Babu wanda ya hana Shettima shiga Aso Rock ba— Fadar Shugaban Ƙasa
Published: 19th, April 2025 GMT
Fadar Shugaban Ƙasa ta ƙaryata labarin da karaɗe kafofin sada zumunta cewa sojoji sun hana mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima shiga Fadar Shugaban Ƙasa.
Labarin da ya tayar da ƙura cewa sojojin sun tare ƙofar shiga fadar shugaban ƙasa da cewa umarni ne daga sama ya koma gidansa da ke makwabtaka da fadar shugaban kasa, zuwa lokacin da Shugaba Tinubu ya dawo daga ziyarar aiki da ya kai ƙasar Faransa.
Wata sanarwa da Stanley Nkwocha, hadimin shugaban ƙasa kan yada labarai, ya fitar, ta ce, babu kashin gaskiya a labarin.
Sanarwar ta kara da cewa hasali ma, masu yaɗa labarin karya sun ƙirƙirar shi ne da nufin haddasa saɓani tsakanin shugaban ƙasa Bola Tinubu da mataimakin nasa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Shugaban Ƙasa
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kasar Iran Ya Ce: Iran Da Saudiyya Za Su Iya Magance Yawancin Matsalolin Yankin Gabas Ta Tsakiya
Shugaban kasar Iran ya bayyana cewa: Iran da Saudiyya za su iya magance yawancin matsalolin yankin Gabas ta tsakiya
Shugaban kasar Iran Mas’ud Pezeshkian ya jaddada cewa: Iran da Saudiyya za su iya magance yawancin matsalolin yankin Gabas ta Tsakiya ta hanyar dogaro da karfinsu a hade ba tare da bukatar shiga tsakani daga kasashen waje ba.
Shugaban kasar Iran Mas’ud Pezeshkian ya tarbi ministan tsaron kasar Saudiyya Khalid bin Salman a yammacin jiya Alhamis, wanda ke ziyarar aiki a birnin Tehran fadar mulkin Jamhuriyar Musulunci ta Iran dauke da wata babbar tawagarsa.
Shugaban na Iran ya jaddada cewa Iran ta kuduri aniyar karfafa alakar ‘yan uwantaka a tsakanin kasashen musulmi.
Pezeshkian ta kara da cewa: Saboda wata wasiyya ta hadin gwiwa, shugabannin kasashen musulmi za su iya ba da misali mai kyau na zaman tare da samun bunkasar wadata.
Shugaban na Iran ya ci gaba da cewa: Iran a shirye take ta fadada alakar ta da Saudiyya ta kowane fanni.