Masarautar Kauru da ke jihar Kaduna ta jaddada kudirinta na tabbatar da tsaro, inda ta bukaci mazauna yankin da su kasance masu taka-tsan-tsan duk da ci gaban da gwamnati ta samu a baya-bayan nan wajen magance matsalar ‘yan fashi da garkuwa da mutane da kuma munanan hare-hare.

Mai martaba Sarkin Kauru, Alhaji Zakari Ya’u Usman na biyu, ya jaddada muhimmancin hadin kai wajen wanzar da zaman lafiya da tsaro a lokacin da ya gabatar da sakon Sallar a fadarsa da ke Kauru.

Alhaji Zakari Ya’u Usman ya kuma yi gargadi game da masu ba da labari da ke taimaka wa masu laifi tare da karfafa gwiwar mazauna yankin da su kai rahoton duk wani abu da ake zargi.

Dangane da harkokin kiwon lafiya, Sarkin ya bukaci iyaye da su ba da fifiko ga allurar rigakafin yara don kare su daga cututtukan da za a iya rigakafin su.

 

Ya kuma shawarci mata masu juna biyu da su rika zuwa duba lafiyarsu akai-akai, sannan ya shawarci jama’a da su nemi kulawar lafiya a kan lokaci domin rage kamuwa da cututtuka kamar hawan jini da ciwon suga.

A cewarsa, Masarautar ta nuna godiya ga gwamnatin jihar kan aikin hanyar Pambeguwa zuwa Kauru da kuma tallafawa manoma ta hanyar rabon taki. Sai dai Sarkin ya roki a kara ayyukan hanyoyin da suka hada da Kauru zuwa Mariri a karamar hukumar Lere, Unguwan Ganye zuwa Dokan Karji mai hade da Kasuwan Magani a karamar hukumar Kauru, da kuma titin mai tsawon kilomita 10 a cikin garin Kauru.

Ya kuma bukaci a kammala kashi na biyu na gyaran fadar Kauru, musamman a wuraren da ke bukatar kulawar gaggawa, musamman a lokacin damina.

Sarkin ya yi addu’a don ci gaba da zaman lafiya da wadata a shekaru masu zuwa.

 

Hakazalika, Sakataren Masarautar, Malam Muhammad Sani Suleiman (Danburan Kauru) ya nuna jin dadinsa ga wadanda suka halarci bukukuwan Sallah tare da jajantawa iyalan wadanda rashin tsaro ya shafa.

COV/Yusuf Zubairu Kauru

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Yan Ta adda Bayanai Gargadi Sarkin Kauru

এছাড়াও পড়ুন:

Iran: Amurka ta hada kai da Isra’ila wajen kawo cikas ga harkar tsaro a gabas ta tsakiya

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce Amurka na da hannu a ayyukan haramtacciyar kasar Isra’ila na yada rashin tsaro da zaman lafiya a yankin.

A wata ganawa da ya yi da Hans Grundberg, wakilin Majalisar Dinkin Duniya na musamman a kasar Yemen a birnin Tehran, Araghchi ya yi Allah wadai da ci gaba da hare-haren soji da Amurka ke kaiwa sassa daban-daban na kasar Yeman, wanda ke sanadin mutuwar fararen hula da kuma lalata kayayyakin more rayuwa.

Ya kara da cewa: Hare-haren da sojojin Amurka suke kai wa kasar Yamen, wanda ya zo daidai da irin yadda gwamnatin sahyoniyawan ke ci gaba da aiwatar da kisan gilla a zirin Gaza da kuma hare-haren da take kaiwa kasashen Lebanon da Siriya, wata alama ce kawai da ke nuna irin hadin kai da Amurka take yi da Isra’ia wajen rashin bin doka da oda da kuma yadda take da alaka da ayyukan Isra’ila wajen yada rashin tsaro da zaman lafiya a yankin.

Ya bayyana cewa Amurka tana da rashin fahimtar mutanen Yemen, wanda kuma yana da kyau ‘yan siyasar Amurka da su gane cewa ci gaba da mamaye da kisan kiyashi a Falasdinu shine tushen rashin tsaro a yankin.

Dole ‘yan siyasar Amurka su fahimci cewa Amurka ba za su  iya da’awar maido da kwanciyar hankali a yankin ba ta hanyar kai hari kan Yemen da kashe mutanen Yemen da ba su ji ba ba su gani ba,” in ji Araghchi.

Ya kara da cewa laifin al’ummar kasar Yaman shi ne hadin kai da goyon bayansu ga al’ummar Palastinu da ake zalunta.

Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya soki kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da kin daukar wani mataki dangane da keta ka’idojin yarjejeniyar MDD da kuma dokokin kasa da kasa da gwamnatocin Amurka da Isra’ila suke yi.

Ya ce ya kamata Majalisar Dinkin Duniya ta dauki matakai cikin gaggawa don kawo karshen karya doka da rashin mutunta ka’idojin kasa da kasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NUJ Kebbi Tayi Kiran Ayi Bukukuwan Sallah Lafiya
  • Tsohon Gwamnan Zamfara Ya Bukaci A Ci Gaba Da Tallafawa Mabukata Bayan Ramadan.
  • Nijar ta fice daga rundunar MNJTF mai yaƙi da masu iƙirarin jihadi
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci: Kasashen Yamma Sune Yan Ta’adda Na Gasliya A Yankin
  • Sarkin Gombe ya nemi manoma da makiyaya su zauna lafiya
  • Iran: Amurka ta hada kai da Isra’ila wajen kawo cikas ga harkar tsaro a gabas ta tsakiya
  • Eidl Fitr: Gwamna Dauda Lawal Ya Buƙaci A Samu Haɗin Kai Da Zaman Lafiya
  • Bayan Hukuncin ‘Yansanda, Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah
  • An Gudanar Da Gagarumar Zanga- Zanga Ta Ranar Qudus Ta Duniya A Birnin Roma Na Kasar Italiya