2025-02-21@14:49:39 GMT
إجمالي نتائج البحث: 923
«buga wasa a»:
(اخبار جدید در صفحه یک)
Gwamnatin kasar Argentina ta sanar da ficewarta daga hukumar lafiya ta duniya WHO. Mai magana da yawun shugaban kasar Manuel Adorni ya fadawa taron manema labarai cewa, shugaban kasar Javier Milei, ya umarci ministan harkokin wajen kasar Gerardo Werthein, da ya dauki matakin janye Argentina daga hukumar lafiya ta duniya. Adorni ya ce, ” ‘yan Argentina ba za su kyale wata kungiya ta kasa da kasa ta tsoma baki a harkokin da suka shafi ‘yancin kasarmu ba. “ Ya kara da cewa,”Ya kamata a fayyace cewa Argentina ba ta karbar kudade daga hukumar ta WHO don kula da lafiya, don haka, wannan matakin, kamar yadda wasu ke cewa, a kalla a shafukan sada zumunta, ba ya wakiltar asarar kudade ga kasar,...
Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya bayyana cewa : Gabadayen Falastinu tun daga kogi har zuwa teku ta al’ummar Falasdinawa ce. Jagoran ya jaddada goyon bayan Iran ne ga gwagwarmayar Falasdinawa kan kasarsu mai dimbin tarihi, tun daga kogin Jordan zuwa tekun Bahar Rum, kamar shafin offishin jagoran ya sanar. Kallaman Jagoran na zuwa ne a daidai lokacin da shugaban Amurka Donald Trump ya gabatar da wata shawara mai cike da cece-kuce na kaurar da Falasdinawa daga zirin Gaza da kuma sanya Amurka ta karbe yankin da yaki ya lalata. Ta hanyar yada wannan sako a cikin harsuna da dama, Iran ta nanata kudurinta na tabbatar da Falasdinu. Shugaba Trump na Amurka ya tsaya...
Ministan tsaron Isra’ila, Isra’ila Katz ya umarci sojojin gwamnatin kasar da su shirya wani shiri na “ficewar” Falasdinawa daga zirin Gaza. Umarnin Katz ya biyo bayan shawarar Shugaba Donald Trump na tilastawa Falasdinawa Gaza barin zirin da kuma sanya Amurka ta mamaye yankin da yaki ya lalata. “Na umurci IDF da su shirya wani shiri don ba da damar ficewa na radin kan mazauna Gaza,” in ji kakakin na Isra’ila a cikin wata sanarwa. Katz ya bayyana cewa ya fadawa sojojin Isra’ila da su yi shirin da “zai ba da damar duk wani mazaunin Gaza da ke son barin yankin zuwa, ga duk wata kasa da yake son karba.” Ministan tsaron Isra’ila ya kara da cewa “Tsarin zai hada da...
Ƙungiyar Malamai ta Najeriya NUT reshen Jihar Ebonyi ta sanar da fara yajin aikin sai baba-ta-gani a ƙananan hukumomi bakwai na jihar sakamakon rashin biyan albashin watanni. Yankunan da abin ya shafa sun haɗa da: Ebonyi, Edda, Ezza South, Ezza North, Ivo, Ishielu da Ƙaramar Hukumar Ohaukwu. Mutuwar Almajirai: Tinubu ya buƙaci a samar da matakan kare ɗalibai Uwa ta fusata ta jefa ’yarta cikin kogi a Bayelsa Ƙungiyar ta koka kan rashin biyan albashin sama da watanni uku ga malaman da ke Ƙananan hukumomin da abin ya shafa. Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun sakataren ƙungiyar, Bassey Asuquo kuma aka rabawa manema labarai a Abakiliki babban birnin jihar a ranar Alhamis. Sanarwar...
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya kara kudirin kasafin kudin shekarar 2025 daga naira tiriliyan 49.7 zuwa naira tiriliyan 54.2, yayin da majalisar dokokin kasar ke kokarin ganin an zartar da shi kafin karshen wata. Shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, ya sanar da karin kasafin ta hanyar wasiku daban-daban da shugaba Tinubu ya aikewa majalisar dattawa da ta wakilai. A cikin wasikar da aka karanta yayin zaman majalisar, Sanata Godswill Akpabio ya ce an sami karin kudin ne sakamakon karin kudaden shigar da hukumar tara haraji ta kasa FIRS ta samu na Naira tiriliyan 1.4, yayin da hukumar hana fasakwabri ta kasa ta tara Naira tiriliyan 1.2, da kuma Naira tiriliyan 1.8 da wasu hukumomin gwamnati suka tara. A don...
Wasu ‘yan bindiga sun kai hari kauyen Tsiga da ke karamar hukumar Bakori a jihar Katsina inda suka yi garkuwa da tsohon Darakta Janar na Hukumar Kula da Matasa masu yi wa kasa hidima NYSC, Birgediya Janar Maharazu Tsiga mai ritaya da wasu mutum takwas. Majiya mai tushe ta bayyana hakan ga gidan rediyon Najeriya a wata hira da manema labarai, yayin da ‘yan sanda ba su tabbatar da faruwar lamarin ba. Wani shaidan gani da ido ya bayyana yadda gungun ‘yan bindigan suka afkawa al’ummar a kan babura da misalin karfe sha biyu na dare. “Da misalin karfe 12 na dare ne ‘yan bindigar suka shigo garin na tsiga a bisa babura, inda suka rika harbi a sararin samaniya,...
Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci hukumomin ilimi su tabbatar da cewa makarantun gwamnati da masu zaman kansu sun ɗauki matakan kare ɗalibai daga haɗura. Wannan kira na zuwa ne bayan da wata gobara ta yi ajalin almajirai 17 a wata makarantar tsangaya da ke garin Ƙauran Namoda, a Jihar Zamfara. Allah Ya yi wa Sheikh Ishaq Yunus rasuwa Tinubu ya yi sauye-sauye a Jami’ar Abuja Gobarar, wacce ta tashi da daddare a ranar Talata, ta kuma jikkata wasu almajirai bakwai, amma yanzu haka suna asibiti ana kula da su. Shugaba Tinubu ya jajanta wa Gwamnatin Jihar Zamfara da iyalan waɗanda da suka rasa ’ya’yansu a wannan iftila’in, tare da yin addu’ar samun sauƙi ga waɗanda suka jikkata. Ya buƙaci makarantu...
Babban jami’in jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin Cai Qi, ya yi kira a ranar Laraba, da a ci gaba da yin kokari wajen kawar da ayyukan da ba su da ma’ana, da rage nauyin da ke wuyan jami’an kananan matakai, don tabbatar kyakkyawan salon aiki tsakanin ’yan jam’iyya da jami’ai wajen cimma burin da aka sa a gaba a cikin shirin shekaru biyar-biyar karo na 14 wato daga shekarar 2021 zuwa ta 2025. Cai, wanda kuma mamban zaunannen kwamitin kula da harkokin siyasa na kwamitin kolin JKS ne, kuma mamba a sakatariyar kwamitin kolin JKS, ya bayyana hakan ne a wani taro na matakin koli game da wannan batu. Taron ya bayyana cewa, ya kamata a mayar da hankali wajen...
Fitaccen Malamin Addinin Musulunci nan na Jihar Kaduna, Sheikh Ishaq Yunus Almadany, ya rasu bayan fama da rashin lafiya. Ya rasu a ranar Alhamis a Asibitin 44 Army Reference da ke Kaduna. An tsinci gawar Ɗan Majalisar da aka yi garkuwa a jajibirin Kirsimeti Tinubu ya sauke shugabar Jami’ar Abuja, ya yi sauye-sauye a jami’o’in Najeriya Jami’in hulɗa da jama’a na na kafafen sada zumunta na ƙungiyar Izalatul Bidia Waikamatus Sunnah (JIBWIS), Ibrahim Shehu Giwa ne, ya tabbatar da rasuwar. Shugaban JIBWIS reshen Jihar Kaduna, Alhaji Adamu Ibrahim, ya bayyana alhininsa, tare da yin addu’ar Allah Ya gafarta masa Ya kuma Aljanna makomarsa. Masallacin Sultan Bello da ke Kaduna, shi ma ya sanar da rasuwar malamin a shafinsu na Facebook,...
An tsinci gawar mai shari’a Azuka, Ɗan Majalisa mai wakiltar mazaɓar Onitsha ta Arewa a Majalisar Dokokin Jihar Anambra. An gano gawar Azuka da aka sace a jajibirin Kirsimeti a shekarar 2024 a kan gadar 2nd Niger Bridge, a cikin Anambra, ranar Alhamis. Uwa ta fusata ta jefa ’yarta cikin kogi a Bayelsa Yadda matar aure ta kashe dan kishiyarta da tafasasshen ruwa Marigayin yana hanyarsa ta zuwa bukukuwan ƙarshen shekara ne tare da ‘yan uwansa a lokacin da ’yan bindiga suka yi awon gaba da shi a Ugwunakpamkpa da ke cikin garin Onitsha. Sai dai jami’an tsaro da ke binciken sace shi sun cafke wasu da ake zargin sun kai su inda aka gano gawarwakin mambobin jam’iyyar Leba. Da...
A wani rahoto na ibtila’i da ya afku a unguwar Ukubie da ke ƙaramar hukumar Ijaw ta Kudu a Jihar Bayelsa inda wata mata mai suna Madam Stella ta jefa ‘yarta ’yar shekara shida mai suna Rachael a cikin kogi saboda fushi. A cewar shaidu, Rachael ta je yin wanka a bakin kogi duk da gargaɗin da mahaifiyarta ta yi mata. Yadda matar aure ta kashe dan kishiyarta da tafasasshen ruwa An sace tsohon Shugaban Hukumar NYSC, Janar Tsiga “Lokacin da mahaifiyar ta samu ’yarta a bakin kogin, sai ta fusata. Duk da gargaɗin da aka yi mata na ƙauracewa kogin, Rachael ta ƙi, wanda hakan ya sa mahaifiyar tashin hankali ta fusata,” in ji wani ganau. A cikin fushi,...
Shugaban ƙasar Amurka, Donald Trump, ya sanya hannu kan sabuwar dokar da ta hana ‘yan wasan da sukai sauyin jinsi (transgender) shiga wasannin mata. Ya bayyana cewa wannan dokar zata kawo ƙarshen “cece ku ce da ake yi kan wasannin mata” tare da tabbatar da kariya ga ‘yan wasa mata daga fuskantar rashin adalci. A dokar Trump na neman a dakatar da makarantu daga samun tallafin gwamnati idan suka bari ‘yan wasan transgender su taka leda a ƙungiyoyin mata. Sin Ta Sanar Da Daukar Matakan Mayar Da Martani A Kan Karin Harajin Amurka Sin Za Ta Mai Da Martani Kan Dukkanin Cin Zalin Ciniki Da Aka Yi Mata Haka zalika, Trump ya shirya matsa wa ƙungiyar wasannin Olympics ta duniya...
An kama wata matar aure bisa zargin ta da kashe dan kishiyarta ta hanyar zuwa masa tafasasshen ruwa a kaciyarsa a garin Dawakin Tofa da ke Jihar Kano. ’Yan sanda a Jihar Kano na zargin matar ta je ta dauki yaron ne a wurin kakarsa, ida ake kula da shi bayan an yi masa kaciya, kasancewar mahaifiyarsa da mahaifin sun rabu. Bayanai sun nuna cewa duk da cewa kakar ta ki amincewa, amma sai da matar ta nace ta dauki yaron da cewa za ta kula da shi, bayan nan ne kuma sanya masa tafasasshen ruwa a gaban nasa, maimakon ruwan dumi. Duk da raunin da tafasasshen ruwan ya yi masa kuma, sai aka kai shi wurin mai maganin gargajiya...
