A wani hari da jirgin sama maras matuki da dakarun kai daukin gaggawa su ka kai akan sansanin ‘yan hijira a Jahar ” Nahrun-Nil” a Arewacin Sudan sun kashe mutane da dama da kuma jikkata wasu, haka nan kuma sun yi sanadiyyar yanke wutar lantarki a yankin.

Kafar watsa labaru ta “al-muhakkak” ta ce; Dakarun kai daukin gaggawar sun kai hari da jirgin sama maras matuki akan sansanin ‘yan hijira da ya yi sanadiyyar mutuwar da dama daga cikinsu da kuma yanke wutar lantarki a garin Atbarah, a jihar “Nahrun-Nil” ta arewa.

Hukumar dake samar da wutar lantarki ta Sudan ta tabbatar da yankewar samar da wuta a wannan yankin saboda harin da mayakan na rundunar daukin gaggawa su ka kai.

Kamfanin samar da wutar lantarki na Sudan ya tabbatar da cewa, ‘yan kwana-kwana suna matukar kokarinsu domin kashe gobarar da ta tashi.

Kwamitin tsaro a jihar ta “Nahrul-Nail” ya bayyana wannan irin harin da cewa; Yankan baya ne, kuma ana kai shi ne akan fararen hula da kuma muhimman cibiyoyin dake cikin Jahar.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: wutar lantarki

এছাড়াও পড়ুন:

Abu Ubaidah: Mun Harbo Sojojin Mamaya 4 Daga Nesa A Beit-Hanun

Mai Magana da yawun dakarun ‘Kassam” Abu Ubaidah ya sanar da cewa; sun harbo sojojin mamaya 4 ta hanyar wani kwanton bauna da su ka yi musu a Beit-Hanun.

Kakakin dakarun na ” Kassam” ya  kuma ce; Har yanzu suna ci gaba da kwamawa da ‘yan mamaya da kuma yi musu kwanton bauna a wurare mabanbanta.”

Abu Ubadah ya kuma jaddada cewa; ‘yan gwgawarmaya su ne ke zabin lokacin da wurin da za su kai wa abokan gaba hari, kuma jaruntarsu tana bayyana daga garin Beit Hanun zuwa Rafah, da hakan yake a a matsayin abin alfahari ta fuskar soja.

A ranar Alhamis din da ta gabata, ‘yan gwgawarmayar sun harbo sojojin HKI 4 daga cikinsu har da masu manyan mukamai, tare da halaka su da kuma jikkata wasu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƴan Ta’adda Sun Kashe Maharba 10 A Adamawa
  • Karon Farko Sin Ta Fi Samar Da Wutar Lantarki Ta Aiki Da Makamashin Nukiliya A Duniya
  • An kashe sojoji 12 a barikin Nijar
  • ‘Yan Gudun Hijiran Sudan Sun Yi Kira Ga Kungiyoyin Kasa Da Kasa Da Su Ceto Yara Da Tsofaffi Daga Mummunan Kangi A Sudan
  • Abu Ubaidah: Mun Harbo Sojojin Mamaya 4 Daga Nesa A Beit-Hanun
  • A Karon Farko A Tarihi Adadin Lantarki Da Sin Ke Iya Samarwa Ta Karfin Iska Da Hasken Rana Ya Zarce Wanda Ake Iya Samarwa Ta Amfani Da Dumi
  • An kashe Shugaban coci da wata mace a Benuwe
  • Masana’antun Nijeriya Sun Kashe Naira Tiriliyan 1.11 Wajen Samun Wutar Lantarki A 2024 – Rahoto
  • Rashin Wutar Lantarki: Jihohin Kano, Katsina Da Jigawa Na Samun Wutar Awa 2 Ne Kacal A Kullum