Aminiya:
2025-04-14@18:14:56 GMT

Farashin fetur na iya tashi bayan Dangote ya daina sayar da mai a Naira

Published: 20th, March 2025 GMT

’Yan Najeriya na iya fuskantar ƙarin farashin man fetur bayan da Matatar Man Dangote ta bayyana cewa ta daina sayar wa ’yan kasuwa man fetur a kuɗin Naira.

Matatar, wacce ke siyan ɗanyen mai da Naira bisa yarjejeniyar gwamnati, yanzu ta koma sayan ɗanyen mai da dalar Amurka.

Ƙungiyoyin ƙwadago sun buƙaci Tinubu ya mayar da Fubara kan kujerarsa Tinubu ya rantsar da Ibas a matsayin mai kula da Ribas

An ƙirƙiro yarjejeniyar siyan ɗanyen mai da Naira ne domin rage tsadar mai.

Bisa ga wannan yarjejeniya, Kamfanin Man Fetur na Ƙasa (NNPCL), yana da alhakin samar wa Matatar Dangote gangar ɗanyen mai a kowace rana 385,000, domin ta tace ta kuma sayar da shi a farashin Naira.

Sai dai rashin cika alƙawari daga NNPCL ya sa yarjejeniyar ta gaza ɗorewa.

Wata majiya ta bayyana cewa, “NNPCL bai cika alƙawarin da ya ɗauka ba, hakan ya sa Dangote ba shi da wani zaɓi illa ya fara siyan ɗanyen mai da dala.

“Yanzu matatun cikin gida sai sun samu dala kafin su iya ci gaba da aiki.”

Matatar Dangote ta ce, “Dole ne mu daidaita kuɗin sayar da kayayyakinmu da kuɗin da muke siyan ɗanyen mai. Yarjejeniyar Naira ba ta samar da isasshen ɗanyen mai da zai iya kula da aikinmu ba.”

Masana sun yi gargaɗi

Masana tattalin arziƙi sun yi gargaɗin cewa wannan mataki zai haddasa tashin farashin man fetur yayin da aka fara samun sauƙin tashin kayan masarufi.

Dokta Thomas Ogungbangbe, wani masanin harkokin makamashi, ya ce, “Idan ana siyan ɗanyen mai da dala, dole ne a sayar da man fetur a farashin kasuwar duniya. Wannan zai ƙara matsin lamba ga dalar Amurka kuma ya jefa ’yan ƙasa cikin ƙarin wahala.”

A cewarsa wannan mataki na iya janyo ƙaruwar shigo da mai daga ƙasashen waje.

“Muna tunanin tace mai a gida zai warware matsalar tsadar mai, amma yanzu muna dawowa kan matsalar da muka nemi mu magance ta,” in ji Dokta Ogungbangbe.

Dokta Marcel Okeke, wani ƙwararre a ɓangaren harkar man fetur, ya buƙaci gwamnati da ta ɗauki matakin gaggawa.

“Dawo da tsarin sayen ɗanyen mai da Naira zai taimaka. Idan ba a yi hakan ba, farashin man fetur zai ƙara hauhawa, wanda zai haddasa tashin gwauron zabin hauhawar farashi kayayyaki da kuma matsi ga tattalin arziƙi,” in ji shi.

Sakamakon tashin farashin canjin dalar Amurka, wasu masana sun yi hasashen cewa farashin man fetur na iya haura Naira 1,000 kan kowace lita a makwanni masu zuwa, idan ba a ɗauki matakin shawo kan lamarin ba.

Ƙungiyoyin ƙwadago sun ja daga

Dangane da wannan lamari, ƙungiyoyin ƙwadago da na kare haƙƙin masu amfani da kayayyaki sun fara shirye-shiryen gudanar da zanga-zanga kan yiwuwar ƙarin farashin mai.

Ƙungiyoyin Ƙwadago na Najeriya na NLC da TUC, sun buƙaci Gwamnatin Tarayya ta ɗauki matakin gaggawa domin daƙile lamarin da ka iya jefa al’umma cikin wahala.

“Wannan mataki da Matatar Dangote ta ɗauka zai sanya rayuwa ta ƙara tsananta ga miliyoyin ‘yan Najeriya da suka riga suka faɗa cikin matsin tattalin arziƙi,” in ji Shugaban NLC, Joe Ajaero.

Farashin kuɗin sufuri na iya tashi

A halin yanzu, ana sa ran hauhawar farashin man fetur zai ƙara tsadar kuɗin sufuri, wanda hakan zai daɗa ta’azzara wahalar rayuwa.

Wasu direbobin mota sun nuna damuwarsu cewa idan farashin mai ya ƙaru, dole ne su ƙara kuɗin abun hawa, wanda zai ƙara dagula halin da talakawan Najeriya ke ciki wajen yin zirga-zirga a kullum.

Idan ba a samu mafita cikin gaggawa ba, tasirin lamarin zai iya shafar tattalin arziƙin Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dalar Amurka ɗanyen mai Naira Tashin Farashi yarjejeniya siyan ɗanyen mai da farashin man fetur

এছাড়াও পড়ুন:

Jama’ar Gabon sun kada kuri’a a zaben shugaban kasa, na farko bayan mulkin zuri’ar Bongo

A Gabon, yau Asabar ne Jama’ar kasar suka kada kuri’a  domin zaben shugaban kasar, a karon farko bayan kifar da iyalan gidan Bongo daga mulkin kasar.

Janar Brice Oligui Nguema, wanda ya kifar da mulkin Ali Bongo na daga cikin ‘yan takarar dake fafatawa a zaben daga cikin ‘yan takara guda takwas.

Sauran yan takarar sun hada da Firaministan kasar Alain Claude Bilie-by-Nze, wanda ya rike wannan mukami a lokacin mulkin Bongo, da kuma wasu manyan kusoshin tsohuwar jam’iyya mai mulki ta PDG.

Kimanin mutum miliyan daya ne aka tantance su kada kuri’a a zaben, daga cikin jimilar miliyan biyu da rabi na kasar.

A karfe 06:00 na yamma agogon kasar wato 05:00 na yamma agogon GMT, na yau aka tsara rufe rumfunan zaben.

Za a iya fara sanar da sakamakon zaben daga gobe Lahadi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasashen Turai na E3 sun goyi bayan tattaunawar Iran da Amurka
  • A daina cutar ’yan Najeriya ta hanyar rabon kayan tallafi
  • Inganta Rayuwar Al’umma: Amurka Da Ƙungiyar Kasuwanci Ta Nijeriya Sun Karrama Gwamna Lawal
  •  Nigeria: Wani Bom Da Ya Tashi A Maiduguri Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutane 7
  • Sama da mutane 1,560 ne sukayi shahada tun bayan da Isra’ila ta koma kai farmaki Gaza
  • Jama’ar Gabon sun kada kuri’a a zaben shugaban kasa, na farko bayan mulkin zuri’ar Bongo
  • Yaya ‘Yan Siyasar Amurka Ke Kasafta Harajin Ramuwar Gayya?
  • Yadda bom ya tashi da ɗan gwangwan a Legas
  • Mahaifi ya yi wa ’yarsa ciki a Bauchi
  • Basukan Da Nijeriya Ke Biya Sun Karu Zuwa Naira Tiriliyan 13