2025-03-29@03:56:10 GMT
إجمالي نتائج البحث: 973

«a Allah Ya ba»:

(اخبار جدید در صفحه یک)
    Kamfanin kula da sufurin layin dogo na kasar Sin, ya ce jarin manyan kadarori da kasar ta zuba a bangaren layin dogo ya kai yuan biliyan 43.9, kwatankwacin dala biliyan 6.12, a watan Janairun bana. A cewar kamfanin, adadin ya karu da kaso 3.7 bisa dari idan aka kwatantan da makamancin lokacin a bara. A wannan lokaci, an gudanar da manyan ayyuka, ciki har inganta layin dogo mai saurin tafiya tsakanin biranen Chengdu da Chongqing. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)
    Kungiyar kula da harkokin jigilar kayayyaki da sayen kayayyaki ta kasar Sin ta samar da adadin sana’o’in adana kayayyaki na Sin a watan Janairun da ya gabata cewa, wanda ya nuna cewa, yawan bukatun ajiye kaya a Sin ya bunkasa cikin sauri duba da karuwar bukatun sayayya a lokacin bikin sabuwar shekara, kuma sana’o’in adana kayayyaki na ci gaba da samun bunkasuwa. Adadin sana’o’in adana kayayyaki na Sin ya kai kashi 52.5%, a watan Janairun da ya wuce, wanda ya karu da kashi 1.9% bisa na watan Disamban da ya gabata, adadin da ya kai koli a cikin watanni 10 da suka gabata. Sakamakon manufofin tabbatar da tattalin arziki da ingiza bunkasuwa, da ma yadda aka koma aiki bayan hutun...
    ’Yan bindiga sun kashe wani fasto, Rabaran Bala Galadima yayin harin da suka kai garin Lubo da ke Ƙaramar Hukumar Yamaltu Deba a Jihar Gombe. Aminiya ta ruwaito cewa, ’yan bindigar sun kuma yi fashin kuɗi har Naira dubu 300 a yayin harin da suka kai cikin dare wayewar gari Lahadi. Wani mazaunin garin ya bayyana cewa maharan, waɗanda sun kai takwas, sun kai farmakin ne da misalin karfe 1 zuwa 3 na dare, inda suka firgita jama’a da harbe-harbe kafin su kutsa cikin gidan wani mutum mai suna Musa Puma. Majiyar ta ce maharan sun rutsa matar gidan da bindiga inda suka karbi kuɗi naira dubu dari 300 tare da yin garkuwa da ɗaya daga cikin ’ya’yansu da kuma...
    Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya mika sakon ta’aziyya ga takwaransa na Namibia, Nangolo Mbumba, bisa rasuwar shugaban kasar na farko, Sam Nujoma. A madadin gwamnati da al’ummar Sinawa, shugaba Xi Jinping ya bayyana jimami tare da yin ta’aziyya ga iyalan Nujoma da ma gwamnati da al’ummar kasar Nambia. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)
    Babban hafsan hafsishin sojojin Iran Manjo Janar Muhammad Bakri ya bayyana cewa sojojin Iran a shirye suke fiye da ko wani lokaci don kare JMI daga makiyanta. Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ya bayyana cewa Bakiri ya bayyana haka ne a lokacinda yake tattaki na bukukuwan cika shekaru 46 da nasarar juyin juya halin musulunci a nan kasar Iran a nan birnin Tehran a safiyar yau Litinin. Ya ce: Halin da sojojin JMI suke ciki yafi na ko wani lokacin kyau, don haka a shirye suke su gudanar da ayyukansu a duk lokacinda bukatar haka ta taso. Dangane da tattaunawa tsakanin Iran da Amurka kuma, Janar Bakiri ya bayyana cewa, jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul...
    Yanzu-Yanzu: Ƴan Bindiga Sun Sace Iyali 3 A Filato
    Khalilul Hay, shugaban kungiyar Hamas a Gaza, wanda ya halarci gangamin bikin cika shekaru 46 da nasarar juyin juya halin musulunci a kasar Iran, ya bayyana cewa yakin Tufanul Aksa ya na matsayin mataki na farko ne na kwatar kasar Falasdinu daga hannun wadanda suka mamayeta. Ya kuma kara da cewa JMI ta taimakawa kungiyar sa kuma tana ci gaba da taimaka mata, har’ila yau yana da yakini Iran zata ci gaba da taimakawa kungiyar Hamas har zuwa nasara. Tashar talabijin ta Almayadeen ta kasar Lebanon ta watsa jawabin Al-Hay kai tsaye daga birnin Tehran a safiyar yau litinin, inda ya yi Jawabi a dandalin Azadi dake tsakiyar birnin Tehran. Yace, farmakin ‘waadu Sadik na daya da na biyu duk...
    Sam Nujoma, dan gwagwarmaya neman yencin kasar Namibiya karkashin gwamnatin wariyar launin fata ta Afrika ta kudu, ya rasu a jiya Lahadi kamar yanda gwamnatin kasar ta Namibi a ta bada sanarwa. Shugaban kasar ta Namibia mai ci, Nangola Mbumba ya ce tsohon shugaban kasar ya na jinya a as wani asbiti a babban birnin kasar  Windhoek  na kimani makonni 3 amma rai yayi halinsa a daren Asabar da ta gabata ya na dan shekara 95. Shafin yanar gizo na Labarai ‘Africanews’ ya bayyana cewa kasar Namibia ta sami yencin kanta ne daga hannun gwamnatin wariya ta Afirka ta kudu a shekara 1990. Sannan Nujoma ya zama shugaban kasar na farko na tsawon shekaru 15. Sannan aka zabi shugaba mai...
    Duk da cewa, cikakken bayani kan wannan ziyara bai fito fili ba har zuwa lokacin hada wannan rahoto, LEADERSHIP ta tattaro cewa, ganawar ba za ta rasa nasaba da burin Atiku na tsayawa takarar shugabancin Nijeriya ba a zaben 2027 mai zuwa.   Har ya zuwa lokacin hada wannan rahoton, manyan ‘yan siyasar ba su kammala ganawar ba.
    Sanarwar ta kuma bayyana cewa wannan ziyara ta gwamnan, za ta ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin gwamnatin jihar Zamfara da Bankin na Duniya.   Cikin jawabin sa a wurin, Gwamna Dauda Lawal ya jaddada ƙudirin gwamnatin sa na ƙarfafa dangantakar ta Bankin Duniyar.   “Ina so in fara da nuna godiya ta ga Bankin Duniya game da tallafin da ya ke bayarwa a jihar mu. Mun jingina da manufofin Bankin Duniya wajen inganta rayuwar al’ummar mu kawar da talauci da ci gaban ayyukan inganta rayuwa.   “Muna sane da ƙalubalen da muka fuskanta, wanda ya shafi gudanar da ayyukan ci gaba a jihar Zamfara, musamman waɗanda suka samu matsala wajen aiwatarwa, sakamakon yanayin da aka shiga. Amma, lallai babu shakka muna...
    Gwamna Inuwa Yahaya, ya kuma umarci hukumomin tsaro da su bi sawun waɗanda suka aikata wannan aika-aika domin kamu su, kana ya kuma miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan mamacin da cocin ECWA, da ɗaukacin al’ummar Kirista, yana mai addu’a ga mamacin.
    Wasu ’yan daba sun gine-ginen makaranta a yankin Okpoga da ke Karamar Hukumar Okpogwu da ke Jihar. Ɓata-garin sun ƙona gine-ginen ne a Makarantar Sakandaren Central UBE da ke Ogwu-Okpoga da kuma Makarantar Ƙaramar Sakandare s ake Obossa. Wani shaida ya bayyana wa wakilinmu cewa a makon da ya gabata ne ’yan daban suka yi wannan aika-aika. Shaidan wanda bai amince a bayyana sunansa ba, ya yi zargin wata manufar siyasa ce ta sa ’yan daban suka cinna wa gine-ginen wuta. Ya bayyana damuwa kan yawaitar irin wannan aika-aika a ’yan kwanakin nan. Kokarinmu ma ji daga kakakin ’yan sanda ta Jihar Binuwai, Catherine Aneneh, bai yi nasara ba, saboda mun kira ta a waya ba ta shiga ba. ’Yan...
    An gurfanar da wasu mutum uku ’yan uwan juna kan yi wa wata matar aure da mijinta dukan kawo wuƙa a yankin Karamar Hukumar Gezawa da ke Jihar Kano. An gurfanar da su ne a gaban Babbar Kotun Musulunci ta Gazawa kan zargin yi wa matar auren karaya uku a ƙafarta da hannunta bayan sun yi mata dukan kawo wuƙa tare da ji mata raunuka. Sun kuma ƙuƙƙuje mijinta da ya yi ƙoƙarin ceton ta bayan shi ma suka lakaɗa masa duka. Ana tuhumar su laifin yin kutse da yin barazana da haɗa kai wajen aikata laifi da ji wa mutane munanan raunuka. ’Yan sanda sun ba al’ummar Sheka awa 24 su kawo sunayen ’yan daba Ɗan fashi ya yi...
    Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Kano ya ba al’ummar yankin Sheka awa 24 su kawo wa rundunar sunayen manyan ’yan daban da ke addabar yankin. Rundunar ta ba da wannan wa’adin ne bayan matsalar ’yan daba ta ya ƙi ci ta ƙi cinyewa a yankin da ke Ƙaramar Hukumar Kumbotso. A yayin wani zama na musamman da kwamishinan rundunar ta yi da al’ummar yankin ne aka ba su wannan sanarwar. Kwamishinan ’yan sandan, wanda ya samu wakilci DPO na yankin Dakata, ACP Yusha’u Mus’ud, ya ce muddin al’umma ba su taimaka da bayanan jagororin ’yan daban ba, ta ɓata-garin an kama su ba, babu yadda za a yi ɓata-garin su daina addabar yankin. Ɗan fashi ya yi wa ɗaliban jami’a uku...
    “Zaben Alhaji Ibrahim Ibn Umar El-Kanemi, a matsayin sabon Shehun Dikwa, an gudanar da shi cikin lumana da hadin kai wanda sarakunan masarautar suka taka rawar gani wajen zakulo wanda ya dace,” in ji Zulum.   Ya bukaci sarkin da ya yi ba da jagoranci daidai da irin kalubalen zamani, yana mai jaddada rawar da masarautar ke takawa wajen farfado da Borno daga shekaru masu yawa na rashin tsaro.
    ’Yan sanda a Babban Birnin Tarayya Abuja sun buƙaci al’umma su kawo musu rahoton duk wanda aka ga yana sana’ar bola-jari a cikin gari. Kwamishinan ’Yan Sanda na Abuja, Disu Olatunji, ne ya sanar da haka bayan taron Majalisar Tsaro ta Babban Birnin Tarayya wanda Minista Ezenwo Nyesom Wike ya jagoranta. Idan ba a manta ba, a ranar 13 ga watan Janairu, 2025 ne Hukumar Babban Birnin Tarayya ta haramta ayyukan ’yan bola-jari a cikin faɗin birnin. Umarnin ya taƙaita ayyukansu ga kan juji da ke ya yankunan da suke wajen birnin. A lokacin zaman ne aka dakatar da ayyukan ’yan gwangwan na tsawon makonni biyu, saboda zargin alaƙarsu da ’yan bola-jari. NAJERIYA A YAU: Shin Har Yanzu Akwai Masu...
    More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba Akan karkasa mutane gida-gida a bisa mizanin tattalin arziki, musamman a tsarin jari-hujja, inda ke da mawadata da kuma matalauta. A tsakanin al’umma kuma akwai ajin mutane masu matsakaicin samu waɗanda ake kira “Middle Class”. Akan sanya mutane a wannan aji ne galibi bisa la’akari da aiki ko sana’ar da suke yi, da kuɗin da suke samu, da matakin ilimin da suka kai, da ma matsayinsu a tsakanin al’umma. Sai dai a baya-bayan nan irin wadannan muntane sun bi sahun matalauta wajen korafi game da yadda suke dandana kudarsu saboda tsadar rayuwa. NAJERIYA A YAU: Dalilin Faɗuwar Farashin Tumatur A Kasuwa DAGA LARABA: Yadda Al’adun Aure A Ƙasar Hausa Suka Koma ‘Event Centre’...
    Iran tana gudanar da bukukuwan zagayowar nasarar juyin juya halin Musulunci yau tsawon shekaru 46 tare da samun nasarori da kalubale A yau Litinin ne, al’ummar Iran suke gudanar da bukukuwan tunawa da cika shekaru 46 da samun nasarar juyin juya halin Musulunci a kasar, wanda marigayi Imam Ruhollah Khomeini (Yardan Allah ta tabbata a gare shi) ya jagoranta, a cikin wadannan shekaru da dama, juyin juya halin Musulunci ya fuskanci makirce-makirce masu yawa da cikas, kuma ya samu gagarumar nasara, mafi muhimmanci daga cikinsu shi ne hambarar da gwamnatin sarki Shah da kasashen yammacin duniya suke goya masa baya, kamar yadda Iran bayan samun nasarar juyin juya halin Musulunci ta yi nasarar kafa gwamnati da samar da ginshikanta da...
    Siyasar tsananata matsin lamba kan Iran ta gaza cimma buri kuma hana fitar da man da Iran ke fitarwa mafarki ne da ba zai tabbata ba Ministan mai na kasar Iran Mohsen Paknejad ya bayyana matsayar matsin lamba da Amurka ke yi kan fitar da man kasar Iran a matsayin siyasa ta nuna gazawa, yana mai cewa: Hana fitar da man fetur din Jamhuriyar Musulunci ta Iran zuwa wajen kasar, mafarki ne da ba zai taba wanzuwa ba. Ministan mai na Iran Mohsen Paknejad a matsayin mayar da martani ga furucin Trump ta sake dawo da tsananta siyasar matsin lamba da nufin gurgunta harkar tattalin arzikin Iran ta hanyar hana ta fitar da man fetur, a jiya Lahadi ya bayyana...
    Kwamandan rundunar sojojin ruwa na dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran ya bayyana cewa: Za su iya rufe mashigar Hormuz, amma ba za yi hakan a yanzu ba Kwamandan rundunar sojojin ruwa na dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran Birgediya Janar Ali Reza Tangsiri ya yi bayani kan irin fitattun abubuwan da jirgin ruwan da Iran ta kera mai suna Shahid Bahman Baqiri, inda ya ce; Wannan jirgi shi ne nau’i daya tilo saboda babu wata kasa a yankin yammacin Asiya da ke da makamancinsa. Birgediya Janar Tangsiri ya bayyana a cikin shirin ”Labarin juyin juya hali” a tashar Al-Alam cewa: Bayan sanarwar da Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya fitar dangane...
    Kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran ya jaddada cewa: Kungiyar Hamas duk da iyakantaccen kayan yakinta ta kalubalanci gwamnatin ‘yan sahayoniyya Kwamandan dakarun kasa na Dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran Birgediya Janar Morteza Miryan ya jaddada cewa: Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ta kalubalanci gwamnatin mamayar ‘yan sahayoniyya da suke samun goyon bayan Amurka da kasashen Yamma duk da iyakantaccen kayan yakin da ta mallaka na kare kai. Birgediya Janar Miryan ya ce a cikin jawabinsa a wajen bikin tunawa da shahidan harin “Wal-Fajir 8” da aka gudanar a lokacin tunawa da shahidan lardin Alborz da ke yammacin birnin Tehran: A lokacin yakin da aka yi na shekara ta 1980 zuwa shekara ta 1988),...
    Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na sharhin bayan labarai, wanda zai yi magana a kan “Yadda JMI Ta Bunkasa Sana’argine-gine da da kamfanoni tare da amfani da fasahar cikin gida’ wanda ni tahir amin zan karanta. Tun bayan nasarar juyin juya halin musulunci a nan kasar Iran a shekara 1979, daya daga cikin bangarorin da aka sami gagarumin ci gaba a cikinsa shi ne, bunkasa sana’ar gine –gine da kuma samar da masana’antu, wanda ya kai ga kasar ta kai ga wadata a wannan bangaren, wani abu daga kasashen waje, sai abunda ba za’a rasaba. Har’ila yau wannan ya wadanar da mutane da dama a kasar. Kafin haka idan mun dubi...
    Wani babban jami’in Ƴansanda, ASP Shafi’u Bawa, na rundunar 61 Police Mobile Force (PMF), an tsinci gawarsa a dakinsa a garin Kontagora, Jihar Neja, a ranar Asabar, bayan da ake zargin ya kashe kansa. Majiyoyi sun tabbatar da cewa an gano gawar ASP Bawa rataye a saman silin ɗin ɗakinsa. Mahaifinsa, Malam Usman Bawa, ne ya fara gano lamarin kafin ya kai rahoto ofishin ‘yansanda na Kontagora. Matsalar ‘Yan sandan Amurka Ta Nuna Karfin Tuwo Na Kara Tsananta Abin Fashewa Ya Hallaka Mutum Guda, Ya Jikkata 6 A Neja Kakakin rundunar ‘yansandan jihar, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da afkuwar lamarin, yana mai cewa: “A ranar 8/2/2025 da misalin ƙarfe 2 na rana, an samu rahoton cewa ASP Shafi’u Bawa...
    Shugaban kasar Namibia dake kan gado Nangolo Mbumba ne ya sanar a yau Lahadi cewa, jagoran samun ‘yacin kasar Sam Nujoma ya rasu a jiya Asabar da dare, bayan da aka kwantar da shi a wani asibitin babban birnin kasar Windhoek. Sanarwar da shugaban kasar ta Namibia mai ci a yanzu, ya fitar ya bayyana mutuwar Nujoma da cewa; ginshikin da aka kafa kasar akansa ya girgiza. Sam Nujoma ya jagoranci fadan sama wa kasar ta Namibia ‘yanci daga mulkin nuna wariyar launin fata na Afirka ta kudu, a shekarar 1990, sannan kuma ya jagoranci kasar na tsawon shekaru 15. A lokacin da yake a raye, al’ummar kasar ta Namibia suna girmama shi matuka a matsayin wanda ya jagoranci fadan...
    Shugaban kasar Iran Mas’ud Fizishkiyan ya yi kira da a kafa kawancen duniya da dukkanin kasashen musulmi za su shiga ciki, domin taimakawa mutanen Gaza, da sake gina yanki, tare da cewa, kasashen musulmi kadai za su iya sake gina yankin na Gaza tare da dawo da rayuwa a cikinsa. A ganawar da ya yi da mambobin majalisar jagoranci ta kungiyar Hamas, anan Tehran ya yi jinjina ga shahidan kawancen gwagwarmaya, ya kuma yi murna akan nasarar da ‘yan gwgawarmaya su ka samu akan ‘yan sahayoniya. Shugaban kasar ta Iran ya kara da cewa; Nasarorin da mutanen na Gaza su ka samu, sun hana makiya ‘yan sahayoniya cimma manufofin da su ka shata, duk da cewa adadin shahidan da aka...
    “Da sauri jami’an ‘yansanda suka isa wurin, inda suka gano wata mata ‘yar shekara 25 mai suna Promise Eze, ‘yar Jihar Ebonyi, daure a wata karamar kujera an rufe bakinta da filasta. An same ta a sume kuma cikin damuwa. Jami’an ‘yan sanda sun dauki matakin gaggawa, inda suka kubutar da ita daga hannun wadanda aka yi garkuwa da su, sannan suka garzaya da ita asibitin gundumar Wuse, inda ta farfado,” in ji sanarwar. Adeh ta ce binciken farko da aka yi ya nuna cewa Eze ta leka otal din a safiyar ranar 30 ga watan Janairu tare da Okoro, wanda ta hadu da shi ta intanet. A cewarta, wanda ake zargin ya gabatar da kansa a matsayin ma’aikacin kamfanin...
    Wakilin Jagoran juyin juya halin Musulunci a kasar Iraki ya ce: Juyin juya halin Musulunci ya gabatar da wani sabon samfuri na hadin kan al’umma Ayatullah Mojtaba Hosseini, wakilin Jagoran juyin juya halin Musulunci a kasar Iraki ya bayyana muhimmancin hadin kan al’ummar musulmi da kuma nauyin da ya rataya a wuyan musulmi na daidaiku da na al’umma dangane da manufofin juyin juya halin Musulunci, yana mai cewa: juyin juya halin Musulunci ya gabatar da wani sabon salo na hadin kan al’ummar musulmi. A jawabin da ya gabatar na zagayowar samun nasarar juyin juya halin Musulunci a Iran da aka gudanar a tsohon gidan da Imam Khumaini (r.a) da ya zaune a birnin Najaf, Ayatullah Husaini ya jaddada muhimmancin hadin...
    Sojojin mamayar Isra’ila sun fara janyewa daga yankin Netzarim da ke tsakiyar Zirin Gaza Kafofin yada labaran haramtacciyar kasar Isra’ila sun tabbatar da cewa: Sojojin mamayar Isra’ila za su fara ficewa daga yankin Netzarim da ke tsakiyar Zirin Gaza a daren jiya. Jaridar Yedioth Ahronoth ta haramtacciyar kasar Isra’ila ta watsa rahoton cewa: Rundunar sojin mamayar Isra’ila ta ba da umarnin ficewa daga yankin Netzarim da ke tsakiyar Gaza a wani bangare na aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin kungiyar Hamas da gwamnatin mamayar Isra’ila a yankin. Jaridar ta bayyana cewa: Runduna ta 162 ta sojojin mamayar ta sake matsawa zuwa kusa da kan iyaka da kuma janyewa daga yankin Netzarim na nufin cewa, babu sojojin mamayar Isra’ila a arewacin...
    Sojojin Sudan suna kokarin canza ma’aunin yaƙin kasar bayan da suka sun tunkari birnin Khartoum fadar mulkin kasar domin yantar da shi gaba daya Babban birnin kasar Sudan, Khartoum, shi ne tushen rikicin kasar da a halin yanzu aka shafe makonni ana gwabza fada tsakanin sojoji da mayakan dakarun kai daukin gaggawa, amma fadan ya kara kamari a ‘yan kwanakin da suka gabata. Sojoji suna kara ci gaba da tunkarar babban birnin kasar bayan fitattun sojojin kasar da suka hada da sojoji da mayaka masu goyon bayan sojoji da hukumar leken asiri da dakarun tsaron Sudan da suke sansanin Haddab da ke bangaren arewa maso gabashin yankin Gabashin Nilu a arewa maso gabashin Khartoum suka doshi birnin na Khartoum da...
    Ga wasu manyan ‘yan kwallo da tauraronsu ke haskawa a duniya, wadanda asalin ‘yan Nijeriya ne, wato ko dai iyayensu baki daya ko wani daga cikin iyayen ‘yan Nijeriya ne.   Jamal Musiala (Jamus) Matashin dan wasa Jamal Musiala, wanda aka haifa a ranar 26 ga Fabrairun shekarar 2003, fitaccen dan kwallon kasar Jamus ne da kungiyar kwallon kafa ta Bayern Munich ta Jamus din kuma yana cikin matasan ‘yan kwallon da suke tashe a duniya a yanzu saboda ba za ka lissafa matasan ‘yan wasa guda biyar ba a duniya ba tare da ka saka sunansa ba. An haife shi ne a garin Stuttgart da ke Jamus, amma mahaifinsa mai suna Daniel Richard asalin can Nijeriya ne, wanda ya...
    Iran ta ce a shirye take ta tallafa wa Burkina faso a yakin da take da ta’addanci. Wannan bayyanin ya foto ne bayan wata ganawa tsakanin Firaministan Burkina Faso Rimtalba Jean Emmanuel Ouédraogo da jakadan Jamhuriyar Musulunci ta Iran a Burkina Faso, Mista Mojtaba Faghihi a Ouagadougou. Taron dai ya baiwa mutanen biyu damar sake yin nazari kan hadin gwiwar dake tsakanin kasashensu. A cikin wannan yanayi, Iran ta bayyana aniyar ta na tallafawa Burkina Faso, a kokarinta na dakile matsalar rashin tsaro. Tehran, ta bakin jakadanta, ta kuma bayyana sha’awarta kan sauran fannonin hadin gwiwa, kamar su noma, masana’antu, likitanci da al’adu. Ya ce Iran a shirye take ta ba da dukkan goyon bayan da ya dace ga Burkina...
    A yau Asabar, 8 ga wannan wata da safe, babban sakataren kwamitin tsakiya na jam’iyyar Kwaminis ta Sin kuma shugaban kasar Sin Xi Jinping ya saurari rahoton aiki na kwamitin JKS da gwamnatin lardin Jilin a birnin Changchun dake lardin Jilin. Bayan kammala sauraro, shugaba Xi ya yi jawabi inda ya jaddada cewa, ya kamata hukumomin lardin Jilin su aiwatar da shirin farfado da yankin arewa maso gabashin kasar Sin a dukkan fannoni a sabon zamani da kwamitin tsakiya na JKS ya tsara, da tabbatar da tsaron kasar a fannoni 5, da maida hankali ga aikin samun ci gaba mai inganci, da bin tsarin tunanin sabon ci gaba, da bude kofa ga kasashen waje, da yin kwaskwarima a dukkan fannoni,...
    Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya nada Umar Farouk Ibrahim a matsayin sabon Sakataren Gwamnatin Kano. Nadin na kunshe cikin wata sanarwar da Kakakin Gwamnatin Kano, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya wallafa a shafukansa na sada zumunta a yammacin ranar Asabar 08, ga Febarairun 2025. Dalilan Da Suka Sa Gwamnan Kano Sallamar SSG Da Wasu Kwamishinoni 5 Gwamnan Kano Ya Karyata Jita-jitar Rikicinsa Da Sakataren Gwamnatin Jihar Nadin Na Ibrahim zai fara aiki ne daga ranar Litinin mai zuwa 10, ga Febarairun 2025. Sanarwar nadin ta bayyana cewa an zabi, Ibrahim a matsayin sabon Sakataren Gwamnatin Jihar saboda shafe sama da shekaru talatin ya na aikin gwamnati da tarin kwarewar aiki da yake da ita a hukumomi da ma’aikatu daban-daban...
    “Ina so na fara da godiya ga Bankin Duniya kan tallafin da yake ci gaba da bai wa jiharmu. Mun daidaita manufofin ci gabanmu da manufar Bankin Duniya na kawar da talauci da inganta ci gaba mai dorewa.” “Mun kuma lura da kalubalen tsaro da a baya suka yi tasiri wajen aiwatar da ayyuka a jihar Zamfara, musamman wadanda suka kawo cikas ga cimma burin da aka sanya a gaba. Duk da haka, muna samun ci gaba yayin da ake fuskantar ƙalubalen, kuma abubuwa suna komawa daidai.” “Mun inganta matakan tsaro ta hanyar kwararan matakai da jihar ta dauka na inganta tsaro da kara daukar matakan dakile barazanar tsaro.” “Gwamnatinmu ta dukufa wajen tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi ta...
    Jihar Adamawa ta rasa shahararre kuma babban malamin addinin musilunci, Sheikh Ibrahim Abubakar Daware, ranar Juma’a, bayan fama da rashin lafiya. Sheikh Daware ya kasance malami mai karamci wanda yake koyar da darussan addini da kuma gudummawa a kasashen musulmi daban-daban da sassan jihohin Nijeriya da dama. Dauda Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Almajirai 17 Da Suka Rasu A Sakamakon Tashin Gobara A Zamfara Uwargidan Tinubu Ta Kai Wa Gwamnan Jigawa Ziyarar Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifiyarsa Da Ɗansa An gudanar da jana’izar malamin kamar yadda addinin musilunci ya tanada a gidansa da ke karamar hukumar Fufore a ranar Asabar. Sheikh Ibrahim Daware, ya rasu ya na da shekaru 71, ya bar matan aure hudu da ‘ya’ya 43 da jikoki 53.
    Jihar Adamawa ta rasa shahararre kuma babban malamin addinin musilunci, Sheikh Ibrahim Abubakar Daware, ranar Juma’a, bayan fama da rashin lafiya. Sheikh Daware ya kasance malami mai karamci wanda yake koyar da darussan addini da kuma gudummawa a kasashen musulmi daban-daban da sassan jihohin Nijeriya da dama. Dauda Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Almajirai 17 Da Suka Rasu A Sakamakon Tashin Gobara A Zamfara Uwargidan Tinubu Ta Kai Wa Gwamnan Jigawa Ziyarar Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifiyarsa Da Ɗansa An gudanar da jana’izar malamin kamar yadda addinin musilunci ya tanada a gidansa da ke karamar hukumar Fufore a ranar Asabar. Sheikh Ibrahim Daware, ya rasu ya na da shekaru 71, ya bar matan aure hudu da ‘ya’ya 43 da jikoki 53.
