƙai” Suratu Ãli Imrãn aya ta 31.
Salati Yana Ƙarfafa Son Bin Annabi (S.A.W):
Duk wanda yake yawan yin salati zai fi son yin koyi da Annabi (S.A.W) a cikin salla, da hulɗa da jama’a, da ibada da kuna mu’amala.
Idan mutum yana yawan yin salati, zuciyarsa tana son yin koyi da halayensa na gaskiya, kamar riƙon amana, da tausayi, da sanin ya kamata.
Salati Yana Hana Saɓa wa Annabi (S.A.W):
Duk wanda yake yawan yin salati, zai fi jin nauyin yin saɓo ko barin sunna. Domin yana sane da matsayin Annabi (S.A.W), kuma yana jin nauyin rashin bin hanyarsa.
Salati Yana Kawar da Tsauraran Ƙa’idojin bidi’a:
Yin salati yana hana mutum bin hanyoyin da ba sunna ba. Domin yana sane cewa abin da Annabi (S.A.W) ya bari, shi ne mafi alheri. Matuƙar mutum ya lazimci salatin da Annabi (S.A.W) ya zo da shi, to tabbas zai sami haka.
Fa’idoji Goma na Yin Salati ga Annabi (S.A.W)
-Yin salati yana da fa’idodi masu yawa, daga ciki akwai:
• Allah yana yin salati sau goma ga Musulumin da ya yi salati sau ɗaya.
• Ana gafarta wa mutum zunubi.
Ana ɗaga matsayi a Aljanna.
• Ana samun ceto (shafa’a) a ranar Alƙiyama.
• Ana samun waraka daga damuwa da baƙin ciki.
• Ana samun amsa addu’a.
• Ana kasancewa tare da Annabi (S.A.W) a ranar Alƙiyama.
• Ana samun kariya daga wahalar kabari.
Ana samun albarka a rayuwa.
• Ana samun kwanciyar hankali da soyayya a zuciya.
Hanyoyin yin salati suna da yawa, amma mafi inganci shi ne wanda Annabi (S.A.W) ya koyar, wato Salatin Ibrahimiyya
“Allahumma salli ‘ala Muhammadin wa ‘ala ali Muhammadin, kama sallaita ‘ala Ibrahima wa ala ali Ibrahima, innaka hamidun majid. Allahumma barik ala Muhammadin wq ala Ali Muhammadin kama barakta ala Ibrahim wa ala Ali Ibrahim innaka hamidun majid.”
A taƙaice, wannan magana ta Ibn Juzai tana nuni ne ga cewa wanda yake yawan yin salati ga Annabi (S.A.W) zai ƙara ƙaunarsa kuma zai fi son bin sunnarsa. Idan muna son Annabi (S.A.W), dole ne mu yawaita yin salati gare shi. Idan muna son bin sunnarsa, dole ne mu yawaita tunawa da shi. Idan muna son rabauta a duniya da lahira, salati na ɗaya daga cikin manyan hanyoyin da za su kai mu ga hakan. Allah Ta’ala Ya sa mu kasance cikin masu yawan salati ga Annabi (S.A.W) da bin sunnarsa har mu kasance tare da shi a Aljanna!. Amin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Abu Razina Nuhu Ubale Paki Ramadan wanda yake yawan yin salati ƙaunar wanda ya Duk wanda ya bin sunnarsa salati yana Salati Yana
এছাড়াও পড়ুন:
Shirye-shiryen Bukukuwan karamar Sallah
Sunana Naja’atu Baffa Jihar kaduna:
Ni dai a gaskia ban son akwai wani anko da za ai wannan sallar ko babu ba. Ina son saka takalmi mai dan tudu ba sosai ba, sai mayafi blue black, sai atamfa ta riga (half bubu) da ‘skirt’, sai sarka da dankunne da Awarwaro ‘silver’. Ina sha’awar cin Snacks irinsu meatpie, samosa, doughnut da kuma cake, sai kuma Yoghurt mai inibi. Ina son in ziyarci kanwar babata wacce take a cikin garin Adamawa.
