Ranar idin Karamar Sallah rana ce da Musulmi ke farin cikin kammala azumin watan Ramadan wacce ke zuwa a ranar daya ga watan Shawwal din shekarar Musulunci.
Allah Madaukakin Sarki ya shar’anta Sallar Idi a matsayin ibadar kammala Azumin Ramadan wacce take kan kowane Musulumi, baligi, mai hankali, kuma mazaunin gida — namiji ko mace.
A yayin da ake shirin shan shagalin Kamar Sallah, malamai sun bayyana muhimman abubuwan da ya kamata su aikata a ranar, kamar yadda Hadisan Annabi (SAW) suka nuna:
Duk Musulumi maza da mata manya da kanana su halarci sallar Idi. Fitar da zakkar fid da kai, wato Zakkar Kono. Cin dabino ko abinci kafin zuwa Sallar Idi. Yin wankan idi kafin zuwa halartar sallar idi. Sanya sabbi ko mafiya kyawtun tufafi da mutum ya mallaka. Sanya turare da yanke farce Ana son sanya turare ga maza. Yawaitawa da kuma bayyana kabarbari ga maza da mata. Daina yin kabbarori daga lokacin da aka tayar da sallar.Allahu Akbar, Allahu Akbar, Allahu Akbar, LaiLaha illAllah, Allahu Akbar walillahil hamdu. Sauraron huduba bayan kammala Sallar. Zuwa sallar da dawowa ta hanyoyi daban-daban. Rashin zuwa da makami ko wani abu da zai razana mutane sallar idi. Ziyara da taya ’yan uwa da sauran murna.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Sallar Idi zakkar fidda kai Allahu Akbar
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnati Ta Ba da Umarnin Tafiya Yi Wa Ƙasa Hidima Ga Duk Masu HND
Yawancin wadanda suke da HNd basu samu damar tafiya aikin Yiwa kasa Hidima/Aikin Bautawa kasa wanda hakan ne kuma aka gay a kamata ayi masu adalci kan lamarin
Sai dai kuma irin ci gaban da aka samu ya kawo ko samar da wata matsala ta yadda wadanda suka yi karatun suka kammala a makaranta sai ta kasance wasu daga cikinsu basu samu damar tafiya aikinyiwa kasa hidima ba saboda irin karatun da suka yi.
Da yake bada ta shi gudunmawa darekatan lamurran ‘yan jaridu da hulda da jama’a ma’aikatar ilimi ta tarayya Boriowo Folasade, ya fitar da sanarwa wadda take tabbatar da gaskiyar lamarin na abubuwan da suka biyo bayan dukkan tarurrrukan da kuma ganawar da aka yi.
Sanarwa ta nuna cewa sabon matakin da aka dauka wani abin farincikine ga wadanda suka kammala karatun da ake samun Babbar difiloma ta kasa HNd wadanda a baya ba a basu damar tafiya wuararen da za su yiwa kasa hidima ba.
An ma bayyana cewar matakan da ma’aikatar ilimi ta tarayya ta dauka na tabbatar da cewar ana yin adalci ya kasance ana tafiya da kowa a lamarin ilimi na Nijeriya.
Su ma wadanda suka kammala karatun nasu ba irin na wadanda suka zauna a makaranta ba, suma za su iya je aikin yiwa kasa hidima na shekara daya da takwarorin su wadanda suka samu ko karatun da ya basu damar samun digiri suke yi.
Domin samu daukar mataki wanda ba’a vata lokaci ba an umarci Hukumar kula da ilimin daya shafi fasaha da kere- kere (NBTE)ta gaggauta samar da bayanai na wadanda suka kammala HNd domin tafiya harkar ta yi wa kasa hidama NYSC.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp