Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Zargin Takurawa Mataimakin Shugaban Kasa Shettima
Published: 19th, April 2025 GMT
Fadar shugaban kasa ta musanta rahotannin da ke nuni da cewa an hana mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, GCON shiga fadar shugaban kasa, inda ta bayyana ikirarin a matsayin shirme, kage da kuma karya gaba daya.
Wata sanarwa da babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan harkokin yada labarai da sadarwa na ofishin mataimakin shugaban kasa Stanley Nkwocha ya sanyawa hannu, ta ce rahoton da wasu shafukan da ba su da tushe suka yada shi, na cikin jerin labaran karya da aka kitsa domin haifar da rashin jituwa tsakanin shugaban kasa da mataimakinsa.
Sanarwar ta kara da cewa, “Wannan wani yunkuri ne mai rauni na cin mutuncin mutum da ofishin Mai Girma, Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima.
Nkwocha ya ce labarin da ake cewa sojoji dauke da makamai sun hana mataimakin shugaban kasa shiga fadar Shugaban kasa wato Villa ba wai kawai an yi ne ba haka kawai, a’a har ma ya nuna rashin fahimtar ayyukan gwamnati.
Sanarwar ta ce, wannan shi ne mafi girman furuci na fatar baka, kuma hakan yana nuni da cewa masu yin wannan tatsuniyoyi sun gaji da zargi da kuma hasashe, in ji sanarwar.
Wannan dai ba shi ne karon farko da fadar shugaban kasar ke yin watsi da irin wadannan rahotannin ba. Kwanaki kadan kafin hakan, ta karyata labaran karya da ke yawo a shafukan yakin neman zabe dauke da hoton shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu. Fadar shugaban kasar ta yi imanin cewa irin wannan karyar wani yunkuri ne na kawo cikas ga hadin kai da amincin shugabancin kasar.
Mataimakin shugaban kasar ya ci gaba da maida hankali kan ayyukan sa da kuma marawa shugaban kasar baya wajen cimma muradun ‘yan Najeriya. Sanarwar ta kara da cewa, ba shi da wani abin da zai raba hankali.
Nkwocha ya yabawa ‘yan Najeriya da ke ci gaba da nuna goyon bayansu ga gwamnatin Tinubu-Shettima, ya kuma bukaci kafafen yada labarai da su nemi bayanai daga majiyoyi masu inganci tare da yin taka-tsan-tsan wajen bayar da rahotanni masu ban sha’awa.
Sanarwar ta kara da cewa, “alkwarin da ke tsakanin wannan gwamnati da ‘yan Najeriya ya yiwu ne ta hanyar halaltaccen tsarin mulki.
Bello Wakili
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: shugaban kasar Sanarwar ta
এছাড়াও পড়ুন:
Shin Mataimakin Gwamnan Bauchi ya ‘mari’ Ministan Tinubu?
Rahotanni na cewa Mataimakin Gwamnan Bauchi, Auwal Mohammed Jatau, ya zabga wa Ministan Harkokin Waje, Yusuf Maitama Tuggar, mari saboda kalaman suka da ya yi kan gwamnatin jihar.
Wasu rahotanni na cewa Ministan ya yi wasu kalamai na caccaka ga Gwamna Bala Mohammed, lamarin da ya fusata mataimakinsa ya ɗauke Ministan da mari.
An shiga ruɗani kan satar al’aurar maza a ƙasar Chadi JAMB ta sauya ranar soma jarrabawar banaBayanai sun ce lamarin ya faru ne a cikin motar da ke dakon wasu manyan jami’an gwamnati, ciki har da Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, yayin da suke kan hanyar zuwa naɗin sarauta da kuma ɗaurin auren ’yar tsohon gwamnan jihar, Muhammad Abdullahi Abubakar SAN.
Aminiya ta ruwaito cewa, a Juma’ar da ta gabata ce manyan jami’an gwamnati suka halarci ɗaurin auren Khadija Muhammad, da kuma naɗin sarautar Makama Babba I da aka gudanar a Fadar Sarkin Bauchi.
Sai dai cikin wata sanarwar mayar da martani kakkausa kan lamarin, kakakin mataimakin gwamnan, Muslim Lawal, ya musanta labarin, yana mai nanata cewa ubangidansa mutum ne mai mutunci da kamala da ba zai taɓa tsoma kansa cikin irin wannan hauragiya ba.
Amma wani da abin ya faru kan idonsa kuma ya buƙaci a sakaya sunansa, ya shaida wa Aminiya cewa, Mataimakin Gwamnan ya fusata ne bayan Ministan Harkokin Wajen ya riƙa jifar Gwamna Bala Mohammed da kalamai marasa daɗi. Majiyar ta ce wannan ce ta sanya rikicin ya hautsine a cikin motar da ke dakon manyan jami’an gwamnatin zuwa Fadar Masarautar Bauchi. Aminiya ta yi ƙoƙarin jin ta bakin Minista Yusuf Tuggar ya ci tura har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton.
Sai dai ɗan gwamnan jihar, Shamsuddeen Bala Mohammed na daga cikin waɗanda suka yi farin ciki da faruwar lamarin wanda ya riƙa tashe a dandalin sada zumunta na X.
Cikin wata wallafa mai tashe da ɗan gwamnan ya ƙara yaɗawa, mai ɗauke da saƙon cewa, “Mataimakin Gwamna na farko da ya mari Minista a Bauchi. Mista Taka ka sha mari….” da sauran saƙonni makamancin wannan da suke tashe.
Ana iya tuna cewa, wannan tsamin dangantaka ya samo asali ne tun bayan da Gwamna Bala Mohammed ya riƙa sukar Shugaba Bola Tinubu kan rashin shugabanci nagari.
A cewar gwamnan, manufofin da gwamnatin Tinubu ta ƙaƙaba sun jefa al’ummar ƙasar nan cikin ƙangin talauci da tsadar rayuwa.
Sai dai a martanin da Ministan ya mayar, ya ce gwamnan na fakewa da manufofin Tinubu domin ɓoye gazawarsa da zummar samun karɓuwa wajen neman kujerar shugabancin Nijeriya a Zaɓen 2027.
Wannan dai na zuwa ne a yayin da ake zargin cewa shi kansa Ministan na fafutikar zama Gwamnan Bauchi a 2027.