Ranar idin Karamar Sallah rana ce da Musulmi ke farin cikin kammala azumin watan Ramadan wacce ke zuwa a ranar daya ga watan Shawwal din shekarar Musulunci.
Allah Madaukakin Sarki ya shar’anta Sallar Idi a matsayin ibadar kammala Azumin Ramadan wacce take kan kowane Musulumi, baligi, mai hankali, kuma mazaunin gida — namiji ko mace.
A yayin da ake shirin shan shagalin Kamar Sallah, malamai sun bayyana muhimman abubuwan da ya kamata su aikata a ranar, kamar yadda Hadisan Annabi (SAW) suka nuna:
Duk Musulumi maza da mata manya da kanana su halarci sallar Idi. Fitar da zakkar fid da kai, wato Zakkar Kono. Cin dabino ko abinci kafin zuwa Sallar Idi. Yin wankan idi kafin zuwa halartar sallar idi. Sanya sabbi ko mafiya kyawtun tufafi da mutum ya mallaka. Sanya turare da yanke farce Ana son sanya turare ga maza. Yawaitawa da kuma bayyana kabarbari ga maza da mata. Daina yin kabbarori daga lokacin da aka tayar da sallar.Allahu Akbar, Allahu Akbar, Allahu Akbar, LaiLaha illAllah, Allahu Akbar walillahil hamdu. Sauraron huduba bayan kammala Sallar. Zuwa sallar da dawowa ta hanyoyi daban-daban. Rashin zuwa da makami ko wani abu da zai razana mutane sallar idi. Ziyara da taya ’yan uwa da sauran murna.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Sallar Idi zakkar fidda kai Allahu Akbar
এছাড়াও পড়ুন:
Mayaƙan ISWAP sun tarwatsa gada a Yobe
’Yan ta’addar ISWAP sun tarwatsa wata gada da ta haɗa garin Ngirbuwa da garin Goneri a Ƙaramar Hukumar Gujiba da ke Jihar Yobe.
Wannan na zuwa ne ƙasa da mako guda da ‘yan ta’addan suka lalata gadar nan ta Mandafuna da ta haɗa garin Biu da Damboa a Jihar Borno.
JAMB ta sauya ranar soma jarrabawar bana Manyan jami’an gwamnati sun halarci auren ’yar tsohon Gwamnan BauchiMajiyar leƙen asiri ta shaida wa Zagazola Makama cewa harin ya afku ne da misalin ƙarfe 10:30 na daren ranar ranar Alhamis ɗin da ta gabata, ta hanyar amfani da wani bam wajen lalata sauran sassan gadar.
Wannan aikin ta’addanci ya kawo cikas ga zirga-zirga tsakanin al’ummomin biyu da ma sauran al’ummomin yankin, lura da cewar gadar na kan hanyar Katarko ne zuwa garin Goneri.
Masana tsaro na nuna cewar, lalata wannan gadar mota na iya kawo cikas ga harkokin tsaro a wannan yanki, lura da cewar yankin na da iyaka da wasu dazuzzukan da ke da iyaka da dajin Sambisa da ya zama maɓoyar ‘yan ta’addan a wasu ɓangarorin.