Girmama Hukuncin Kotu Muhimmin Jigo Ga Dimokuradiyya – Farfesa Fagge
Published: 22nd, February 2025 GMT
An shawarci shugabanni da aka zaba da su girmama hukuncin kotu domin tabbatar da dimokuradiyya a ƙasar.
Wani malami a Jami’ar Bayero ta Kano, Farfesa Kamilu Fagge, ya bayar da wannan shawara a Kaduna, yana nuna damuwarsa kan zargin karya dokokin kotu a harkokin siyasa.
Ya bayyana damuwarsa kan matakin da Gwamna Ademola Adeleke na Jihar Osun ya dauka na gudanar da zaɓen kananan hukumomi duk da umarnin kotu da ke hana hakan.
Farfesa Fagge ya gargaɗi shugabanni da aka zaɓa cewa rashin mutunta hukuncin kotu, duk da rantsuwar da suka yi na kare kundin tsarin mulkin ƙasa da bin doka, na iya zama barazana ga dimokuradiyya.
SULEIMAN KAURA
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Dimokuradiyya Farfesa Fagge
এছাড়াও পড়ুন:
Girmama Hukuncin Kotu Muhimmin Jigo Ga Dimokuradiyya – Farfesa Fagge
An shawarci shugabanni da aka zaba da su girmama hukuncin kotu domin tabbatar da dimokuradiyya a ƙasar.
Wani malami a Jami’ar Bayero ta Kano, Farfesa Kamilu Fagge, ya bayar da wannan shawara a Kaduna, yana nuna damuwarsa kan zargin karya dokokin kotu a harkokin siyasa.
Ya bayyana damuwarsa kan matakin da Gwamna Ademola Adeleke na Jihar Osun ya dauka na gudanar da zaɓen kananan hukumomi duk da umarnin kotu da ke hana hakan.
Farfesa Fagge ya gargaɗi shugabanni da aka zaɓa cewa rashin mutunta hukuncin kotu, duk da rantsuwar da suka yi na kare kundin tsarin mulkin ƙasa da bin doka, na iya zama barazana ga dimokuradiyya.
SULEIMAN KAURA