Aminiya:
2025-04-12@21:31:56 GMT

NAJERIYA A YAU: Tasirin ’Yan Uwantaka Ga Rayuwar Al’umma

Published: 10th, April 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Irin alaƙar da ke tsakanin wasu abokai na da matuƙar kusanci da kyau, ta yadda a wasu lokutan ma ba a iya banbance dangantakar tsakaninsu ta ’yan uwan na jini ko kuma abota.

Irin wannan dangantaka ya kamata ne a ce ana samun ta a tsakanin ’yan uwa na jini.

Sai dai a yayin da wasu ke samun kyakkyawan dangantaka tsakaninsu da ’yan uwan su na jini, wasu kuwa ba sa ga-maciji da nasu ’yan uwan da suke uwa ɗaya uba ɗaya.

NAJERIYA A YAU: Dabarun Samun Kuɗaɗe Ta Hanyar Amfani Da Wayar Hannu DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa ‘Matar Bahaushe Ba Ta Iya Kiran Sunan Mijinta’

Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari ne kan irin tasirin da ’yan uwantaka ke da shi ga rayuwar mutum.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan uwa

এছাড়াও পড়ুন:

Femi Falana SAN Ya Yi Kiran A Inganta Harkar Shari’a A Najeriya

Lauyan kare hakkin bil’adama Femi Falana SAN ya yabawa jihar Kano bisa yadda take tafiyar da harkokin shari’a.

 

Falana ya bayyana hakan ne a yayin wani taron karawa juna sani ga masu gabatar da kara kan ingancin gudanar da shari’ar laifuka da Kurawa Hussein And Associates tare da hadin giwar Ma’aikatar Shari’a ta Kano suka shirya, wanda aka gudanar a otal din Bristol Kano.

 

 

Falana ya yabawa jihar Kano bisa amincewa da dokar hukumar kula da laifuka ta FIDRA a shekarar 2019 tare da zama jiha ta farko da ta soke tuhumar da jami’an ‘yan sanda ke yi na aikata laifuka.

 

Ya kuma jaddada bukatar masu gabatar da kara su samar da na’urori na zamani da horarwa masu inganci don bunkasa ayyukansu.

 

 

Falana ya kuma jaddada mahimmancin inganta yanayin aiki ga masu gabatar da kara don ba su damar mai da hankali kan ayyukansu.

 

 

Kungiyar kare hakkin dan Adam ta bayyana irin kalubalen da talakawa ke fuskanta wajen samun adalci, inda ta bayyana yanayin tattalin arziki da kuma bukatar gwamnati ta shiga tsakani.

 

Falana ya ba da shawarar cewa a baiwa ofishin kare hakkin jama’a ikon taimakawa talakawa, tare da kasancewa a kowace karamar hukuma.

 

“Hakan zai baiwa talakawa damar samun adalci da kuma samun lauyoyin da za su gudanar da shari’o’insu, inda ya ba da misali da hukumar ba da agajin lauya ta kasa (Legal Aid Council) wacce ke da ofisoshi a dukkan jihohin kasar nan 36.

 

 

Falana ya kuma jaddada mahimmancin kare hakkin wadanda ake tuhuma da kuma karfafa amincewa da tsarin shari’a.

 

 

Ya kara da cewa wadanda ake tuhuma suna da ‘yancin neman a ba su lauya, kuma dole ne ‘yan sanda su tuntubi hukumar bayar da agaji ta Legal Aid don samar da lauya. Ya kuma bukaci kafafen yada labarai da su taka rawa wajen wayar da kan jama’a, game da hakkokinsu a karkashin doka.

 

Femi Falana SAN ya yi kira ga kafafen yada labarai da su rika wayar da kan jama’a domin su sanar da jama’a hakkinsu a karkashin doka.

 

 

Cover /Abdullahi jalaluddeen/Kano

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsohon kocin Super Eagles Christian Chukwu ya rasu
  • Yadda Rashin Ilimi Ke Cutar Da Rayuwar Al’umma
  • Najeriya Ta Jaddada Aniyar Aiwatar Da Sakamakon Taron FOCAC Na Beijing
  • Waraka Daga Bashin Ketare
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Zai Shafi Rayuwar ’Yan Najeriya
  • Gwamnatin Kano ta tura tawaga zuwa Edo kan kisan mafarauta
  • Yadda masu safarar ɗan Adam ke yaudarar mutane ta intanet
  • ECOWAS ta damu da takun-tsaka tsakanin Aljeriya da Mali
  • Femi Falana SAN Ya Yi Kiran A Inganta Harkar Shari’a A Najeriya