    Xi Ya Umarci Ceto Daukacin Mutanen Da Suka Nutse A Ruftawar Kasar Da Ta Auku A Kudu Maso Yammacin Sin
    Ibrahim Yucel ya shafe shekaru 20 yana zukar taba sosai a lokacin da ya yanke shawarar ci gaba da zuka sosai. Jarabar son kowane irin abu ba shi da kyau, kuma zukar taba tana cikin mafi muni. Amurka ta dakatar da bai wa Afirka ta Kudu tallafi Yadda rikicin shugabanci ya janyo rufe babban masallacin gari Barin shan taba yana da matukar wahala, yana bukatar jajircewa da sadaukarwa. Duk da gagarumin kokarin da suke yi, kadan ne kawai na masu zukar sigari suka sami nasarar shawo kan jarabar son da suke yi mata. Kimanin shekara 11 da suka gabata, labarin wani mutum na kokarin daina shan taba ya shahara a talabijin da sauran kafafen yada labarai lokacin da ya saka...
    Manchester City ta tsallake rijiya da baya a gidan Orient, bayan ta doke su da ci 2-1, hakan ya sa ta tsallaka zuwa zagaye na biyar na gasar cin kofin FA ranar Asabar. Kamar kullum, Kevin De Bruyne ne ya fitar da kitse daga wuta ana gab-da za a tashi daga wasan. Mai tsaron ragar Manchester City, Stefan Ortega ne ya ci gida tun a minti na 16 da fara wasan, sabon dan wasan City Khusanov ne ya ci kwallonsa ta farko bayan dawowa daga hutun rabin lokaci kafin Kevin De Bruyne ya jefa ta biyu. Mutanen Guardiola kuwa su na matsayi na hudu a gasar Firimiya, hakazalika za su hadu da zakarun Turai, Real Madrid a gasar zakarun Turai...
      Ga Yadda zaku hada: Da farko za ku samu Tukunya sai ku zuba sukarin a ciki, ku dora shi a wuta ya narke ya yi zafi ya dan tafasa, sai ku kawo lemon tsami guda daya ku matse a ciki sai ku bar shi ya dan dahu sannan ku sauke. Sai ku samu roba me dan girma, ku zuba fulawar a ciki sannan ku kawo Baikin Fauda ita ma ku zuba sai ku zuba dan Gishiri kadan ba da yawa ba sai ku zuba Bota idan kuma ba kuda Bota za ku iya zuba mai ku kwaba da shi, sai ku kwaba sosai ku juya shi ya juyu sosai, sannan ku samu abin murzawa ku yi ta buga shi,...
    Jagoran juyin juya halin musulunci a nan Iran ya gana ta tawagar shoura ta kungiyar Hamas a safiyar yau Asabar a nan Tehran inda ya bayyana cewa mayakan kungiyar sun sami nasara a kan Amurka da HKI a yakin da suka dora masu na tsawon watanni 15. Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Imam Sayyid Aliyul Khaminae yana cewa tsagaita wuta da aka samu bayan wannan lokaci mai tsawo na fafatawa yayi dai-dai. Tawagar shuraa ta Hamas din dai sun hada da shugaban riko na kungiyar Khalil Al-Hayya, shugaban majalisar shoora ta kungiyar Muhammad Ismail Darwish da sauransu. Jagoran ya kara da cewa nasarar da mutanen Gaza suka samu a kan Amurka da kawayenta misdaki nan a...
    Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshiyan ya bayyana cewa, kasar Iran ba zata jada baya ba, kuma ba zati yi  rauni ba saboda takunkuman zaluncin da kasashen yamma suka dorawa kasar. Ya ce kasar tana da arzikin da zata ci gaba da kasancewa a gaba da kasashen da dama a yankin Asiya ta kudu, duk tare da wadannan takunkuman. Tashar talabijin ta Press tv ta nakalto shugaban yana fadar haka a yau Asabar a garin Sirjan, daga  na kudu masu gabacin lardin Kerman. Inda ya gabatar da kamfanoni da ayyukan jama’a wadanda aka kammala, wadanda suka hada har da sabbin wuraren yawon bude ido da kuma shakatawa. Shugaban y ace, kasar Iran ba zata jada baya ba, sannan makiyan kasar sun...
    Firay Ministan HKI Banyamin Natanyahu ya bawa kasar Saudiya Shawara samarwa Falasdinawa kasa daga cikin hamada mai girma da take da shi. Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Natanyahu yana fadar haka wa wata tashar talabijin ta HH a safiyar yau Asabar. Amma a maida martani ga Natanyahu, dan majalisar dokokin kasar Burtania a jam’iyyar Larbor Afzal Khan yace, wannan shawarar ta Natanyahu tabbaci ne na laifin fitta mutane daga kasarsu da karfi, don kawai ya na son a kwace zirin gaza daga Falasdinawa. Falasdinawa basa bukatan karin kasa suna son yenci ne a kasarsu. Inji dan majalisar dokoki Kim Johnson na jam’iyyar Lebour.. Kafin haka dai sarki Saman bin Abbdul azizi na kasar Saudiya yace ba...
    Albarkacin bikin bude gasar wasannin motsa jiki ta lokacin hunturu ta Asiya karo na 9 dake gudana a birnin Harbin na Sin, shugaban kwamitin shirya gasar Olympics ta kasa da kasa, Thomas Bach ya ziyarci cibiyar yada labarai ta gasar a jiya Juma’a, kuma ya yi hadin kai da shugaban rukunin gidajen rediyo da talibijin mallakin kasar Sin, wato CMG, Shen Haixiong, don bai wa runkunin na CMG damar tsarawa da kuma sarrafa watsa labarun gasar Olympics ta lokacin hunturu ta Milan da Cortina d’Ampezzo ta shekarar 2026. Shen Haixiong ya ce, gasar wasannin motsa jiki ta lokacin hunturu ta Asiya da ake shiryawa a birnin Harbin, wata kasaitaciyyar gasa ce ta kasa da kasa da Sin ta shirya bayan...
    Wata ‘yar uwa ana auranta aka kira ta ana yi mata nasiha sai ta ce ni dai kun dame ni da na yi hakuri na yi hakuri, tun da yana sona ina son shi kam ai shike nan, wallahi ko shekara daya ba’a yi ba ran nan na kai mata ziyara sai take cewa Amina ashe da ake cewa na yi hakuri nake ganin an dame ni da gaskiyarsu yanzu wallahi har gani nake hakurin da aka ce na yi ma ya yi kadan. To rayuwar aure sai da hakuri, idan muka yi hakurin nan da ake fada in sha Allahu za mu ga nasararsa a gaba, amma idan ba mu yi hakurin nan da ake fada mana ba za...
    A bayan nan ne mahukunta a Ƙaramar Hukumar Agege, a ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ƙaramar Hukumar Agege, Alhaji Ganiyu Kola Egunjobi suka kulle babban masallacin Hausawa na garin, biyo bayan wani rikici da ke da alaƙa da na limanci ya ɓarke a masallacin a ranar Juma’a makon jiya. Rikicin na zuwa ne bayan rasuwar babban limamin garin Agege, Shaikh Sharif Habib Abdul-Majid, wanda ya rasu kwanaki biyu gabanin aukuwar lamarin. Yadda Kano ke samar da madarar Naira biliyan 2.2 An dakatar da dagaci kan zargin saran maraya da adda A wani bidiyo da ya karade kafafen sada zumunta na zamani, an ga masallata a cikin masallacin suna kai wa junansu duka, wadanda suka haɗar da ɓangarori uku. Waɗanda suka bai wa...
      Yadda ake amfani da shi: Za ku dinga shafa zumar a gabanku, ku barta na tsawon mintuna 30, sai ku wanke da ruwan dumi, sannan ku shafa Man Zaitun. Za ku dinga yin haka safe da  yamma kafin kwanciya. Sannan ku dinga dafa ‘ya’yan hulba na tsawon mintuna 10 da ruwan da bai wuce kofi daya ba, sai ku dora shi a wuta ya dan tafasa bayan kun sauke shi sai ku tsiyaye shi sai ku sa masa zuma cokali uku, za ki yi wannan hadin shima safe da yamma.   Sai kuma maganin kurajen da kaikayin gaba: Kai tsaye ana cewa sanyin mara shi ne yake jawo wannan matsala, amma abin da ya kamata mu sani shi ne...
    Madara muhimmin abinci ne da ake bukata domin samun sinadarai masu ginawa da ƙara ƙarfi da lafiyar jiki. Bincike ya nuna cewa mutane biliyan shida ne ke shan madara a duniya, wanda ya sa shan madarar saniya da kiwon dabbobi ya zama wani vangare na rayuwar ɗan adam. Dubban mata Fulani suna samun kuɗaɗen shiga ta hanyar sayar da madara ga ɗaiɗaikun mutane ko jama’a ko ’yan kasuwa, waɗanda suke sha ko sarrafa shi domin amfanin kasuwanci. Lura da muhimmancin madara ga rayuwar ɗan Adam da kuma ƙoƙarin rage haɗarin da ke tattare da shan ta, Hukumar Haɓaka Noma da Kiwon Dabbobi ta Jihar Kano (KSADP) ta zuba jarin Dala miliyan 8.03 don gina cibiyoyi 100 na tattara madara...
    Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, ya sha alwashin gyara wa da faɗaɗa sansanin horas da matasan maus yi wa ƙsa hidima (NYSC) na dindindin a jihar. Da yake karɓar babban Daraktan NYSC, Birgediya Janar Yusha’u Ahmed a Maiduguri, Zulum ya ce gwamnatinsa za ta gaggauta gina sansanin dindindin domin karɓar ƙarin ‘yan bautar ƙasa. Ya kuma yaba da gudunmawar da likitoci da malaman kimiyya ke bayarwa a makarantu. Sin Ta Yi Bikin Tunawa Da Wadanda Aka Hallaka Yayin Kisan Kiyashin Birnin Nanjing Tinubu Ya Amince Da Naira Biliyan 80 Domin Sake Gina Madatsar Ruwa Ta Alau Da Ke Borno Shugaban NYSC ya gode wa gwamnatin Borno bisa tallafin da take bai wa ‘yan bautar ƙasa, ciki har da alawus na...
    A gasar Serie A 14:03 – Joao Felix (Chelsea – AC Milan) aro   Premier League 01:00 – Adel Disasi (Chelsea – Aston Billa) aro- 00:25 – Marshall Munetsi (Reims – Wolbes) ba a fayyace kudin ba. 00:15 – Carlos Alcaraz (Flamengo – Eberton) aro- 00:00 – Nasser Djiga (Red Star Belgrade – Wolbes) ba a fayyace kudin ba. 23:15 – Ben Chilwell (Chelsea – Crystal Palace) aro- 23:10 – Mathys Tel (Bayern Munich – Tottenham) aro – 23:00 – Nico Gonzalez (Porto – Manchester City) £50m 22:50 – Eli Junior Kroupi (FC Lorient – Bournemouth) ba a fayyace kudin ba. 21:32 – Somto Boniface (Chelsea – Ipswich) ba a fayyace kudin ba. 21:32 – Aled Palmer (West Brom –...
    Shugaban Amurka Donald Trump ya rattaba hannu a kan dokar da za ta rage tallafin da Amurka ke baiwa Afirka ta Kudu, wanda ake ganin bai rasa nasaba da karar Isra’ila da Afrika ta Kudu ta shigar kan kisan gilla a Zirin Gaza da kuma kwace filaye A ranar Juma’a ne fadar White House ta Amurka ta tabbatar da cewa Trump ya rattaba hannu kan wani kudiri na yanke tallafin kudi ga Afirka ta Kudu, saboda rashin amincewarsa da manufofinta na filaye, har ma da batun shigar da kara kan kisan gillar da ta yi a kotun kasa da kasa (ICJ) kan Isra’ila. Gwamnatin Trump ta ba da misali da shari’ar da Afrika ta kudu ta jagoranta kan Isra’ila a...
    Kwamandan rundunar sojin saman Iran ya bayyana cewa: Sun kai ga nasarar cimma matakin cin gashin kai a kere-keren kayayyakin aikin soja Kwamandan rundunar sojin saman Jamhuriyar Musulunci ta Iran Birgediya Janar Hamid Wahidi ya bayyana cewa: Sojojin saman Iran na ma’aikatar tsaro da taimakon sojojin kasar sun cimma mataki dari bisa dari a fagen gudanar da kere-keren kayayyakin da suke bukata a harkar tsaron kasa, kuma dukkanin kayan aikin wannan runduna an inganta su tare da mayar da su saffarin cikin gida. A ranar Juma’a 7 ga watan Fabrairu, Birgediya Janar Wahidi ya sanar a gaban taron kwamandojin sojojin saman Jamhuriyar Musulunci ta Iran da Jagoran juyin juya halin Musulunci a wata hira da aka yi da shi ta...
    Manyan jami’an kasar Jordan sun gargadi Amurka cewa: Idan ta janyo hargitsi a Jordan, to zai mamaye dukkan kasashen yankin gaba daya Shugaban majalisar dattijan kasar Jordan Faisal Al-Fayez ya jaddada a ranar Juma’a cewa: Ana daukar kasarsa a matsayin ginshikin zaman lafiya a yankin Gabas ta Tsakiya, yana mai cewa; Duk wani hargitsin da zai iya faruwa a kasar, zai shafi kasashen yankin baki daya, yana mai jaddada cewa: Kasashen yamma, musamman Amurka, suna da cikakkiyar masaniya game da wannan lamari. Al-Fayez ya bayyana cewa, a cikin hirarsa da tashar talabijin ta masarautar Jordan kan manyan kalubale da kasarsa ta fuskanta a baya, amma ta yi galaba a kansu da karfi da kuma tsayin daka, tare da dogaro da...
    Kazalka, matsalar ta sanya wasu iyalai da dalibai da dama a kasar yin kokarin jurewa matsin rayuwar da suke ci gaba da fuskanta, wanda hakan yak e kuma kara zamowa, babbar barazana ga rayuwarsu. Bisa fashin baki da rahoton ya yi ya nuna cewa, a shiyoyi shida na kasar, banbancin hauhawan farashin na kayan abincin, ya sha ban ban, inda a yakin Kudu Maso Yamma, lamarin na hauhawan farashin kayan abincin, ya fi yin kamari.
      An yabawa Gwamna Uba Sani saboda tsabtace harkokin hajji da kuma naɗa kwararru don jagorantar Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kaduna. Shugaban Kungiyar Yan Jaridu ta Kasa reshen Jihar Kaduna, Alhaji AbdulGafaar Alabelewe, ne yayi yabo yayin da jami’an kungiyar suka kai ziyarar ban girma ga hukumar. NUJ ta kuma bayyana naɗin Malam Salihu S. Abubakar a matsayin Shugaban Hukumar a matsayin wanda ya dace da mukami, inda suka jaddada cewa gaskiyarsa da bin doka da na da matukar muhimmanci wajen ci gaban hukumar. Alhaji AbdulGafaar ya ce hukumar ta samu nasarori masu yawa a lokacin hajjin da ya gabata, ciki har da maidawa kowane mahajjaci dala 50 daga kudin hadaya da suka biya a Najeriya. Ya kuma...
     Wanda ya jagoranci sallar juma’a a yau anan birnin Tehran, Hajjatul-Islam Kazim Saddiki, ya bayyana cewa: Trump yana yin baraza da tsoratarwa da cewa zai rage karfin da Iran take da shi a fagen fasahar Nukiliya da kuma matsayin da take da shi a cikin wannan yankin na yammacin Asiya, sai dai kuma ya kamata ya fahimci cewa kamar yadda shugaban da ya gabace shi ya yi kuskuren lissafi, to shi ma haka yake yi.” Limamin na Tehran ya kuma ce,Kamar yadda shugaban Amurka da ya gabaci Trump bai sami nasara akan Iran ba, shi ma haka ba zai cimma manufarsa ba. Hajjtul-Islam Siddiki ya kuma kara da cewa; Bai kamata ace muna  kallon cewa ta hanyar abubuwa na zahiri...
    Wasu da ake zargin ’yan fashi ne sun yi awon gaba da wani jirgin ruwa ɗauke da fasinjoji 20 a hanyar ruwan daga Bonny zuwa Okrika a Jihar Ribas. Sai dai jami’ai a ƙaramar hukumar Bonny ta ce ta kuɓutar da tara daga cikin fasinjojin yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike don ceto sauran. Jirgin Amurka ɗauke da mutum 10 ya ɓace Magungunan Jabu: ’Yan majalisa sun nemi yin hukuncin ɗaurin rai da rai Shugaban Ƙaramar hukumar Bonny, Hon Anengi Barasua Claude-Wilcox ya ce, an ceto mutanen tare da haɗin gwiwar jami’an tsaro. Claude-Wilcox a cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Boma Waribor ya fitar a ranar Juma’a, ya ce direban jirgin...
    Kasar Sin ta yi watsi tare da nuna kin amincewarta da tsegumin da aka yi mata daga bangaren Amurka, inda sakataren harkokin wajen Amurkar, Marco Rubio ya yi wasu zarge-zarge marasa tushe balle makama a kan kasar ta Sin, yayin da yake ziyara a yankin Latin Amurka da Caribbean. Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ya bayyana hakan a yau Juma’a, inda ya kara da cewa, kalaman marasa tushe daga bangaren Amurka, wadanda suka karkata zuwa tunanin yakin cacar-baka da nuna son zuciya, zarge-zarge ne kawai na yamadidi a kan kasar Sin da aka kitsa da nufin haifar da sabani tsakaninta da kasashen da abin ya shafa na Latin Amurka da Caribbean, wanda kuma hakan tsoma baki...
    An kaddamar da gasar wasannin motsa jiki ta lokacin hunturu ta nahiyar Asiya karo na 9 a yau 7 ga wata da dare, a birnin Harbin dake lardin Heilongjiang na kasar Sin, inda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya halarci bikin tare da kaddamar da gasar a hukumance. (Zainab Zhang)
    Majalisar Wakilan Tarayya ta buƙaci babban lauyan gwamnatin tarayya da ya gabatar da gyare-gyare ga dokokin da ake da su da nufin zartar da hukunci mai tsauri da suka haɗa da ɗaurin rai da rai ga waɗanda ke da hannu wajen sarrafawa da shigo da magungunan jabu. Da kuma gaggarumin tara ga ’yan kasuwar da aka samu da laifin yin mu’amala da jabun kayayyaki. ’Yan bindiga sun mamaye masallaci da awon gaba da masallata a Sakkwato Lakurawa sun kashe mutum 1 sun jikkata 6 a Kebbi Hakan ya biyo bayan wani ƙuduri kan muhimmancinsa ga jama’a da ɗan majalisa, Tolani Shagaya ya gabatar a zauren majalisar a ranar Alhamis. Ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta kafa dokar ta-ɓaci kan...
    “Babban shugaban sojoji da Babban mashawarcin shugaban kasa kan harkokin tsaro (NSA) suna aiki ba dare ko rana wajen tabbatar da wannan matakin, kamar yadda kuke gani muna sanya kumaji ga dukkanin rundunoni. “Sannan, an janye takunkumin hako ma’adinai a Zamfara, sannan wannan dalilin ne ya sanya muke ganawa a yau domin duba dukkanin bangarorin, inda muke da matsalar tsaro sosai sai mu ga yadda za mu kwato ayyukan,” Badaru ya shaida.
    Wasu da ake kyautata zaton ’yan bindiga ne sun yi garkuwa da wasu masallata a wani masallaci a unguwar Bushe da ke Ƙaramar hukumar Sabon Birni ta Jihar Sakkwato. Waɗanda da ake zargin ’yan bindiga ne sun kai farmaki masallacin ne da asubahin ranar Alhamis a yayin da masu ibada ke yin Sallar Subhi da asuba. Lakurawa sun kashe mutum 1 sun jikkata 6 a Kebbi Yadda bom din Boko Haram ya kashe mutane a hanyar kasuwa a Adamawa Aƙalla masallata 10 da suka haɗa da Limamin ne aka ce an yi awan gaba da su a yayin harin. Jaridar Punch ta ruwaito DSP Ahmed Rufa’i, kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Sakkwato ya tabbatar da faruwar lamarin a ranar Juma’a....
    Sanarwar ta ci gaba da cewa, “A ci gaba da kokarin da rundunar ‘yansandan Jihar Imo ke yi na dakile ayyukan ta’addanci a jihar, jami’an shalkwatar sashen Okigwe tare da hadin gwiwar mazauna unguwar Ogii a ranar 3/02/2025, sun kama wasu mutum uku da aka samu da kokon mutum, kaza da fararen kaya a kan titin Okigwe-Umuahia Edpressigwe. “Mutum ukun da aka kama—Patrick Okoere, Ifeanyichukwu Anyaemeka, da Chukwuemeka Onyekachi 20—ana kan bincike a halin yanzu. Yayin da ake yi masa tambayoyi, Patrick ya bayyana cewa kawun nasa, Osunta Oko, ya nemi ya sayo kokon kan mutum. Ya yi ikirarin cewa ya same shi ne a bakin kogi a kan babbar hanyar Okigwe-Umuahia, yankin da rundunar ke samun labarin sace-sacen mutane....
    Bama-bamai da mayakan Boko Haram suka binne sun kashe mutane biyu a hanyarsu ta zuwa kasuwa a Jihar Adamawa. Kakakin ’yan sanda a jihar Borno, ASP Kenneth Daso, ya ce mutane shida ne a cikin motar a lokacin motar da ta taka bam din a ranar Talatar bayan ta taso daga Karamar Hukumar Hawul ta Borno zuwa Kasuwar Garkida ta jihar Adamawa. “Ana zargin cewa ’yan Boko Haram ne suka dasa bama-baman, kuma motar da ke jigilar mutanen kauyen zuwa kasuwa a Garkida ta taka ta kuma ta fashe. “Wani dan shekara 25 ya mutu nan take, amma sauran fasinjojin an garzaya da su asibiti domin yi musu magani,” inji shi. Shugaban karamar hukuma ya biya wa al’ummarsa kudin wutar...
    Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran ya gana da tawagar kwamandojin sojojin sama da na tsaron sararin samaniyar kasar Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya gana da wata tawagar kwamandojin sojojin sama da na tsaron sararin samaniyar kasar na sojojin Jamhuriyar Musulunci ta Iran a safiyar yau Juma’a a daidai lokacin da ake gudanar da bukukuwan tunawa da kwanaki goma na samun nasarar juyin juya halin Musulunci. Taron na yau ya zo daidai da zagayowar kwanaki goma na samun nasarar juyin juya halin Musulunci, kuma taron tunawa da mubaya’a mai dimbin tarihi ga Imam Khumaini (Allah ya kara masa yarda) a ranar 8 ga watan Fabrairun shekara ta 1979. Don haka a safiyar...
    Tsohon ministan yakin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ya yi furuci da cewa: gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta ba da umarnin sojojinsu su kashe fursunoni yahudawa da masu tsaronsu a Gaza Tsohon Ministan tsaron gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila da aka kora Yoav Gallant a jiya Alhamis ya yi bayani kan matakan da sojojin mamayar Isra’ila suka dauka na tunkarar fursunonin yahudawan sahayoniyya da masu garkuwa da su a Zirin Gaza. A cewar shafin Falestine Today, Gallant ya ce: “Sun ba wa sojojin mamayar Isra’ila umarnin yin amfani da hanyar Hannibal, wato kashe fursunoni ‘yan uwansu da aka yi garkuwa da su tare da masu garkuwa da su a Gaza.” Ya kara da cewa: A jajiberin fara kai farmaki ta kasa kan...
    Majiyoyin sojin Sudan sun sanar da cewa: Sun sake samun nasarar kwace iko da babban birnin kasar Khartoum Majiyoyin sojin Sundan sun sanar da cewa: Cikin dan gajeren lokaci sun samu nasarar sake kwace iko da birnin Khartoum fadar mulkin kasar daga mamayar dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces, bayan da suka yi birnin kawanya daga bangarori hudu. A nata bangaren, Ma’aikatar yada labaran Sudan ta zargi bangarorin waje da jagorantar gudanar da fadace-fadacen da ‘yan tawayen dakarun kai daukin gaggawa ke yi don samun damar cin gajiyar albarkatun kasar, idan ‘yan tawaye suka yi nasara. Rayuwa ta fara inganta a birnin Omdurman kuma kasuwanni sun fara farfadowa, inda jama’a suke komawa ci gaba da harkokinsu na yau...
    Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe ta haramta yawon dare, ta hanyar takaita zirga-zirga daga kare 12 na dare zuwa 5 na asubahi. Kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi ya sanar a ranar Alhamis cewa dokar za ta fara aiki ranar Juma’a, 7 ga Fabrairu, 2025. Ya bayyana cewa an kafa dokar takaita zirga-zirgar ne bayan samun rahotannin barazanar tsaro. Sanarwar ta ce, “takaita zirga-zirgar na da nasaba da karuwar barazanar tsaro da ke fuskantar al’ummar Gombe,” kuma a shirye rundunar take ta shawo kansu. NAJERIYA A YAU: Dalilin Faɗuwar Farashin Tumatur A Kasuwa Majalisa na son ƙirƙiro sabbin jihohi 31 a Najeriya Mutuwar Almajirai: Tinubu ya buƙaci a samar da matakan kare ɗalibai DSP Buhari ya kara da cewa rundunar za...
    Rundunar sojin Najeriya ta ce tana aiki kan hanyoyin da za su yaki ‘yan bindiga da sauran masu tada kayar baya ta hanyar amfani da darussan da aka koya a wajen wani bada horo da ya gudana a Sakkwato.   Babban Hafsan Sojojin Najeriya Laftanar Janar Olufemi Oluyede ya bayyana haka a Sokoto a wajen wani taron karawa juna sani da nufin tattauna sabbin dabarun murkushe ‘yan bindiga da sauran ayyukan tada kayar baya a yankin Arewa maso Yamma, wanda aka gudanar a Runduna ta 8 ta Sojojin Najeriya dake Sokoto.   Wanda ya samu wakilcin babban hafsa Manjo Janar Olusegun Samson Abai, ya ce ziyarar wayar da kan ta taso ne domin inganta aikin da ake yi ta hanyar...
    Gwamna Sani ya bayyana zargin da kungiyar ta yi a matsayin maras tushe, yana mai jaddada cewa “Mafi yawan ‘yan siyasar da ke irin wadannan kalamai na iya zama suna magana da kansu ne kawai,” in ji shi. “Mun kasance a cikin jam’iyya daya a wani lokaci, kuma dole ne in ce na yi mamakin abin da suka yi.” Ya kara da cewa kawancen ba shi da wata hujjoji ta gaskiya kan ikirarin nasu. “Fito da zarge-zarge ba tare da hujja ba, wani yunkuri ne kawai na kawar da hankulan ‘yan Nijeriya,” in ji gwamnan. “Yawancin wadannan ‘yan siyasa sun rike mukamai a gwamnati kasa da shekaru biyu da suka gabata. Me suka yi a lokacin da suke kan mulki?”...
    Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da sauye-sauyen shugabanci a jami’o’in gwamnatin tarayya da dama da suka hada da Jami’ar Abuja wadda a yanzu ake kira da Jami’ar Yakubu Gowon.   A wata sanarwa da mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan yada labarai Bayo Onanuga ya ce a jami’ar Yakubu Gowon, shugaba Tinubu ya rusa majalisar zartarwa gaba daya tare da sauke Farfesa Aisha Sani Maikudi daga mukaminta na shugabar Jami’ar.   Sanata Lanre Tejuoso, wanda a halin yanzu shi ne uban Jami’ar Aikin Gona ta Makurdi ne aka nada shi a matsayin Uban Jami’ar Yakubu Gowon. Sanata Joy Emordi, wacce a yanzu ita ce shugabar jami’ar ilimi ta Alvan Ikoku za ta gaje shi a Makurdi....
    Gwamna Abba Kabir Yusuf ya ziyarci al’ummar Rimin Zakara da ke karamar hukumar Ungogo domin jajantawa iyalan wadanda rikicin ya rutsa da su wanda ya yi sanadin asarar rayuka uku tare da jikkata wasu da dama.   A ziyarar tasa, Gwamna Yusuf ya gana da iyalan wadanda suka rasu, inda ya jajanta musu tare da bayyana cewa gwamnatin jihar za ta dauki nauyin iyalan mutanen uku da suka rasu.   Ya kuma ba da umarnin a gaggauta biyan kudaden jinya ga duk wadanda suka jikkata tare da samar da kayan abinci don tallafawa iyalan wadanda abin ya shafa.   A cikin nuna jin kai, gwamnan ya bayyana shirin gina sabon masallacin Juma’a a Rimin Zakara a matsayin sadaqatu jariya (dauwamammiyar...
    In an taba rarrauna a gabanka, kana da ikon kare masa, to ka kare masa, kin kare masa sakaci ne ba hakuri ba ne. An ruwaito cewa, Annabi (SAW) bai taba dukan wata daga cikin Matansa ba ko kuma cikin masu masa hidima a gida ko a waje. An kama wani Mutum da yake shirin kashe Annabi (SAW), aka gurfanar da shi gaban Annabi (SAW), sai jikinsa ya fara makyerkyata, Annabi (SAW) ya ce masa, kar ka firgita, ko da ka yi niyyar kashe ni, Allah ba zai dora ka a kaina ba. Zaidu dan Sa’anatal Yahudi ya zo wurin Annabi (SAW) kafin ya Musulunta yana neman Annabi (SAW) ya biya shi bashin da ya karba a wurinshi. Sai ya...
    Obuah ya ce, makasudin yin bayanin shi ne don tabbatar da cewa masu aiki da doka ne kawai ke aiki a Babban Birnin Tarayya Abuja da kuma yaki da matsalar masu varna a yankin. Ya ci gaba da cewa, wani samame da ‘yansanda suka kai a wasu kasuwannin Pantaker a baya-bayan nan ya yi nasarar kwato dukiyar al’umma da aka sace da suka kai sama da Naira biliyan daya. “Saboda haka, Hukumar Babban Birnin Tarayya Abuja, tare da jami’an tsaro, ta bayar da umarnin cewa duk wani ma’aikacin pantaker dole ne a yi rajista da kuma bayyana sunansa. Wannan zai ba mu damar gano masu aiki na gaske kuma mu fahimci ayyukan kasuwancinsu. “Haka zalika za a bukaci masu gudanar...
    Shugaban kasar Amurka Donal Trump ya rattaba hannu a kan doka wacce ta yi allawadai da kutun kasa da kasa ta ICC saboda laifin fidda sammacin kama abokiyar Amurka firai ministan HKI da ta yi, sanadiyyar kissan kiyashin da ya yi a gaza. Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Trump ya na fadar haka a lokacinda yake rattaba hannu a kan dokar tasa a jiya Alhamis. Ya kuma kara da cewa kotun da ke birnin huqae ta wuce huruminta a lokacinda ta cutar kawar Amurka HKI tare da fidda sammacin kama shi. A ranar tarlatan da ta gabata ce Benyamin Natanyahu ya tattauna da shugaban Trump wanda yayi masa alkawula da dama, daga cikin har da  kwace...
    Obuah ya ce, makasudin yin bayanin shi ne don tabbatar da cewa masu aiki da doka ne kawai ke aiki a Babban Birnin Tarayya Abuja da kuma yaki da matsalar masu barna a yankin. Ya ci gaba da cewa, wani samame da ‘yansanda suka kai a wasu kasuwannin Pantaker a baya-bayan nan ya yi nasarar kwato dukiyar al’umma da aka sace da suka kai sama da Naira biliyan daya. “Saboda haka, Hukumar Babban Birnin Tarayya Abuja, tare da jami’an tsaro, ta bayar da umarnin cewa duk wani ma’aikacin pantaker dole ne a yi rajista da kuma bayyana sunansa. Wannan zai ba mu damar gano masu aiki na gaske kuma mu fahimci ayyukan kasuwancinsu. “Haka zalika za a bukaci masu gudanar...
    Ministan yaki na HKI Israel Kant ya umurci jami’an gwamnatin kasar su fidda wani tsari wanda zai bawa falasdinawa damar ficewa daga yankin Gaza a radin kansu. Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ministan ya na haka  bi sa umurnin da shugaba Trump na Amurka ya bayar na cewa ‘zai kwace Gaza’. Yace  Palasdinawa a Gaza su na so ko basa so za su bar Gaza, a bisa radin kansu ko kuma da karfi. Shugaban kasar Amurka yace ya dauki nauyin fidda Falasdinawa daga gaza, don wurin ya zama na yahudawan sahyoniyya kadai. Wasu masana suna ganin mai yuwa wannan shirin zai kawo karshen zaman lafiyan da aka samu, bayan yaki na watanni 15 da suka gabata....
    Babban kwamandan dakarun IRGC na kasar Iran Burgediya Janar  Hussain Salami ya bayyana cewa a dai dai lokacinda manya-manyan kasashen duniya suke amfani da takunkuman tattalin arziki, mafi muni a kan wasu kasashe, a lokacin ne kuma, dakarun IRGC  suke yunkuri don kare kammu daga makiya. Sannan samar da ci gaban da muke bukata don kawukammiu daga cikin gida. Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Salami yana fadar haka a jiya Alhamis, ya kuma kara da cewa, JMI ta na samun ci gaba duk tare da matsin lambar da ta take ciki. Kuma zata kara karfin sojojinta, don kare kanta daga duk wata kasa wacce teka barazana ga cibiyoyon Nukliyar kasar ko kuma tana son ta maida...
    Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkiya ya bayyana cewa juyin juya halin musulunci  a nan Iran ya zo ne da sakon zaman lafiya ga dukkan kasashen duniuya, don haka ne ta haramtawa kanta mallakan makaman nukliya wanda yake kissan kare dangi. Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto shugaban yana fadar haka a jiya Alhamis a taron da jakadun kasashen waje da manya-manya baki suka halatta a gidan shugaban kasa a nan Tehran. Sai dai shugaban ya kara da cewa kissan kananan yara baa bin amincewa ne a garemu, Sannan ya ce JMI bata amince da samuwar yan ta’adda a ko ina ba, kuma kasar Iran tana daga cikin kasashe wadanda suka fi cutuwa da ayyukan ta’addanci a duniya....
    More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba Shin mene ne dalilin faɗuwar farashin tumatir warwas a kasuwa? Idan ba a manta ba, a watannin baya farashin tumatir ya yi tashin gwauron zabo wanda aka daɗe ba’a ga irinsa ba. A wancan lokacin, sai da farashin ya kai ga iyalai da dama sun haƙura da shi sun koma sayen na gwangwani ko na leda. NAJERIYA A YAU: Tasirin Yankan Angurya A Rayuwar Mata DAGA LARABA: Yadda Al’adun Aure A Ƙasar Hausa Suka Koma ‘Event Centre’ Wannan ne batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokacin zai yi nazari a kai. Domin sauke shirin, latsa nan
    Binciken CGTN: Tasaruffi A Cikin Sanyi Ya Daukaka Sunan Harbin Da Nuna Yakini Ga Habakar Tattalin Arzikin Sin
    Gwamnan ya bayyana haka a yayin wata ziyarar ta’aziyya da ya kai yankin na Rimin Zakara a yammacin ranar Alhamis 06, ga watan Febarairun 2025.   A yayin ziyarar l, gwamnan ya yi alkawarin gina wa jama’ar yankin na Rimin Zakara katafaren Masallacin Juma’a a matsayin sadaka jariya ga wadanda suka rasu a dambarwar filayan yankin da Jami’ar Bayero. Gwamnan ya yi kuma alkawarin samar da Asibitin sha-ka-tafi da samar musu da hanya da kai hasken wutar lantarki da rijiyoyin burtsatsai da bai wa iyalan mamatan jari da daukar dawainiyar karatun yaransu gwargwadon iko da kuma daukar nauyin jinyar wadanda suka ji rauni a yankin a yayin rusau da aka yi a makon da ya gabata.
    Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya kara kudirin kasafin kudin shekarar 2025 daga naira tiriliyan 49.7 zuwa naira tiriliyan 54.2, yayin da majalisar dokokin kasar ke kokarin ganin an zartar da shi kafin karshen wata. Shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, ya sanar da karin kasafin ta hanyar wasiku daban-daban da shugaba Tinubu ya aikewa majalisar dattawa da ta wakilai. A cikin wasikar da aka karanta yayin zaman majalisar, Sanata Godswill Akpabio ya ce an sami  karin kudin ne sakamakon karin kudaden shigar da hukumar tara haraji ta kasa FIRS ta samu na Naira tiriliyan 1.4, yayin da hukumar hana fasakwabri  ta kasa ta tara Naira tiriliyan 1.2, da kuma Naira tiriliyan 1.8 da wasu hukumomin gwamnati suka tara. A don...
    Wasu ‘yan bindiga sun kai hari kauyen Tsiga da ke karamar hukumar Bakori a jihar Katsina inda suka yi garkuwa da tsohon Darakta Janar na Hukumar Kula da Matasa masu yi wa kasa hidima  NYSC, Birgediya Janar Maharazu Tsiga mai ritaya da wasu mutum takwas. Majiya mai tushe ta bayyana hakan ga gidan rediyon Najeriya a wata hira da manema labarai, yayin da ‘yan sanda ba su tabbatar da faruwar lamarin ba. Wani shaidan gani da ido ya bayyana yadda gungun  ‘yan bindigan  suka afkawa al’ummar a kan babura da misalin karfe sha biyu na dare. “Da misalin karfe 12 na dare ne ‘yan bindigar suka shigo garin na tsiga a bisa babura, inda suka rika harbi a sararin samaniya,...
    Babban jami’in jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin Cai Qi, ya yi kira a ranar Laraba, da a ci gaba da yin kokari wajen kawar da ayyukan da ba su da ma’ana, da rage nauyin da ke wuyan jami’an kananan matakai, don tabbatar kyakkyawan salon aiki tsakanin ’yan jam’iyya da jami’ai wajen cimma burin da aka sa a gaba a cikin shirin shekaru biyar-biyar karo na 14 wato daga shekarar 2021 zuwa ta 2025. Cai, wanda kuma mamban zaunannen kwamitin kula da harkokin siyasa na kwamitin kolin JKS ne, kuma mamba a sakatariyar kwamitin kolin JKS, ya bayyana hakan ne a wani taro na matakin koli game da wannan batu. Taron ya bayyana cewa, ya kamata a mayar da hankali wajen...
    Fitaccen Malamin Addinin Musulunci nan na Jihar Kaduna, Sheikh Ishaq Yunus Almadany, ya rasu bayan fama da rashin lafiya. Ya rasu a ranar Alhamis a Asibitin 44 Army Reference da ke Kaduna. An tsinci gawar Ɗan Majalisar da aka yi garkuwa a jajibirin Kirsimeti Tinubu ya sauke shugabar Jami’ar Abuja, ya yi sauye-sauye a jami’o’in Najeriya Jami’in hulɗa da jama’a na na kafafen sada zumunta na ƙungiyar Izalatul Bidia Waikamatus Sunnah (JIBWIS), Ibrahim Shehu Giwa ne, ya tabbatar da rasuwar. Shugaban JIBWIS reshen Jihar Kaduna, Alhaji Adamu Ibrahim, ya bayyana alhininsa, tare da yin addu’ar Allah Ya gafarta masa Ya kuma Aljanna makomarsa. Masallacin Sultan Bello da ke Kaduna, shi ma ya sanar da rasuwar malamin a shafinsu na Facebook,...
    Shugaban ƙasar Amurka, Donald Trump, ya sanya hannu kan sabuwar dokar da ta hana ‘yan wasan da sukai sauyin jinsi (transgender) shiga wasannin mata. Ya bayyana cewa wannan dokar zata kawo ƙarshen “cece ku ce da ake yi kan wasannin mata” tare da tabbatar da kariya ga ‘yan wasa mata daga fuskantar rashin adalci. A dokar Trump na neman a dakatar da makarantu daga samun tallafin gwamnati idan suka bari ‘yan wasan transgender su taka leda a ƙungiyoyin mata. Sin Ta Sanar Da Daukar Matakan Mayar Da Martani A Kan Karin Harajin Amurka Sin Za Ta Mai Da Martani Kan Dukkanin Cin Zalin Ciniki Da Aka Yi Mata Haka zalika, Trump ya shirya matsa wa ƙungiyar wasannin Olympics ta duniya...
    An kama wata matar aure bisa zargin ta da kashe dan kishiyarta ta hanyar zuwa masa  tafasasshen ruwa a kaciyarsa a garin Dawakin Tofa da ke Jihar Kano. ’Yan sanda a Jihar Kano na zargin matar ta je ta dauki yaron ne a wurin kakarsa, ida ake kula da shi bayan an yi masa kaciya, kasancewar mahaifiyarsa da mahaifin sun rabu. Bayanai sun nuna cewa duk da cewa kakar ta ki amincewa, amma sai da matar ta nace ta dauki yaron da cewa za ta kula da shi, bayan nan ne kuma sanya masa tafasasshen ruwa a gaban nasa, maimakon ruwan dumi. Duk da raunin da tafasasshen ruwan ya yi  masa kuma, sai aka kai shi wurin mai maganin gargajiya...
    Wata gobara da ta tashi a Ƙauyen Zago da ke Ƙaramar Hukumar Danbatta a Jihar Kano, ta ƙone gidaje, amfanin gona, da dabbobi, lamarin da ya janyo wa mazauna ƙauyen asara mai tarin yawa. Gobarar, ta fara ne da safiyar ranar Laraba, inda ta ƙone gidaje da dama tare da lalata hatsi da sauran amfanin gona. An yi garkuwa da tsohon Shugaban Hukumar NYSC Janar Tsiga Ɗan firamare ya je makaranta da bindiga yana barazanar harbe ɗalibai Har ila yau, ta kashe shanu da sauran dabbobi mallakin mazauna ƙauyen. Wasu daga cikin mazauna ƙauyen, Hayyo Zago da Abdulrahman Zago, sun ce gobarar ta ci gaba da ci har zuwa rana kafin jami’an kashe gobara su iss, inda suka yi nasarar...
    Biyo bayan nasarar da suka yi akan Alavés a ƙarshen mako, Barcelona za ta dawo taka leda a yau Alhamis don ƙarawa da Valencia a wasan daf da na kusa da na karshe a gasar Copa del Rey a filin wasa na Estádio de Mestalla dake Valencia. Barcelona na cigaba da jan zarenta a wannan shekarar ta 2025, inda ta buga wasanni da dama ba tare da tayi rashin nasara ba tun bayan shigowar sabuwar shekara, kuma daya daga cikin mafi kyawun sakamakon da ta samu ya zuwa yanzu a bana shi ne wanda ta doke Valencia da ci 7-1 kwanaki 10 da suka gabata. Har Yanzu Arsenal Ta Na Iya Lashe Gasar Firimiya Ta Bana – Alan Shearer Ba...
    Rundunar ‘yan sandan jihar Kebbi, ta kama wasu bakin haure 165 da aka ce sun fito ne daga kasashen da ke amfani da harshen Faransanci tare da mika su ga hukumar kula da shige da fice ta kasa dake jihar domin gudanar da bincike.   A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, SP Nafiu Abubakar ya fitar kuma ya mika wa gidan rediyon Najeriya a jihar Kebbi, ya ce, bisa rahoton bayanan sirri, an gano sama da mutum dari biyu a wani gida mai dakuna uku da ke unguwar Kuwait a cikin birnin Birnin Kebbi.   Sanarwar ta ce, tawagar jami’an ‘yan sanda da ke sashin binciken manyan laifuka (SCID) ne suka kai samame unguwar inda suka...
    Zulum Ya Jagoranci Dawowar Ƴan Gudun Hijira 7,790 Daga Chadi
    Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano, CP Salman Dogo Garba, ya gana da masu ruwa da tsaki a harkokin sufuri domin tattauna yadda ake ci gaba da aiwatar da aikin inshorar motoci na wasu motocin da ke bin hanyoyin jihar Kano.   Taron wanda ya samu halartar shuwagabannin kungiyar ma’aikatan sufuri ta kasa (NURTW), kungiyar masu safara a tituna ta Najeriya (NARTO), kungiyar ma’aikatan sufurin mota ta kasa (RTEAN), da kuma shugaban tashar motocin Kano Line da nufin tabbatar da bin ka’idojin inshora.   CP Dogo ya yabawa masu ruwa da tsaki bisa hadin kan da suka bayar, inda ya ce sama da kashi 85% na masu ababen hawa sun mallaki takardar inshorar motocin da ake bukata daga ranar farko da...
    Shugaba Xi Ya Gana Da Shugaban Pakistan 
    A wani umurnin da ya bayar Jagoran juyin juya halin musulunci a nan Iran, Imam Aya. Sayyid Alilul Khami’nae ya sanya babban sakataren kungiyar Hizbullah a matsayin wakilinsa a kasar Lebanon. Bayan shahadar Sayyed Hassan Nasarallah da kuma Sayyed Hashim safiyuddeen An zabi sheikh Na’em Kasim a matsayin babban sakataren kungiyar ta Hizbullah a kasar Lebanon. Kafin haka dai Shahid Sayyed Hassan Nasarallah ne mai wakiltar jagoran a kasar ta Lebanon. Sheikh Qasim dai  ya taka rawar a zo a gani  wajen yakin da kungiyarsa ta shiga da HKI na watanni 15.. Kuma ana saran shi ne zai zama mai fitar da kungiyar zuwa tudun na tsira daga halin da ta shiga ciki ya kuma ci gaba da yakar kungiyar.
    Wani Jami’in Ɗansanda Ya Bindige Kansa Har Lahira A Jihar Nasarawa
    More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba A tsakanin Hausawa  akan yi wa jaririya wani nau’i na kaciyar mata, wanda ake kira yankan angurya, kwana bakwai da haihuwarta. Ko mene ne alfanu ko illar wannan al’ada ga ’ya’ya mata? NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Noma Ba Tare Da Kashe Kuɗi Da Yawa Ba DAGA LARABA: Yadda Al’adun Aure A Ƙasar Hausa Suka Koma ‘Event Centre’ Albarkacin Ranar Yaƙi da Kaciyar Mata ta Duniya, shirin Najeriya  A Yau zai yi nazari a kan wannan al’ada da tasirinta a rayuwar mata. Domin sauke shirin, latsa nan
    Gwamnan ya yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasu da bai wa ‘yan’uwansu haƙurin jure wannan babban rashi, har ila yau gwamna Dauda Lawal ya yi addu’ar Allah ya bai wa wadanda suka samu raunuka lafiya. Gwamnati za ta yi bincike domin ta gano dalilin afkuwar wannan gobara, domin kaucewa hakan a nan gaba. A karshe ya ce gwamnati za ta bayar da duk wani taimakon da ake bukata da tallafi ga iyalan mamatan da kuma na asibiti.
    Sakamakon yadda kasar Sin take ci gaba da zurfafa yin gyare-gyare a gida daga dukkan fannoni, da kyautata bude kofa ga ketare bisa matakin koli, ya sa kasar ta Sin za ta ci gaba da kara azama kan bunkasar tattalin arziki. Za kuma ta ci gaba da nuna kuzari kan raya kanta tare da amfanar da duniya baki daya. (Tasallah Yuan)    
    Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran ya nada Sheikh Na’im Qassim a matsayin wakilinsa a kasar Lebanon Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya nada babban sakataren kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hizbullah Sheikh Na’im Qassim a matsayin wakilinsa a kasar Lebanon. Marigayi Sayyid Hassan Nasrullahi tsohon babban sakataren kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hizbullah da ya yi shahada, a yakin baya-bayan nan kan kasar Lebanon, shi ne tsohon wakilin mai martaba Imam Khamenei a kasar Lebanon kafin shahadarsa.