An kama wata matar aure bisa zargin ta da kashe dan kishiyarta ta hanyar zuwa masa tafasasshen ruwa a kaciyarsa a garin Dawakin Tofa da ke Jihar Kano. ’Yan sanda a Jihar Kano na zargin matar ta je ta dauki yaron ne a wurin kakarsa, ida ake kula da shi bayan an yi masa kaciya, kasancewar mahaifiyarsa da mahaifin sun rabu. Bayanai sun nuna cewa duk da cewa kakar ta ki amincewa, amma sai da matar ta nace ta dauki yaron da cewa za ta kula da shi, bayan nan ne kuma sanya masa tafasasshen ruwa a gaban nasa, maimakon ruwan dumi. Duk da raunin da tafasasshen ruwan ya yi masa kuma, sai aka kai shi wurin mai maganin gargajiya...
Biyo bayan nasarar da suka yi akan Alavés a ƙarshen mako, Barcelona za ta dawo taka leda a yau Alhamis don ƙarawa da Valencia a wasan daf da na kusa da na karshe a gasar Copa del Rey a filin wasa na Estádio de Mestalla dake Valencia. Barcelona na cigaba da jan zarenta a wannan shekarar ta 2025, inda ta buga wasanni da dama ba tare da tayi rashin nasara ba tun bayan shigowar sabuwar shekara, kuma daya daga cikin mafi kyawun sakamakon da ta samu ya zuwa yanzu a bana shi ne wanda ta doke Valencia da ci 7-1 kwanaki 10 da suka gabata. Har Yanzu Arsenal Ta Na Iya Lashe Gasar Firimiya Ta Bana – Alan Shearer Ba...
’Yan bindiga su yi garkuwa da tsohon Shugaban Hukumar Masu Yi Wa Kasa Hidima (NYSC), Manjo-Janar Maharazu Tsiga (ritaya). Rahotanni daga mahaifarsa Jihar Katsina na cewa maharan sun yi garkuwa da Janar Tsiga ne a ranar Laraba da dare. Bayanan sun bayyana cewa ƙauyensu Tisga da ke ƙaramar hukumar Ƙanƙara ta Jihar Katsina ne maharan suka yi awon gaba da shi tare da wasu mutum shida.
Rahotanni da suke fitowa daga kasar ta Bangaladesh sun ce, a jiya Laraba da marece ne wasu dalibai da sauran mutanen gari sun ka cinna wuta a cikin gidaje masu yawa, da su ka hada da na tsohon shugaban kasa Mujibur Rahman. Abinda yake faruwa yana nuni ne da dambaruwar siyasa da kasar take ci gaba da fuskanta da kuma rashin gamsuwar da mutanen kasar nunawa akan halin da ake ciki. Masu bin diddigin abinda yake faruwa a cikin kasar ta Bangaladesh suna cewa, kai hari a gidan Mujibur Rahman da ake girmamawa a fadin kasar yana nuni da zurfin matsalar da kasar take ciki. Masu Zanga-zangar suna bayar da taken yin kira ga juyin juya hali a kasar a...
An kama wani ɗalibin firamare mai shekara 13 ɗauke da bindiga a makaranta, inda yake barazanar harbe abokan karatunsa da ita. Bayan nan ne jami’an tsaro suka yi nasarar kama shi a Makarantar Firamare ta St. Paul da ke ƙauyen Ikot Ibiok a Ƙaramar Hukumar Eket a Jihar Akwa Ibom. A safiyar Alhamis ne kakakin runduanr ’yan sandan jihar, DSP Timfon John, ta sanar da kama yaron. DSP Timfon John ta bayyana cewa, a yayin bincike sun gano cewa yaron ya shafe kimanin wata uku yana zuwa da bindigar makaranta. An kashe wa ma’aurata ’ya’yansu uku an ɓoye gawarsu a firinji Zargin Tinubu: Gaskiya Naja’atu ta fada kan Nuhu Ribadu —El-Rufai NAJERIYA A YAU: Tasirin Yankan Angurya A Rayuwar Mata...
Mataimakin shugaban kasar Iran Muhamamd Riza Arif ya bayyana cewa, A halin yanzu ba ya cikin shirin gwamnatin Iran yin ganawa a tsakanin shugaban kasa Mas’ud Fizishkiyan da takwaransa na Amurka Donald Trump. A jiya Laraba ne mataimakin shugaban kasar Iran Riza Arif da ya yi Magana da ‘yan jarida inda yake mayar da martani akan fatan shugaban kasar Amurka Donald Trump na ganawa da shugaba Mas’ud Fizishkiyan na Iran, yana mai kara da cewa hakan ba ya cikin shirin gwamnati a wannan lokacin. Mataimakin shugaban kasar ta Iran ya kuma ce, ya kamata Trump ya san cewa, bisa fatawa ta addini da jagoran juyin musulunci ya fitar, Iran ba za ta mallaki makamin Nukiliya ba. Riza Arif ce Iran...
Kasashen larabawa masu kawance da Amurka sun kasance a sahun gaba wajen mayarwa da shugaban kasar Amurkan martani, bayan da ya bayyana cewa kasarsa za ta shimfida ikonta a Gaza, bayan fitar da Falasdinawa da Gaza. Gabanin wannan sanarwar ta Shugaba Donald Trump ya bayyana cewa ya tuntubi kasashen Jordan da Masar masu makwabtaka da Falasdinu da su karbi bakuncin mutanen Gaza na wani lokaci har zuwa sa’adda za a gyara wajen. Masar da Jordan sun yi watsi da wannan shirin da suke dauka a matsayin wata dabara ce ta fitar da Falasdinawa daga cikin kasarsu, da maye gurbinsu da yahudawa ‘yan share wuri zauna. A wani bayani da kungiyar hadin kan Larabawa ta fitar ta bayyana cewa; Abinda Trump...
Wasu ma’aurata sun tsinci gawarwakin kananan ’ya’yansu uku a boye a cikin wani firinji a yankin Nnewichi da ke Nnewi a Jihar Anambra. Iyayen yaran, Mista Udochukwu da Misis Chikazor Ejezie, sun tsinci gawar ’ya’yan nasu a cikin firinji ne bayan da suka dawo gida daga wurin aiki. Bayan dawowarsu ne suka samu gidan a bude ba yadda suka saba ba, kasancewar yaran suka kulle gidan a duk lokacin da za su je wasa. Da shigarma’auratan cikin gidan ne kuma suka ga gawarwakin yaran an sanya a cikin firinjin kayan kankara. Zargin Tinubu: Gaskiya Naja’atu ta fada kan Nuhu Ribadu —El-Rufai NAJERIYA A YAU: Tasirin Yankan Angurya A Rayuwar Mata Kotu ta ɗaure Farfesa shekara 3 kan aikata maguɗin zaɓe...
Kungiyar M 23 mai samun goyon bayan Rwanda ta kara samun gindin zama a gabashin kasar DRC, duk da cewa ta sanar da tsagaita wutar yaki ta gefe daya a jiya Laraba. Mayakan na M 23 sun sanar da kame babban binin gundumar Bukavu. Wani jami’in MDD wanda ya isa garin Goma ya bayyana cewa, Da akwai yiyuwar barkewar wani sabon rikici. MDD ta ce har yanzu ana ci gaba da yaki tsakanin sojojin gwamnati da kuma mayakin na kungiyar M 23. Garin Goma da mayakan na M 23 su ka kwace iko da shi, yana da ma’adanai kwance a kasansa da aka yi kirdadon cewa kudadensa sun kai na biliyoyin daloli.
Wasu ma’aurata sun tsinci gawarwakin kananan ’ya’yansu uku a boye a cikin wani firinji a yankin Nnewichi da ke Nnewi a Jihar Anambra. Iyayen yaran, Mista Udochukwu da Misis Chikazor Ejezie, sun tsinci gawar ’ya’yan nasu a cikin firinji ne bayan da suka dawo gida daga wurin aiki. Bayan dawowarsu ne suka samu gidan a bude ba yadda suka saba ba, kasancewar yaran suka kulle gidan a duk lokacin da za su je wasa. Da shigarma’auratan cikin gidan ne kuma suka ga gawarwakin yaran an sanya a cikin firinjin kayan kankara. Zargin Tinubu: Gaskiya Naja’atu ta fada kan Nuhu Ribadu —El-Rufai NAJERIYA A YAU: Tasirin Yankan Angurya A Rayuwar Mata Kotu ta ɗaure Farfesa shekara 3 kan aikata maguɗin zaɓe...
Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya goyi bayan Hajiya Naja’atu Muhammad a rikicinta da Mashawarcin Shugaban Kasa kan Sha’anin Tsaro, Nuhu Ribadu. Rikicin ya kunno kai ne bayan Naja’atu ta bulla a wani bidiyo inda take kushe Nuhu Ribadu ads aiki a gwamantin Tinubu alhali a lokacin da yake Shugaban Hukumar Yaki da Masu Karya Tattalin Arzikin Kasa (EFCC), ya soki Tinubu da zargin sa da almundahana a yayin taron Majalisar Zartaswa ta Kasa (FEC). Bayan haka ne Ribadu ta hannun lauyansa Ahmed Raji (SAN), ya bukaci ta janye kalaman nata tare da neman afuwarsa, yana mai barazanar maka ta kotu idan ba ta janye ba, domin kalaman nata na neman zubar masa da kima. Amma duka da haka,...
Mai martaba Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya yi kira da a zaman lafiya da hakuri a tsakanin al’ummar garin Rimin Zakara sakamakon rikicin filaye da ya barke tsakanin al’umma da Jami’ar Bayero ta Kano (BUK). Sarkin ya yi wannan roko ne a ziyarar da ya kai yankin bayan dawowarsa daga aikin hajji. Da yake jawabi ga al’ummar yankin, Sarkin ya jajantawa iyalan wadanda suka rasa rayukansu a rikicin tare da addu’ar Allah ya jikan wadanda suka jikkata cikin gaggawa. “Dole ne mu yi wa wadanda suka rasu addu’a da kuma baiwa iyalansu ikon jure wannan rashi, Allah ya sa wannan ya zama na karshe a cikin irin wannan mummunan lamari a cikin al’ummarmu,” inji...
Gwamnatin jihar Neja ta karbi yara ashirin da daya da aka kama a kan iyakar Najeriya da jamhuriyar Nijar yayin da ake safarar su zuwa Sudan. Mataimakin gwamnan jihar, Kwamared Yakubu Garba wanda ya bayyana haka a lokacin da yake karbar yaran a madadin gwamnatin jihar Neja a Minna, ya ce an kama yaran ne a cikin kasashen Kamaru da Mali da Jamhuriyar Nijar da kuma Sudan. Kwamared Yakubu Garba ya bayyana cewa yaran da aka ceto ‘yan karamar hukumar Magama ne a jihar Neja, amma ya yaba da kokarin gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro da kuma hukumar fataucin bil’adama bisa nasarar ceto yaran. Ya ci gaba da cewa ta’addancin ya saba wa kundin tsarin mulkin Najeriya...
Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano, CP Salman Dogo Garba, ya gana da masu ruwa da tsaki a harkokin sufuri domin tattauna yadda ake ci gaba da aiwatar da aikin inshorar motoci na wasu motocin da ke bin hanyoyin jihar Kano. Taron wanda ya samu halartar shuwagabannin kungiyar ma’aikatan sufuri ta kasa (NURTW), kungiyar masu safara a tituna ta Najeriya (NARTO), kungiyar ma’aikatan sufurin mota ta kasa (RTEAN), da kuma shugaban tashar motocin Kano Line da nufin tabbatar da bin ka’idojin inshora. CP Dogo ya yabawa masu ruwa da tsaki bisa hadin kan da suka bayar, inda ya ce sama da kashi 85% na masu ababen hawa sun mallaki takardar inshorar motocin da ake bukata daga ranar farko da...
Mataimakin shugaban kasar Iran kan al-amuran na Musamman Muhammad Javad Zareef ya bayyana cewa tattaunawa kadai da Amurka, ba zai warware matsalolin Iran ba. Kamfanin dillancin labarum IP na kasar Iran ya nakalto Zareef ya na fadar haka a taron majalisar ministocin da aka gudanar a jiya Laraba a nan Tehran. Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iram ya kuma nakalto mataimakin shugaban kasar yana cewa, maslahar daga Amurka Itace ta dagewa takunkuman tattalin arziki. Wasu masana dadama, sun bayyana cewa idan trump ya na son tattaunawa da Iran to da dole ne ta farko Amurka ta dorawa iran sannan a yi maganar tattaunawa. A jiya ne shugaban Trump ya bayyana anniyarsa ta shiga tattaunawa da kasar Iran yana kuma...
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi, a lokacin da yake maida martani ga jawabin shugaban kasar Amurka Donal Trump a jiya Laraba, ya ce takurawa mai tsanani ya karya. Abbas Aragchi ya fadi haka a jiya Laraba , ya kuma kara da cewa bayan takuarawa masu tsanani Amurka tana bukatar tattaunawa da Iran. Harma ya zauna da shugaban kasarta. A wani bangare na maida martanin Aragchi ya bayyana cewa dangane da fadinsa, ba zai taba amincewa Iran ta mallaki makaman Nukliya ba, yace Iran mamba ce a yarjeniyar NTP, a kuma hukumar makamashin nukliya ta IAEA. Zasu lamunce masa kan cewa Iran bata bukatar makaman nukliya. Amma duk da haka Iran ba zata taba sayar da hakkinta na mallakan...
Shugabannan Palasdinawa daga cikin har da kungiyar Hamas da Jahadul Islami duk sun ki amincewa da shirin trump na sake kwace Gaza, kafin haka kuma shugaban ya ce dole Falasdinawa su daga yankin kafin ya kwace shi. Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto shuwagabannin Palasdinawan suna allawadai da shugaban, sun kuma kara da cewa abinda HKI bata samu da yakin wattnin 15 ba, shugaba Trump ya na ya ba su da sauki da kuma wayon da za’a yiwa yaro. A ranar talata ce shugaban kasar Amurka Donal Trump ya bayyana cewa zai kwace Gaza a hannun Palasdinawa sannan ya sake gina shi. Falasdinawa kimani 61,700 suka rasa rayukansu a yayin da fiye da 100,000 ji rauni a...
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba A tsakanin Hausawa akan yi wa jaririya wani nau’i na kaciyar mata, wanda ake kira yankan angurya, kwana bakwai da haihuwarta. Ko mene ne alfanu ko illar wannan al’ada ga ’ya’ya mata? NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Noma Ba Tare Da Kashe Kuɗi Da Yawa Ba DAGA LARABA: Yadda Al’adun Aure A Ƙasar Hausa Suka Koma ‘Event Centre’ Albarkacin Ranar Yaƙi da Kaciyar Mata ta Duniya, shirin Najeriya A Yau zai yi nazari a kan wannan al’ada da tasirinta a rayuwar mata. Domin sauke shirin, latsa nan
Kamfanin hakar ma’adinai na Jiuling Lithium, na kasar Sin, na shirin zuba jarin sama da dala miliyan 200 a domin haƙar lithium a Endo da ke jihar Nasarawa. A ziyarar da gwamna Abdullahi Sule ya kai, shugaban kamfanin, Mista Xiong Jin, ya jaddada aniyarsu ta gina daya daga cikin manyan masana’antar samar da lithium a jihar. Ya kuma bayyana cewa ma’aikatan da aka dauka aiki a wurin za su sami mafi karancin albashi na N500,000. Saurayi Ya Fille Kan Budurwarsa A Nasarawa Gwamna Sule Ya Rushe Majalisar Zartarwar Nasarawa, Ya Sauke Sakataren Gwamnati Gwamna Sule ya bukaci matasa da su rungumi sana’o’in hannu domin cin gajiyar guraben ayyukan yi a fannin hakar ma’adinai. Ya kuma tabbatar da cewa gwamnatin jihar...
Kwanan baya, kasar Amurka ta sanar da kara harajin kashi 10 cikin dari a kan daukacin kayayyakin kasar Sin da ake kaiwa kasar, tare da kafa hujja da wasu batutuwa irin su maganin Fentanyl. Bayan haka, nan take kasar Sin ta sanar da daukar matakan mayar da martani a kan karin harajin Amurka domin kare hakki da moriyarta yadda ya kamata. Saan nan, a ranar 4 ga wata, Sin ta gabatar da cewa, tun daga ranar 10 ga watan Fabrairun shekarar 2025, za ta sanya harajin kashi 10% zuwa 15% kan wasu kayayyakin da ake shigowa da su daga Amurka. A sai daya kuma, kasar Sin ta shigar da kara kan matakan da Amurka ta dauka na karin haraji a...
Gwamnan ya yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasu da bai wa ‘yan’uwansu haƙurin jure wannan babban rashi, har ila yau gwamna Dauda Lawal ya yi addu’ar Allah ya bai wa wadanda suka samu raunuka lafiya. Gwamnati za ta yi bincike domin ta gano dalilin afkuwar wannan gobara, domin kaucewa hakan a nan gaba. A karshe ya ce gwamnati za ta bayar da duk wani taimakon da ake bukata da tallafi ga iyalan mamatan da kuma na asibiti.
