Iran: Tattaunawa kai tsaye da Amurka a yanzu ba shi ne zabinmu ba
Published: 9th, April 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya yi martani ga kalaman shugaban Amurka Donald Trump na baya-bayan nan game da yiwuwar tattaunawa da Iran kai tsaye, inda ya yi karin haske kan matsayar Tehran, kamar yadda jaridar Washington Post ta kawo.
Araghchi ya bayyana imaninsa cewa irin matakan da Iran ta dauka a baya-bayan nan dangane da wannan tattaunawa wani babban yunkuri ne na diplomasiyya.
Ya fayyace cewa sabanin wasu fassarori da aka yi a baya-bayan nan a game da batun tattaunawa tsakanin kasashen biyu, inda ya ce kokarin bayyana ra’ayi ne na gaskiya da bude hanyar diflomasiyya.
Dangane da kalaman Trump da ya yi a ranar litinin, Araghchi ya bayyana cewa Iran a shirye take domin ganin an cimma matsaya, inda za ta halarci tattaunawa a kasar Oman a ranar Asabar.
Ya kuma kara da cewa, wannan ba sabon lamari ba ne, domin ita kanta Amurka tana tsakiyar yin shawarwari kai tsaye game da batun Rasha da Ukraine, batun da ya fi zafi da sarkakiya ta fuskar siyasa da tattalin arziki a mataki na kasa da kasa.
Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya bayyana cewa yana da gogewa a baya a tattaunawar kai tsaye da Amurka wacce kungiyar EU ta shiga tsakani a shekarar 2021.
Araghchi ya bayyana cewa duk da cewa ba a cimma matsaya ba a lokacin, amma da farko lamarin ya faru ne saboda rashin azama ta gaskiya daga gwamnatin Biden.
Ya ci gaba da cewa tattaunawar kai tsaye zabi ne wanda zai iya yiwuwa, amma kuma saboda masaniya a kan abubuwan da suka faru a baya Iran tana da cikakiyar masaniya da gogewa game da salon tattaunawa da Amurka, domin kuwa Iran ba ta amince da Amurka ba, amma kuma hakan ba zai hana tattaunawa ba.
Ya kara da cewa, Iran ba za ta taba amincewa da tattaunawa karkashin matsin lamba da kuma barazana ta sojia kanta ba, amma za ta amince da tattaunawa ne kawai a karkashin fahimta da kuma girmamma juna.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Araghchi ya
এছাড়াও পড়ুন:
Babu Wani Saɓani Tsakanin Tinubu Da Shettima — Jigon APC
Ya ce a siyasa akwai nau’ukan mutane uku – masu gaskiya, maƙaryata, da masu son tada zaune tsaye.
Ya ce su a matsayinsu na ‘ya’yan jam’iyyar APC na gaskiya, suna goyon bayan Tinubu da Shettima, kuma idan akwai kura-kurai, suna ganin ya kamata a gyara ne, ba a lalata komai ba.
Dangane da raɗe-raɗin cewa ana shirin sauya Shettima kafin zaɓen 2027, Jalo ya ce wannan ma labarin ƙanzon kurege ne.
Ya ce jam’iyya tana da hanyarta na sauya mutum, amma babu wani abu makamancin haka yanzu.
Ya ƙara da cewa suna jiran 2031 domin Shettima ya fito takarar shugaban ƙasa.
Har ila yau, ya buƙaci masu yaɗa jita-jita da su janye maganganunsu, su jira domin idan akwai matsala, za ta bayyana kanta.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp