Aminiya:
2025-04-14@18:00:54 GMT

Farashin fetur na iya tashi yayin da Dangote ya daina sayar da mai a Naira

Published: 20th, March 2025 GMT

’Yan Najeriya na iya fuskantar ƙarin farashin man fetur bayan da Matatar Man Dangote ta bayyana cewa ta daina sayar wa ’yan kasuwa man fetur a kuɗin Naira.

Matatar, wacce ke siyan ɗanyen mai da Naira bisa yarjejeniyar gwamnati, yanzu ta koma sayan ɗanyen mai da dalar Amurka.

Ƙungiyoyin ƙwadago sun buƙaci Tinubu ya mayar da Fubara kan kujerarsa Tinubu ya rantsar da Ibas a matsayin mai kula da Ribas

An ƙirƙiro yarjejeniyar siyan ɗanyen mai da Naira ne domin rage tsadar mai.

Bisa ga wannan yarjejeniya, Kamfanin Man Fetur na Ƙasa (NNPCL), yana da alhakin samar wa Matatar Dangote gangar ɗanyen mai a kowace rana 385,000, domin ta tace ta kuma sayar da shi a farashin Naira.

Sai dai rashin cika alƙawari daga NNPCL ya sa yarjejeniyar ta gaza ɗorewa.

Wata majiya ta bayyana cewa, “NNPCL bai cika alƙawarin da ya ɗauka ba, hakan ya sa Dangote ba shi da wani zaɓi illa ya fara siyan ɗanyen mai da dala.

“Yanzu matatun cikin gida sai sun samu dala kafin su iya ci gaba da aiki.”

Matatar Dangote ta ce, “Dole ne mu daidaita kuɗin sayar da kayayyakinmu da kuɗin da muke siyan ɗanyen mai. Yarjejeniyar Naira ba ta samar da isasshen ɗanyen mai da zai iya kula da aikinmu ba.”

Masana sun yi gargaɗi

Masana tattalin arziƙi sun yi gargaɗin cewa wannan mataki zai haddasa tashin farashin man fetur yayin da aka fara samun sauƙin tashin kayan masarufi.

Dokta Thomas Ogungbangbe, wani masanin harkokin makamashi, ya ce, “Idan ana siyan ɗanyen mai da dala, dole ne a sayar da man fetur a farashin kasuwar duniya. Wannan zai ƙara matsin lamba ga dalar Amurka kuma ya jefa ’yan ƙasa cikin ƙarin wahala.”

A cewarsa wannan mataki na iya janyo ƙaruwar shigo da mai daga ƙasashen waje.

“Muna tunanin tace mai a gida zai warware matsalar tsadar mai, amma yanzu muna dawowa kan matsalar da muka nemi mu magance ta,” in ji Dokta Ogungbangbe.

Dokta Marcel Okeke, wani ƙwararre a ɓangaren harkar man fetur, ya buƙaci gwamnati da ta ɗauki matakin gaggawa.

“Dawo da tsarin sayen ɗanyen mai da Naira zai taimaka. Idan ba a yi hakan ba, farashin man fetur zai ƙara hauhawa, wanda zai haddasa tashin gwauron zabin hauhawar farashi kayayyaki da kuma matsi ga tattalin arziƙi,” in ji shi.

Sakamakon tashin farashin canjin dalar Amurka, wasu masana sun yi hasashen cewa farashin man fetur na iya haura Naira 1,000 kan kowace lita a makwanni masu zuwa, idan ba a ɗauki matakin shawo kan lamarin ba.

Ƙungiyoyin ƙwadago sun ja daga

Dangane da wannan lamari, ƙungiyoyin ƙwadago da na kare haƙƙin masu amfani da kayayyaki sun fara shirye-shiryen gudanar da zanga-zanga kan yiwuwar ƙarin farashin mai.

Ƙungiyoyin Ƙwadago na Najeriya na NLC da TUC, sun buƙaci Gwamnatin Tarayya ta ɗauki matakin gaggawa domin daƙile lamarin da ka iya jefa al’umma cikin wahala.

