Aminiya:
2025-04-12@21:23:13 GMT

Za a ci gaba da sayar da ɗanyen mai a farashin Naira — Gwamnati 

Published: 9th, April 2025 GMT

Gwamnatin Tarayya ta tabbatar da cewa za ta ci gaba da sayar da ɗanyen mai da man da aka tace farashin Naira, maimakon amfani da dalar Amurka.

Wannan mataki na daga cikin manufofin gwamnati na bunƙasa tattalin arziƙin cikin gida, rage matsin lamba kan kasuwar musayar kuɗi, da kuma bunƙasa makamashi.

’Yan bindiga sun mamaye garuruwa 64 a Filato — Gwamna Mutfwang ’Yan bindiga sun kashe masunta 3 a Sakkwato

Ma’aikatar Kuɗi ta bayyana hakan ne a shafinta na X, inda ta ce wannan ba mataki ne na wucin-gadi ba, sai dai tsari ne da ake son ya ɗore wanda Majalisar Zartaswa ta Ƙasa, ta aminta da shi.

“Wannan manufa za ta taimaka wajen bunƙasa tace mai a gida, rage dogaro da dala, da kuma inganta tsaro a fannin makamashi a Najeriya,” in ji Ma’aikatar.

“Wani muhimmin ɓangare ne na shirin gwamnati don kare makomar tattalin arziƙin ƙasa.”

A ranar Talata ne manyan jami’an Ma’aikatar Kuɗi, NNPCL, FIRS, CBN, da wasu manyan hukumomi suka gana domin duba yadda aikin ke tafiya da kuma magance matsalolin da ka iya tasowa a tsawon lokacin aiwatar da shirin.

“Mun fahimci cewa sauye-sauye irin wannan suna zuwa da ƙalubale,” in ji wani jami’i daga cikin mahalarta taron.

“Amma dukkanin hukumomin da ke da hannu a cikin shirin sun ƙudiri aniyar ganin an cimma nasara.”

A baya-bayan nan NNPCL ya daina sayar wa matatar Dangote ɗanyen mai a farashin Naira bayan ƙarewar yarjejeniyar da suka ƙulla.

Hakan ya haifar da tashin farashin man fetur a gidajen mai a faɗin ƙasar nan, lamarin da masana suka ce hakan zai sake shafar tattalin arziƙin Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dalar Amurka ɗanyen mai farashi Ma aikatar Kuɗi Naira

এছাড়াও পড়ুন:

Macron :  Faransa na shirin amincewa da yankin Falasdinawa a matsayin kasa

Shugaban kasar Faransa, Emmanuel Macron, ya ce kasarsa na shirin amincewa da yankin Falasdinawa a matsayin kasa nan da watanni masu zuwa.

Ya ce hakan na iya faruwa a farkon watan Yuni nan wannan shekarar a taron Majalisar Dinkin Duniya da za a gudanar a New York.

kawo yanzu, Kasashe 147 ne suka amince da yankin na Falasdinawa a matsayin kasa mai yanci.

Kasashen Sifaniya da Ireland da Norway su ne na baya-bayan nan da suka nuna amincewarsu a watan Mayun bara da yankin na Falasdinawa a matsayin kasa mai yanci, matakin da ya fusata Isra’ila.

Kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa da dama dai na ganin samar da kasashe guda biyu Falasdinu da Isra’ila shi ne gimshikin samar da zaman lafiya a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  A Yau Asabar Ne Ake Bude Tattaunawa A Kasar Oman Akan Shirin Makamashin Nukiliyar Iran
  • Basukan Da Nijeriya Ke Biya Sun Karu Zuwa Naira Tiriliyan 13
  • Rayuwar ‘Yan Arewa Na Cikin Hadari, Yayin Da Gurbataccen Gishiri Ya Fantsama A Kasuwanni
  • Yadda Bankin Stanbic IBTC Ke Bunkasa Tattalin Arzikin Abokan Huldarsa
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Zai Shafi Rayuwar ’Yan Najeriya
  • Gwamnati ta gargaɗi jihohi 30 kan ambaliyar ruwa
  • Matatar Ɗangote ta rage farashin fetur zuwa N865
  • Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur 
  • Macron :  Faransa na shirin amincewa da yankin Falasdinawa a matsayin kasa
  • Majalisar Kano Ta Yi Murna Da Lambar Yabo Da Jaridar LEADERSHIP Ta Bai Wa Abba