“Canada, Mexico da Sin su ne suke sayen rabin duk kayayyakin amfanin gona da Amurka ke fitarwa. Kasuwanni ne da muke bukata babu makawa don raya tattalin arzikin Amurka. Sanya haraji kan manyan kasuwannin fitar da kayayyakin guda uku na noma da kiwo na Amurka, musamman na dogon lokaci zai haifar da mummunan sakamako,” in ji sanarwar. Tabbas! abin da manoman suka fada gaskiya ne, domin ko a shekarar 2018, karin harajin da Amurka ta kakkaba a kan kayayyakin kasar Sin, ya janyo kasar ta Sin wadda a baya ita ce ta fi shigo da wake na Amurka, ta sanya karin harajin kashi 25 cikin 100 na ramuwar gayya kan kayayyakin da Amurka ke fitarwa. Kuma a yanzu ma, Sin...
Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran ya nada Sheikh Na’im Qassim a matsayin wakilinsa a kasar Lebanon Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya nada babban sakataren kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hizbullah Sheikh Na’im Qassim a matsayin wakilinsa a kasar Lebanon. Marigayi Sayyid Hassan Nasrullahi tsohon babban sakataren kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hizbullah da ya yi shahada, a yakin baya-bayan nan kan kasar Lebanon, shi ne tsohon wakilin mai martaba Imam Khamenei a kasar Lebanon kafin shahadarsa.
Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Tsananta matsin lamba da ake son dauka kan Iran ba zai yi wani tasiri ba Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya jaddada cewa: Manufar matsin lamba da shugaban Amurka Donald Trump ya dauka kan Iran za ta sake yin kasa a gwiwa tare da rashin nasara. Araqchi ya bayyana a cikin wata sanarwa da ya fitar bayan kammala zaman majalisar ministocin a yau Laraba, inda ya ce mafi girman matsin lamba shi ne gwajin da aka yi kan kasar Iran da bai yi nasara ba, ya kara da cewa; Idan babban batu shi ne cewa Iran ba ta kama hanyar mallakar makamin nukiliya ba, to hakan na iya yiwuwa kuma babu...
Saka sunan Taye Taiwo a cikin jerin zakakuran yan wasan kungiyar ya nuna yadda dan wasan ya nuna bajinta da kuma yadda ita kanta kungiyar ta Marseille ta yaba da irin kokarin da ya yi a baya.
Jami’in tsaron kasar Iran ya karyata sabuwar da’awar jaridar New York Times ta kasar Amurka Jami’in tsaron kasar Iran ya musanta wasu sabbin zarge-zargen da jaridar New York Times ta Amurka ta wallafa game da zargin Iran cewa tana bunkasa ayyukannta na kera makaman kare dangi. Jami’in tsaron ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Tasnim cewa: Ikirarin da jaridar New York Times ta yi game da wata kungiyar asiri ta masana kimiyyar Iran da ke aikin samar da hanyoyin kera makaman nukiliya cikin sauri, ba komai ba ne illa shirme da zage-zage marasa tushe da kan gado. Jami’in ya kara da cewa: “Wadannan rudun tunani ba su da alaka da gaskiya, kuma kawai labaran karya ne da wasu kafafen yada...
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Iran za ta mayar da martani ga duk wata barazana ko matsin lamba gwargwadon tsayin dakarta Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya bayyana cewa: Iran ta sha tabbatar da cewa a shirye take ta gudanar da huldar siyasa da diflomasiyya don tabbatar da moriyar kasa, kuma tana shirye ta gudanar da kumajin siyasa da diflomasiyya wajen kare muradunta da tsaron kasa, sannan tana da azamar daukan duk wani matakin kare kanta da masalaharta tare da mayar da martani ga duk wata barazana ko matsin lamba gwargwadon tsayin daka da gwagwarmayarta. Isma’il Baqa’i ya bayyana haka ne a yayin da yake mayar da martani ga tambayar cewa; Maganganun da shugaban...
Sojojin Sudan sun kwace iko da birnin Al-Kamlin da ke jihar Aljazira a tsakiyar kasar Rundunar sojin Sudan ta sanar a yau jiya Talata cewa: Sojojinta da mayakan da suke goya musu baya sun kwace iko da birnin Al-Kamlin da ke jihar Aljazira a tsakiyar kasar, kuma babban hafsan hafsoshin rundunar sojin kasar Janar Abdul-Fattah Al-Burhan ya yi alkawarin samun nasara a nan kusa kadan kan wadanda ya kira ‘yan tawaye. Sojojin Sudan sun watsa labarin ta hanyar kafofin Facebook da Instagram tare da wallafa faifan bidiyon yadda al’ummar birnin suka fito kan tituna suna bayyana murnarsu da ‘yantar da birninsu daga hannun ‘yan tawaye tare da bayyana wannan nasara a matsayin babban ci gaba ga sojojin Sudan. A nasa...
Wata gobara da ta tashi a wata makarantar tsangaya da ke Ƙaramar Hukumar Kaura-Namoda a Jihar Zamfara, ta yi ajalin almajirai 17. Dukkanin almajiran sun ƙone ƙurmus, ta yadda ba a gane kowa a cikinsu ba. Saura ƙiris Bello Turji ya zo hannu – Ministan Tsaro Tinubu ya ƙara kasafin kuɗin 2025 zuwa N54.2trn Shaidu sun bayyana cewa gobarar ta farq ne cikin daren ranar Talata, kuma ta ɗauki kimanin sa’o’i uku tana ci. Rahotanni sun bayyana cewar wasu almajirai 16 sun samu munanan raunuka a gobarar. Wani mazaunin yankin, Abdulrasaq Bello Kaura, ya bayyana cewa gobarar ta fara ne sakamakon kamawar wasu itatuwa da aka ajiye. Wani ganau ya shaida cewar, “Abin ya faru ne a makarantar Malam Ghali,...

Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Yabawa Gwamna Namadi Bisa Amincewa Da Tsarin Bada Tallafi A Mazabu
Majalisar Dokokin Jihar Jigawa ta yabawa Gwamna Umar Namadi bisa amincewarsa ga manufar majalisar, ta bullo da tsarin bada tallafin sana’oi na mazabu ba tare da jinkiri ba. Shugaban Majalisar, Alhaji Haruna Aliyu Dangyatin ya bayyana haka a lokacin da yake kaddamar da rabon tallafi wanda wakilin mazabar Kanya a majalisar dokokin jihar,Alhaji Ibrahim Hashim Kanya, ya bai wa al’ummar garin Kanya dake karamar hukumar Babura. Yana mai cewar, majalisar ta bullo da tsarin bada tallafin domin mara baya ga Kudurorin Gwamna Umar Namadi guda goma sha biyu, ta fuskar bunkasa tattali da samar da ayyukan yi ga jama’a. A jawabinsa, wakilin mazabar Kanya Alhaji Ibrahim Hashim Kanya, ya ce mutane 1,350 ne za su amfana da tallafin...
Ministan Tsaro, Muhammad Badaru Abubakar, ya bayyana cewa sun kusa da kama ƙasurgumin ɗan ta’addan nan da ya addabi yankin Arewa Maso Yamma, Bello Turji. Ministan ya ƙara da cewa Gwamnatin Tarayya tana da tabbacin cewa matsalar tsaro za ta zama tarihi kafin ƙarshen shekarar 2025. Sarkin Jiwa a Abuja ya yi rashin mahaifiya Tinubu ya ƙara kasafin kuɗin 2025 zuwa N54.2trn “Shugaban ƙasa na cewa yaushe matsalar tsaro za ta ƙare, saboda lokacin da ya kamata ta ƙare ya yi. “A wani zama da muka yi da shi da shugabannin hafsoshin tsaron, an tattauna sosai, kuma shugaban ya ce su faɗa masa yaushe matsalar za ta ƙare, suka ce da yardar Allah zuwa ƙarshen shekarar nan,” in ji shi....
Mai martaba sarkin Jiwa a yankin birnin tarayya Abuja, Alhaji Idris Musa ya yi rashin mahaifiyarsa mai suna Hajiya Ramatu Ibrahim. Ta rasu ne a safiyar Lahadi kamar yadda sarkin malamai na masarautar malam Jibrin Yakubu Adam ya tabbatarwa Aminiya. Hajiya Mai Babbar Ɗaki, kamar yadda ake yi mata laƙabi, ta rasu ta bar ‘ya’ya huɗu da kuma jikoko sama da 30. Ya ce, an gudanar da janaiza tare da binneta a Babbar maƙabartar Garin Jiwa a ranar ta Lahadin. Tinubu zai tafi Faransa daga nan ya zarce Habasha Jami’ar ABU da ke Zariya ta yi sabon shugaba Cikin waɗanda suka halarci jana’izar akwai Sarkin Bwari Alhaji Muhammad Auwal Ijakoro, da Gomo na Kuje Alhaji Haruna Tanko Ibrahim, da...
Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya buƙaci a ƙara adadin kasafin kuɗin shekarar 2025 daga Naira tiriliyan 49.7 zuwa Naira tiriliyan 54.2. Wannan buƙata na ckkin wata wasiƙa da ya aike wa Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, wadda aka karanta a zaman majalisar na ranar Laraba. Tinubu zai tafi Faransa daga nan ya zarce Habasha NAHCON ta tsawaita wa’adin biyan kuɗin Hajjin bana A baya, Tinubu ya gabatar wa Majalisar Dokoki kasafin Naira tiriliyan 49.7 a ranar 18 ga watan Disamba. 2024. Sai dai a cikin wasiƙarsa, ya bayyana cewa ƙarin da aka yi ya samo asali ne daga ƙarin kuɗaɗen shiga da hukumomin gwamnati suka tara. Wannna ya haɗa da Naira tiriliyan 1.4 da Hukumar Tara Haraji ta...
A yau ne shugaba Bola Ahmed Tinubu zai tashi daga Abuja zuwa birnin Paris na kasar Faransa a wata ziyarar kashu kai, inda daga nan zai wuce Addis Ababa, babban birnin kasar Habasha. A cikin wata sanarwa da mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Bayo Onanuga ya fitar, ya ce a birnin Addis Ababa, shugaba Tinubu zai bi sahun shugabannin Afirka a zaman taron majalisar zartarwa karo na 46 da kuma zaman taro na 38 na shugabannin kasashen kungiyar tarayyar kasashen Afirka wato AU, wanda aka shirya daga ranar 12 zuwa 16 ga watan Fabarairun 2025. Shugaban zai isa Addis Ababa a farkon mako mai zuwa don halartar taron kungiyar ta AU. Yayin da yake...
Ancelotti ya shaidawa manema labarai ranar Talata cewa “Bellingham ya samu rauni yayin atisaye amma kuma Vinicius Jr zai buga wasan gobe duk da cewar har yanzu ya na kan murmurewa daga raunin da ya ji a watan jiya Ya kuma ce Mbappe ya yi atisaye kamar yadda aka saba a yau, amma gobe ba zai samu damar buga wasan ba, Madrid ce kan gaba a teburin La Liga da maki 49 a wasanni 22, maki daya tsakaninsu da Atletico Madrid wadda zasu hadu ranar Asabar a Santiago, bayan nan kuma zasu ziyarci zakarun Ingila, Manchester City a gasar cin kofin zakarun Turai a ranar 11 ga Fabrairu.