Sunana Aminu Adamu Malam Maduri A Jihar Jigawa:
To batun shidimar sallah sai mu ce Alhamdullilah domin duk tanadin da mutum yayi sai ya kare, duba da yadda kayayyakin suturu ko tufafi suke tsada don haka sai mutum yayi amfani da abun da ya samu, domin gudanar da bikin sallar cikin kwanciyar hankali ya fi komai dadi. To magana ta gaskiya shadda ita ce kalar kayan da zai fi yawa domin ita shadda ba a daina yayinta kuma tana daga cikin kalar suturar da duk mai hali ko sukuni zai so ya dinka, amma wasu kuma za su dinka yaduka domin kowa da irin kalar suturar da ta fi burge shi. To ni dai nafi sha’awar farin kaya musamman yadda manyan kaya ma’ana riga, binjima da wando da kuma hula fara wannan sune kalar suturar dana fi so musamman lokacin zuwa idi. Batun babu zabi duk wanda na samu zan ci, amma nafi son biskin alkama da miyar yakuwa ko jar miya. To da farko dai Masallacin idi shi ne guri na farko, sannan kuma sai ziyarce-ziyarce gidajen ‘Yan’uwa da abokan arziki.
Sunana Zainab Zeey Ilyas Jihar kaduna:
An yi wa sallah tanadi da dama kamar kayan da za a sa, Lalle, kitso, da sauransu. Bana tunanin gaskiya akwai wani anko da aka fitar domin a halin yanzu ko wa abin da Allah ya hore mai zai saka. Ina son saka shadda mai ‘stones’, ina son cin funkaso, tuwon shinkafa da miyar Agushi wadda ta ji ganda, kaji da kayan ciki, sai lemon ginger, sai farfesun zallar naman zabi.
Sunana Anas Bin Malik Achilafia Yankwashi A Jihar Jigawa:
Ana yin tanadi wa bukukuwan Sallah da yawa, amma dai ni kam babu tanadin dana yi wa sallar bana, batun anko ko yayin kayan da ake siya, ni dai kam har yau ban lura ba, amma dai bana Iyalai na suna sha’awar Shadda, kuma gaskiya ba na ina sha’awar cin sakwara da hadadden lemu (Ubangiji Allah ka kara hore mana). A bisa al’ada kuma muna kaiwa ‘yan’uwa da abokan arzuka ziyara, tare da taya murnar kammala ibada. Ubangiji Allah karva mana ibada, ya sa mun dace.
Sunana Muhammad Isah Zareku Miga A Jihar Jigawa:
Tanadin dana yi wa wannan sallah shi ne ina so ta same ni cikin koshin lafiya da kuma ‘yan canji a cikin aljihuna. Wannan shekarar ta zo da son yin wankan shadda wato shampoo ita ce kowacce saurayi ko budurwa take/yake son sakawa duk da tsadar rayuwa da muke fama da ita. Ina sha’awar saka farar sutura ko shadda da farar hula a lokacin tafiya sallar idi. Abincin da nake muradin ci sh ine funkaso da jar Miya da naman kaji. Ina son kai ziyara zuwa gidan ‘Yan’uwa da abokan arziki in sha Allah.
Sunana Lawan Isma’il (Lisary) Jihar kano Rano LGA:
Babban tanadi shi ne Allah ya nuna mana ita muna raye da koshin lafiya. Haka ne kam duk da ana cikin yanayi ba za a rasa wadanda suka yin ba amma mu masu iyali iya yaranmu da iyayensu muka samu muka yi wa. da son samune ni dai sabuwar shadda fara idan kuwa ba ita ba to na sami koda koriya ce ko yadi shi ma fari ko koren. Waina da kunun daka ko na alkama da miya. Bayan dawowa daga sallar idi zan je gidan mahaifina da kuma gidan surukaina sai kuma na ‘yan’uwa da abokaina na kusa domin kara sada zumunci. Allah ya karvi ibadunmu.
Sunana Aisha T. Bello Jihar kaduna:
Sallah bikin daya rana in ji masu magana, a gaskiya na yi ma wannan sallah tanadi babba in Allah ya sa muna da rabon gani. Zan sanyaya raina ta samar da abun da na fi so a ci da sha, zan kai ziyara, zan je kallon hawan sallah, sannan zan kikkira ‘yan’uwa domin taya su barka da sallah da yardar Allah. A gaskiya bana jin wannan sallar akwai wani tanadi na anko kamar kullum, duba da yanayin rayuwa ana ta abun ci da sha ne, ina sha’awar saka doguwar riga da salla in sha Allah, sannan in sa babban mayafi in halarci sallar idi. In Allah ya ba ni dama ina so in kai ziyara jihar katsina don ganin dangina da ‘yan’uwa in sha Allah.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp