Iran tana gudanar da bukukuwan zagayowar nasarar juyin juya halin Musulunci yau tsawon shekaru 46 tare da samun nasarori da kalubale

A yau Litinin ne, al’ummar Iran suke gudanar da bukukuwan tunawa da cika shekaru 46 da samun nasarar juyin juya halin Musulunci a kasar, wanda marigayi Imam Ruhollah Khomeini (Yardan Allah ta tabbata a gare shi) ya jagoranta, a cikin wadannan shekaru da dama, juyin juya halin Musulunci ya fuskanci makirce-makirce masu yawa da cikas, kuma ya samu gagarumar nasara, mafi muhimmanci daga cikinsu shi ne hambarar da gwamnatin sarki Shah da kasashen yammacin duniya suke goya masa baya, kamar yadda Iran bayan samun nasarar juyin juya halin Musulunci ta yi nasarar kafa gwamnati da samar da ginshikanta da samun gagarumar nasarori da ci gaba a dukkanin fannonin kimiyya da fasaha, kuma Iran ta zama daya daga cikin kasashen da suka ci gaba a duniya.

A shekara ta 1979 ne duniya ta shaida wani lamari na juyin juya hali na duniya wanda ya sauya fasalin duniya tare da bai wa Imam Ayatullah Ruhollah Khomeini (amincin Allah ya tabbata a gare shi) nasarar kifar da gwamnatin kama karya mafi zalunci mai karfin alaka ta kud da kud da kasashen yammacin Turai ta Sarki Shah Mohammad Reza Pahlavi da ya dauki matakin gudu daga Iran zuwa abokansa musamman Amurka sannan ya yi gudun hijira zuwa kasar Masar bayan da ya fuskancin juya baya ga iyayen gijinsa na yammaci Turai.

Juyin juya halin Musulunci ya samar da sabon daidaito ta hanyar kafa ma’auni na kasa da kasa tare da kafa kasa mai cin gashin kanta da ta ‘yantar da kanta daga wadanda suke juya akalar duniya a wancan lokacin wato Amurka da Tarayyar Soviet.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: nasarar juyin juya halin Musulunci juyin juya halin Musulunci ya

এছাড়াও পড়ুন:

Za’a Gudanar Taron Tattaunawa Tsakanin Rasha Ta Amurka A Karo Na Biyu 2 A Birnin Rayad na Kasar Saudiya

A gobe Litinin 24 ga watan Maris ne tawagogin masu tattaunawa na kasashen Amurka da Rasha zasu hadu a birnin Rayida na kasar Saudiya don ci gaba da tattaunawan da suka fara a yan makonnin da suka gabata dangane da yakin da ke faruwa a Ukraine, shekaru fiye da 3 da suka gabata, da kuma dangantaka a tsakanin kasashen biyu.

Kamfanin dillancin labaran Sputnik na kasar Rasha ya nakalto Yury Ushakov mai bawa shugaba Putin shawara kan al-amurin siyasa yana fadar haka. Ya kuma kara da cewa Sanata Georgy Karasin ne zai jagoranci tawagar masu tattaunawa ta kasar Rasha sannan ta kasar Amurka an rika an samar da tawagar, wasu zata hadu da na Rasga a gobe litin a birnin Riyad.

Kafin haka dai shugaban kasar Rasha Vladimir Putin sun tattauna da tokwaransa na kasar Amurka Donal Trump kan al-amura da dama wadanda suka shafi yakin a Ukraine da tsagaita budewa juna wuta na wata guda da kuma wasu al-amura.

Karsin daga karshe ya ce yana fatan tattaunawan zata yi armashi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kiyaye Ci Gaba Mai Dorewa A Huldar Sin Da Amurka Ya Dace Da Moriyar Sasssan Biyu
  • ‘Yansanda Sun Cafke Mutum 2 Kan Zargin Kashe Ɗan Achaɓa Da Sace Babur Ɗinsa A Bauchi 
  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Karfafa Gwiwar Kamfanonin Kasashen Duniya Da Su Fadada Zuba Jari A Sin 
  • Wajibcin Gina Al’ummar Duniya Mai Kyakkyawar Makomar Bai Daya
  • Iran ta yi gargadin cewa keta hurumin Lebanon da Isra’ila ke yi barazana ne ga zaman lafiyar duniya
  • Ana ci gaba da gudanar da zanga-zangar goyon bayan Falastinu a kasashen duniya
  • Za’a Gudanar Taron Tattaunawa Tsakanin Rasha Ta Amurka A Karo Na Biyu 2 A Birnin Rayad na Kasar Saudiya
  • Moscow : Dole ne Rasha da China su shiga tattaunawar nukiliya da Iran
  • Karin Sinawa Suna Son Kashe Kudi
  • Falasdinawa 80,000 ne suka halarci sallar Juma’a a mako na uku na Ramadan a masallacin Al-Aqsa