Jawabin shugaban majalisar, ya biyo bayan dambarwar hankalin al’ummar kasar ne, bayan shelar ranar 18 ga watan Maris da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi na ayyana dokar ta-baci na tsawon wata shida a Jihar Ribas. Matakin ya zo ne daidai lokacin da rikicin siyasa ke kara kamari, inda aka dakatar da Gwamna Siminalayi Fubara tare da rusa majalisar dokokin jihar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Gargadi

এছাড়াও পড়ুন:

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Ya Yi Bikin Easter Tare da Al’ummomin Kiristoci

 

Makera, Jihar Kaduna – Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, Rt. Hon. Yusuf Dahiru Liman, ya halarci bukukuwan Easter tare da al’ummomin Kiristoci na Gundumar Makera, inda ya bukaci su yi amfani da lokacin wajen tabbatar sa saƙon bangaskiya, yabo, da sadaukarwa da ke tattare da bikin.

A jawabin da ya gabatar, Hon. Liman ya jaddada muhimmancin bikin Easter a matsayin lokaci na sabunta dogaro da Allah. Ya kuma bukaci mabiya addinin Kirista da su rungumi koyarwar hakuri, kauna, da kuma fifita bukatun wasu akan nasu.

Kakakin ya kuma yi kira ga daukacin jama’ar Jihar Kaduna da su ci gaba da bunkasa zaman lafiya da juna ba tare da la’akari da bambancin addini, kabila ko ra’ayin siyasa ba, yana mai cewa hadin kai shi ne ginshikin ci gaban jihar da kasa baki daya. Ya jaddada bukatar gudanar da addu’o’i don dorewar zaman lafiya da inganta sha’anin tsaro.

A kokarinsa wajen inganta kiwon lafiya, Hon. Yusuf Dahiru Liman ya dauki nauyin mutane 200 da suka hada da tsofaffi da mabukata daga Kakuri-Gwari da unguwar Television domin shiga tsarin inshorar lafiya na KACHMA wanda ke ba da damar samun kulawar lafiya mai araha.

Baya ga hakan, Kakakin ya bayar da guraben karatu ga dalibai 200 daga wadannan al’ummomi domin tallafa musu a harkar ilimi da gina al’umma mai wayewa.

Bikin na Easter ya samu halartar shugabannin addini da sarakuna, shugabannin matasa da mata, da sauran manyan masu ruwa da tsaki na al’umma.

A nasa jawabin, Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na Jihar Kaduna, Mr. James Kanyip ya yabawa nasarorin da aka samu wajen karfafa tsaro da inganta zaman tare a jihar. Ya bayyana cewa gwamnati na amfani da hanyoyin sasantawa da tattaunawa wajen magance matsalolin tsaro, tare da kira ga jama’a da su kasance masu lura da kuma sanar da hukumomi duk wani abin da ba su amince da shi ba.

Shugabannin al’umma su ma sun yi amfani da damar wajen yabawa Kakakin bisa kokarinsa na kawo ci gaba. Mista Monday Kazah daga Kakuri-Gwari da Mista Ishaya Amfani daga unguwar Television sun jinjinawa Hon. Liman saboda shirye-shiryensa na tallafawa jama’a ta hanyar bayar da guraben karatu, koyar da sana’o’i, da samar da ayyukan yi. Sun kuma tabbatar masa da goyon baya da addu’o’i domin samar da dokokin da za su bunkasa rayuwar jama’a.

Shamsuddeen Mannir Atiku

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Majalisar Neja Ya Mika Sakon Easter Ga Al’ummar Kirista.
  • Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Ya Yi Bikin Easter Tare da Al’ummomin Kiristoci
  • Bukatar Kawo Karshen Mamayar Da Kamaru Ke Yi Wa Yankunan Nijeriya
  • Manchester Ta Kai Zagayen Semi Final A Europa Bayan Doke Lyon
  • UEFA: Wasan Arsenal Da Real Madrid Ya Haddasa Rikici A Tsakanin Magoya Bayan Kungiyoyin A Kano
  • Kasar Pakistan Ta Kara Jaddada Dokar Rashin Amincewa Da HKI A Matsayi Kasa
  • Majalisar Dokokin Zamfara Ta Dawo da Dan Majalisa Basko da Aka Dakatar
  • Majalisa ta gayyaci Kantoman Ribas, Ibok-Ete Ibas
  • Ina Da Ƙwarewar Da Zan Iya Zama Shugaban Ƙasar Nijeriya – Makinde