Kamun Akanta-janar Take-taken Toshe Bakin Gwamnan Bauchi Ne – Ƙungiya
Published: 28th, March 2025 GMT
kungiyar ta koka kan cewa bai dace a yi amfani da EFCC wajen kamun Jami’an gwamnatin jihar Bauchi da nufin nuna yatsa wa Gwamna Bala Muhammad wanda ya kasance mai fitowa da hakikanin gaskiyar halin da talakawa ke ciki da nema musu hakkinsu daga wajen shugaban kasa.
kungiyar ta lura da cewa in ana amfani da irin wannan salon lallai za a samu nakasu wajen kyautata demukradiyya a kasar nan domin mutane da dama za su yi shiru kan abubuwan da suke tafiya ba daidai ba domin gudun musgunawa.
Eyes on Democracy ta kuma nuna shakku kan yadda aka kama Akanta Janar din a lokacin da yake halartar taron FAAC a Abuja, inda ta bayyana cewa hukumar EFCC ba ta gayyace shi ba balle ya ki zuwa da har za a dauki matakin kamashi.
“Babu ko shakka cewa Gwamna Bala Mohammed yana tafiyar da harkokin kudi da dukiyar jihar cikin tsanake da gaskiya, a karkashin shugabancinsa jihar Bauchi na samun ci gaba da ba a tava ganin irinsa ba kuma cikin sauri a sassa daban-daban,” kungiyar ta shaida.
Ƙungiyar ta bukaci ‘yan Nijeriya, kungiyoyin farar hula, da sauran kasashen duniya da su lura da wadannan ayyukan da ba su dace da tsarin dimokradiyya ba, su bijirewa duk wani yunkuri na mayar da hukumar EFCC dandalin cin zalin siyasa.
Bugu da kari, kungiyar ta yi kira ga hukumar EFCC da ta yi aiki bisa doka, sannan ta bukaci da a gaggauta sakin Akanta Janar din, idan har akwai zarge-zarge na gaskiya da ake yi masa, kungiyar ta dage cewa a bi su kamar yadda doka ta tanada.
“Muna tsayawa tsayin daka da Gwamna Bala Mohammed da dukkan masu fada a ji na gaskiya da adalci a Nijeriya. Babu wata barazana da za ta hana a gudanar da gangamkn na tabbatar da dimokuradiyya, gaskiya da rikon amana,” in ji ƙungiyar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: kungiyar ta
এছাড়াও পড়ুন:
Benuwe: Har yanzu ba a gano wasu mutanen ƙauyuka ba – Gwamna Alia
Rundunar ’yan sandan Jihar Benuwe a ranar Alhamis ta tabbatar da cewa an samu kwanciyar hankali a unguwar Otobi da ke Ƙaramar hukumar Otukpo biyo bayan wani mummunan hari da ya tilastawa mazauna garin barin gidajensu.
Kakakin rundunar ’yan sandan, CSP Catherine Anene a wata tattaunawa ta wayar tarho da wakiliyarmu, ta kuma yi watsi da rahoton sabbin hare-haren da aka kai kan unguwannin Emichi, Okpomaju da Odudaje, inda ta bayyana su a matsayin rahoton ƙarya don yawo tsoratar da jama’a.
An kashe sojoji, fararen hula da dama a Borno ’Yan Najeriya miliyan 150 sun samu ingantacciyar wutar lantarki – Minista“Unguwar Otobi yanzu akwai kwanciyar hankali, mun bar wasu jami’anmu tun ranar Laraba ana gudanar da bincike,” in ji Anene.
A halin da ake ciki, Gwamnan Jihar Benuwe, Hyacinth Alia ya bayyana cewa har yanzu ba a gano wasu mutanen ƙauyen ba bayan harin.
“Mun yi asarar mutane 11. Mun tura ƙarin jami’an tsaro,” in ji gwamnan yayin wani taron manema labarai inda ya bayyana hare-haren a matsayin batun ƙwace fili.”
Da yake mayar da martani kan wannan ci gaban, Sanata mai wakiltar mazaɓar Benuwe ta Kudu kuma shugaban marasa rinjaye na Majalisar Dattawa, Abba Moro ya yi gargaɗin cewa idan gwamnati ta ci gaba da gazawa wajen kare rayuka, al’ummarsa za su iya amfani da hanyoyin kare kansu.
Sanatan, a cikin wata sanarwa da Emmanuel Eche’Ofun John, mashawarcinsa kan harkokin yaɗa labarai ya fitar, ya bayyana cewa hare-haren da suka janyo asarar rayuka da dukiyoyi na biliyoyin Naira abu ne da ba za a amince da su ba.
Ya kuma yi kira ga gwamnatoci a kowane mataki da su tashi tsaye wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
Ya kuma yabawa Gwamna Alia da a ƙarshe ya fito ya yi Allah-wadai da wannan aika-aika a jihar, ya kuma buƙace shi da ya ƙara yi wa al’umma aiki, yana mai jaddada cewa ƙoƙarin gwamnati a dukkan matakai bai isa ba.
Moro ya kuma yi kira da a kafa sansanonin hukumomin tsaro a cikin unguwannin jama’a masu rauni