“Wannan mataki da Matatar Dangote ta ɗauka zai sanya rayuwa ta ƙara tsananta ga miliyoyin ‘yan Najeriya da suka riga suka faɗa cikin matsin tattalin arziƙi,” in ji Shugaban NLC, Joe Ajaero.

Farashin kuɗin sufuri na iya tashi

A halin yanzu, ana sa ran hauhawar farashin man fetur zai ƙara tsadar kuɗin sufuri, wanda hakan zai daɗa ta’azzara wahalar rayuwa.

Wasu direbobin mota sun nuna damuwarsu cewa idan farashin mai ya ƙaru, dole ne su ƙara kuɗin abun hawa, wanda zai ƙara dagula halin da talakawan Najeriya ke ciki wajen yin zirga-zirga a kullum.

Idan ba a samu mafita cikin gaggawa ba, tasirin lamarin zai iya shafar tattalin arziƙin Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dalar Amurka ɗanyen mai Naira Tashin Farashi yarjejeniya siyan ɗanyen mai da farashin man fetur

এছাড়াও পড়ুন:

Salah Ya Kafa Tarihi Yayin Da Liverpool Ke Dab Da Lashe Gasar Firimiya

A ranar Lahadi Liverpool ta sake matsa ƙaimi a gasar Firimiya bayan ta doke abokiyar karawarta West Ham United ci 2-1 a filin wasa na Anfield dake birnin Liverpool, yayin da Mohamed Salah ya kafa tarihin cin ƙwallaye a kakar wasa ta bana, sakamakon ya sa Liverpool ta samu tazarar maki 13 tsakaninta da Arsenal dake matsayi na biyu a kan teburin gasar.

Yayinda yake saura wasanni shida a kammala gasar, Liverpool na buƙatar maki 3 kacal domin lashe gasar a karo na biyu tun bayan da aka sauya wa gasar suna da fasali, West Ham na matsayi na 17 da maki 35 akan teburin gasar.

Ba Zan Ci Gaba Da Zama A Liverpool Ba -Salah Salah Ya Ƙulla Sabuwar Yarjejeniyar Shekaru 2 Da Liverpool

ESPN ta ruwaito cewa kafin fara wasan, an yi shiru na minti daya a Anfield don nuna girmamawa ga mutane 97 da iftila’i ya rutsa da su a filin wasa na Hillsborough a shekarar 1989, sai dai magoya bayan Liverpool sun ɓarke da ihu jim kaɗan bayan shirun, inda suke nuna jin daɗinsa dangane da sabon kwantiragin shekaru biyu da Salah ya sanya hannu a tsakiyar mako.

A wannan wasan ne Salah ya kafa tarihin wanda ya fi zama komai da ruwanka a wajen zura ƙwallaye a raga a wasannin gasar inda ya zura ƙwallaye 27 ya kuma taimaka aka jefa 18, ana alaƙanta Salah da komawa ƙasashen Larabawa domin cigaba da taka leda, amma kuma sabon kwantiragin da Salah ya sakawa hannu ya sa zai cigaba da zama a Anfield tsawon shekaru biyu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Salah Ya Kafa Tarihi Yayin Da Liverpool Ke Dab Da Lashe Gasar Firimiya
  • A daina cutar ’yan Najeriya ta hanyar rabon kayan tallafi
  • Inganta Rayuwar Al’umma: Amurka Da Ƙungiyar Kasuwanci Ta Nijeriya Sun Karrama Gwamna Lawal
  •  Nigeria: Wani Bom Da Ya Tashi A Maiduguri Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutane 7
  • Isra’ila ta yi barazanar fadada hare-hare Gaza yayin da ta yanke Rafah daga birnin Khan Yunis
  • Yaya ‘Yan Siyasar Amurka Ke Kasafta Harajin Ramuwar Gayya?
  • Yadda bom ya tashi da ɗan gwangwan a Legas
  • Basukan Da Nijeriya Ke Biya Sun Karu Zuwa Naira Tiriliyan 13