Leadership News Hausa:
2025-03-31@04:32:14 GMT

Ina Mafita Game Da Ƙalubalen Ƙarancin Abinci A Nijeriya

Published: 28th, March 2025 GMT

Ina Mafita Game Da Ƙalubalen Ƙarancin Abinci A Nijeriya

Jihohin da wannan matsalar ta fi shafa sun hada da, Zamfara, Borno, Yobe da kuma Katsina, musamman duba da yadda aukuwar yawan rikice-rikice, ya tarwatsa rayuwar miliyoyin alumomin yakin da fadawa cikin kangin fatara da yunwa da kuma rashin samun wadataccen abinci.

A ra’ayin mu, matsalar karancin abinci a kasar nan, ba voyayayen abu bane, musammamn duba da cewa, yawan aukuwar tashe-tashen hankula, kalubalen rashin tsaro da matsatin tattalin arziki, suna manyan hummulhaba’isin da ke janyo karancin abinci a a cikin alumma.

Misali, yawan samun hare-haren ‘yan bindiga a yankin kudu maso gabas, ayyukan ‘yan bindiga daji a yankin arewa masu yamma da kuma rikice-rikicen kabilanci a sauran yankuanan, sun janyo tarwatsa miliyoyin alumomi daga matsugunan su, lalata gonakansu wanda hakan ya janyo, aka samu raguwar noma amfanin gona, sauyar da amfanin gonar, inda hakan ya kuma haifar da karancin abinci a cikin alumma tare da samun hauhawan farashin kayan abinci.

Akasarin fannin noma a kasar nan, ya dogara ne kachokam kan samun ruwan damina, inda kuma fanin ke cin karo da samun sauyin yanayi, wanda hakan ke sanya wa a fusaknaci fari ko sauyin samun yanayin saukar ruwan sama da kuma akuwar annobar ambaliyar ruwan sama, inda hakan ke yiwa amfanin gona da aka shuka illa da kuma shafar dabbobi.

Wannan matsalar ta ambaliyar ruwansaman ba wai ta tsaya a kan amfanin gona bane, ta na kuma lalata matsunan alumma da kuma kara haifar da talauci a tsakanin su.

Sauye-sauye na dogon zango kan tattalin arziki da Gwamnatin Tarayya mai ci ta kirkiro da su a shekarar 2024 ta kuma wanzar da su, sun kasance za su iya janyo nakasu, a yunkurin da ake yi na samar da wadataccen abinci a kasar nan.

Duba da yadda ake ci gaba da samun hauhawan farashin kaya, karyewar darajar Naira, samun karuwar farashin man fetur, hakan yakara haifar da tsadar noma amfanin gona, tsadar sufuri, wanda hakan zai kara sanya wa masu sayen kayan abincin, su saya da tsadar gaske.

Bugu da kari, matsain na tattalin arzikin ya kuma janyowa alumma rashin samun wasu abubuwa kamar na iya kula da kiwon lafiyarsu da ci gaba da daukar nauyin karatun ‘ya’yansu.

Hukumar FOA tare da sauran masu ruwa da tsaki da suka hada da sasshen samar da abinci na Majalisar dinkin Duniya wato WFP da Asusun tallafawa kanannan yara na Majalisar dinkin Duniya UNICEF, Gidanuniyar Kula da kananan Yara da kuma kungiyar Kare Raji ta Mercy Corps, sun jima suna jaddada mahimmancin daukar matakan gaggawa na jin kai kafin aukuwar dukkanin wata annoba.

Daga cikin sakamkon taro na CH da aka gudaanr a Abuja wakilin FOA Nijeriya Kouacoau Dominikue Koffy ya jabawa Gwamnatin Tarayya da kuma masu ruwa da tsaki a CH, musamman bisa mayar da hankali da suka yi wajen ganin an samar da wadataccen abinci da kuma sanya ido da suke yi don a samar da wadataccen abincin.

Ya kuma yi kira ga Gwamnatocin Jihohi da sauran abokan hadaka da su zuba kudade domin a wanzar da tsarin na kasa da a za a gudanar a watan Okotobar 2025, inda ya yi nuni da cewa, ba tare da an samar da bayanai da samar da kyakyanwan shiri zai yi wuya, a cimma burin da aka sanya a gaba.

A ra’ayin wannan jaridar, mun yi amannar cewa, kalubalen karancin abinci abu ne da ke bukatar hada karfi da karfe, wanda hakan zai wuce batun siyasantar da maganar da shelanta samar da Rumbunan adana hatsi.

Ya zama wajibi Gwamnatin Tarayya ta ayyana dokar ta vaci wajen samar da wadataccen abinci tare da kafa tawaga mai karfi da za ta hada da Ma’aikatun Gwamnati, Hukumomin Tsaro, kungiyoyin Jin kai, Kamfanonin Masu Zaman Kansu da sauran masu ruwa da tsaki, musamman domin a samar da tare da kaddamar da kyakyawan tsari na kasa.

Dole ne Gwamnatocin Jihohi su marawa kokarin da Gwamnatin Tarayya ke yi kan zuba nannun jari wajen samar da abinci, samar da kayan adana amfanin gona, tsarin rabar da amafnin gonar, kuma kamfanoni masu zaman kansu, musamman masu yin noma domin samun riba, suma suna da gudunmawr da za su bayar wajen kara bunkasa fannin aikin noma, musamman domina a tabbatar da cewa, abincin ya isa ga teburin, musamman marasa karfi, wadanda kuma za su rinka sayen abincin, a cikin farashi mai sauki.

Ya zama wajbi UNICEF, FAO, WEF, da sauran takwarororin su, da su kara kaimi wajen aikin sa kai a yankunan da karancin abinci ya fi kamari, domin taimakawa Gwamnati wajen wanzar da aikin na dogon zango.

A zaman mu na kasa, ba ta savu mu yi ikirarin cewa, kasar na kan turba ba, bayan alhali, ‘yan kasar na ci gaba da fuskantar yunwa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Ra ayinmu samar da wadataccen abinci karancin abinci a Gwamnatin Tarayya wanda hakan

এছাড়াও পড়ুন:

Manyan Amfanin Gona Biyar Da Ya Kyautu Manoma Su Zuba Hannun Jari A 2025

Manyan Matakai Biyar Da Manoma Da Masu Zuba Hannun Jari A Fannin Aikin Noma Ya Kamata Su Yi La’akari Da Su Kamar Yadda kwararrun Suka Bayar Da Shawara:

1- Irin Kwakwar Manja Na Malesiya

Bukatar da ake da ita ta Irin Kwakwar Manjan Nijeriya a duk shekara, ya kai na tan miliyan 3, inda kuma wanda ake samarwa a cikin kasar, ya ragu da tan miliyan 1.4.

Kazalika, a gonar da ake noman Kwakwar Manja, za a iya samar da tan 12.5 a kowace hekta daya a duk shekara. Misali, a 2023 a heckta 20 a cikin shekara daya, an girbe Kwakwar da ta kai kimanin tan 250, inda akalla aka samu ribar kimanin Naira 150,000 na kowanne tan daya, wanda kuma ke nuna karin samun kudin shigar da ya kai Naira miliyan 37.5.

Hakan ya kuma kara nuna yadda aka kara bunkasa samun kudin shiga a shekarar da kimanin Naira miliyan 26.25.

2- Gonar  Noman Filanten:

Nijeriya ce kan gaba a duniya wajen noman Filanten, duba da cewa; a duk shekara ana noma amfanin da ya kai kimanin tan miliyan 2.8 zuwa tan miliyan 3.1.

Idan kana da Naira miliyan 5, za ka iya mallakar hekta ta noman Filanten, amma ya danganta da inda gonar taka take.

Haka zalika, bisa bai wa gonar kulawar da ta kamata, a tushe daya na Filanten a shekara, za a iya samar kimanin rassa 10,000.

Sannan, duk Nono daya na Filanten, ana sayar da shi daga Naira 2,000 zuwa Naira 4,000, inda a shekara daya, za a iya tara sama da Naira miliyan 40, wato tun daga wata 18 da aka shuka Irin nata.

Kulawar da ake ba shi a shekara bayan an shuka Irinsa, har zuwa girmansa da fara nunarsa, an kiyasata ana kashe sama da Naira miliyan 2, inda manoman za su iya samun ribar sama da miliyan 18 ko fiye da haka a shekara daya.

3- Gonar  Noman Dabino:

Nijeriya ce kan a gaba a Afirka wajen noman Dabino, duba da cewa; an kiyasta cewa, a shekara daya ana noma sama da tan 250,000.

Sai dai, abin takaici a 2024, Nijeriya ta shigo da Dabino daga ketare da ya kai na dala miliyan 17.8, inda kasar kuma ta fitar da Dabinon na kimanin dala miliyan 2,070 kacal.

Amfanin da ake yi da shi a duniya a shekara daya, ya kai akalla na tan miliyan 8.5, inda a gabas ta tsakiya da Afirka ta tsakiya, suka kasance kan gaba wajen nomansa da kuma rabar da shi.

Dabino na kaiwa tsawon shekara biyar kafin ya fara yin ‘ya’ya.

4- Irin Kwaka Na Malesiya:

A cewar wasu bayanai da Hukumar Kula da Samar da Abinci da Aikin Gona ta Duniya (FAO) ta fitar, ta dora Nijeriya kan mataki na 18 wajen noman Kwaka a duniya, duba da cewa; kasar na noma Kwakawar da ta kai kimanin tan 225,526 2021.

Wanda ya zuba hannun jari a fannin, zai  iya samun ribar sama da Naira miliyan 36 daga hekta goma da aka noma. Samar da heckta 10 a gonar noman Kwaka, zai kasance daidai da zuba hannun jari na kimanin Naira 26,550,000.

Idan har aka shuka ta, a kowace bishiya daya a shekara za ta iya samar da ‘ya’ya 100 , inda za su kai yawan ‘ya’ya 70 da za a girbe a shekara guda.

Kowane Nono daya na Kwakawar, za a iya sayar da shi kan Naira 900, wanda kuma za a iya samar da kudin shiga kimanin Naira  63,000,000 a shekara daya.

Kazalika, bayan ware kudin aikin da manomi ya kashe, zai kuma iya samun ribar da ta kai ta Naira 36,450,000 a shekara daya.

5- Gonar Noman Kashu:

A cewar wani rahoto da jaridar ‘The Nation’ ta wallafa, sama da hecta 600,000 aka ware domin nomansa, wanda zai iya samar da kimanin tan 220,000 a shekara. Farashin Kashu, ya kai daga tan Naira miliyan daya zuwa Naira miliyan 1.5.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Eid-el-Fitr: Sarkin Kauru Ya Gargadi Masu Bai Wa ‘Yan Ta’adda Bayanai
  • Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Legas, Mutane 10 Sun Kamu
  • Eidl Fitr: Gwamna Dauda Lawal Ya Buƙaci A Samu Haɗin Kai Da Zaman Lafiya
  • Me Ya Sa Fina-finai Masu dogon Zango A Masana’antar kannywood ke Zama Cin kwan Makauniya?
  • Manyan Amfanin Gona Biyar Da Ya Kyautu Manoma Su Zuba Hannun Jari A 2025
  • Taron Boao Ya Sake Ba Duniya Damar Ganin Abubuwa Masu Jan Hankali Game Da Sin
  • WFP: Yara Miliyan 11 Na Fama Da Karanci Abinci A Nijeriya
  • Duk Da Dokar ‘Yancin Samar Da Abinci: Yara Miliyan 11 Na Fama Da Ƙaranci Abinci A Nijeriya
  • Gwamnatin Amurka Tana Shirin Dakatar Da Bada Kudaden Tallafi Don Samar Da Wasu Magunguna