Shugaba Bola Tinubu a wannan Larabar zai bar Nijeriya zuwa ƙasar Faransa domin kai wata ziyara ta ƙashin kai. Daga nan kuma Shugaba Tinubu zai wuce ƙasar Habasha inda zai halarci taron gamayyar ƙungiyar ƙasashen Afirka ta AU. NAHCON ta tsawaita wa’adin biyan kuɗin Hajjin bana Dalilin da farashin citta ya yi tashin gwauron zabo Mai bai wa Tinubu shawara kan yaɗa labarai, Bayo Onanuga a shafinsa na X, ya ce Tinubu zai tafi Paris ɗin ne gabanin tafiyar da zai yi zuwa Addis Ababa, babban birnin Habasha domin taron ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU). A lokacin taron da za a yi a birnin na Addis Ababa a farkon mako mai zuwa, Shugaba Tinubu zai gana da shugabannin ƙasashen Afirka domin...
Shugaba Bola Tinubu a wannan Larabar ya bar Nijeriya zuwa ƙasar Faransa domin kai wata ziyara ta ƙashin kai. Daga nan kuma Shugaba Tinubu zai wuce ƙasar Habasha inda zai halarci taron gamayyar ƙungiyar ƙasashen Afirka ta AU. NAHCON ta tsawaita wa’adin biyan kuɗin Hajjin bana Dalilin da farashin citta ya yi tashin gwauron zabo Mai bai wa Tinubu shawara kan yaɗa labarai, Bayo Onanuga a shafinsa na X, ya ce Tinubu zai tafi Paris ɗin ne gabanin tafiyar da zai yi zuwa Addis Ababa, babban birnin Habasha domin taron ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU). A lokacin taron da za a yi a birnin na Addis Ababa a farkon mako mai zuwa, Shugaba Tinubu zai gana da shugabannin ƙasashen Afirka domin...
Shugaban Hukumar jin dadin Alhazai ta Nijeriya (NAHCON), Farfesa Abdullahi Saleh Usman ya sanar da tsawaita wa’adin biyan kudin kujerar aikin hajjin 2025 zuwa ranar 10 ga Fabrairu, 2025. Karin wa’adin na zuwa ne biyo bayan koke-koke da aka kai wa hukumar na a kara wa maniyyatan da suka gaza kammala biyan kudinsu a kan lokaci. Nijeriya Na Iya Fuskantar Ƙarancin Maniyyata A Hajjin Bana EFCC Ta Gurfanar Da Manajan Darakta Kan Damfarar ₦144m A Gombe Farfesa Usman ne ya bayyana hakan a yayin wani taro da ya gudana a manhajar ‘Zoom’ a ranar Talata 4 ga watan Fabrairu, 2025, tare da masu ruwa da tsaki a shirye-shiryen gudanar da aikin Hajji. Shugaban Hukumar NAHCON ya yi kira ga Sakatarorin...
12-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa Shirin wanda yake kawo maku kissoshi wadanda suka zo cikin alkur’ani mai girma ko cikin wasu littafan wadanda suka hada da littafin Dastane rastan na shahid Aya. Murtadha muttahhari, ko cikin littafin Mathnawi na maulana jalaluddeen ,Rumi, ko kuma cikin wasu littafan. Da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu. ///… Madalla, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata, mun ci gaba da kawo maku sirar Imam Alhassan (s) Jikan manzon All..(s) sannan limami na 2 daga cikin limamai masu tsarki daga iyalan gidan manzon All..(s) kuma da na farko ga Fitima(s) diyar manzon All..(s). Kuma...
Yayin da Hukumar Kula da Hajji ta Kasa ta kara wa’adin biyan kudin Hajjin bana zuwa ranar 10 ga watan Fabrairu, Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kaduna ta umarci dukkan ofisoshin da suke alhakin yin rajista su tabbatar da an yi wa duk masu sha’awar tafiya Hajji rajista kafin ƙarshen wa’adin da aka ƙara. Shugaban Hukumar, Malam Salihu Abubakar, ya kuma yi kira ga dukkan maniyyatan da ba su kammala biyan kuɗinsu ba da su gaggauta yin hakan. Ya jaddada cewa ba za a ƙara wa’adin bayan ranar 10 ga Fabrairu ba, don haka ya bukaci maniyyata su yi amfani da wannan damar su kammala rijistarsu kafin ko zuwa Litinin, 10 ga Fabrairu, 2025. Rel/Adamu...
Sojojin sama na JMI sun sami nasarar kakkabo jiragen yaki na makiyan da aka sawwara, tare da amfani da makami mai suna Majid a cikin atisayen sojojin sama da suke gudanarwa a kudu masu yammacin kasar. Jiragen yaki wadanda ake sarrafasu daga nesa dai, suna da masu muhimmanci a yakin zamani a halin yanzu, don haka sojojin sama na kasar suka bawa al-amarin muhiommanci. Banda haka tana da makiya wadanda suke da su a yankin wadanda suek amfani da irin wadannan makamai. A atisayen dai an sawwara jiragen makiya da dama a sararin samaniya, wadanda suke kokarin fadawa kasar, sannan aka cilla makaman garkuwan sararin samaniya samfurin Majid wadanda suka kakkabosu gaba daya.
Jami’an ‘yansanda tare da hadin gwiwar mafarauta sun kashe wasu da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne a Dajin-madan, da ke karamar hukumar Alkaleri a jihar Bauchi. Da yake tabbatar da faruwar lamarin ga wakilinmu a safiyar ranar Laraba, Kakakin Rundunar ’Yansandan Jihar Bauchi, CSP Ahmed Wakil, ya ce an kashe ‘yan bindigar ne ta hanyar amfani da bayanan sirri da hadin gwiwa da masu sa ido da ke cikin al’ummomin da abin ya shafa. Tinubu Ya Amince Da Naira Biliyan 80 Domin Sake Gina Madatsar Ruwa Ta Alau Da Ke Borno Masana Kimiyyar Sin Sun Kirkiro Sabuwar Fasahar AI Mai Hasashen Zuwan Mahaukaciyar Guguwa Ya kara da cewa, bayan artabun, wasu daga cikin ‘yan bindigar sun tsere da raunukan harbin...
Hukumar Alhazai ta Nijeriya NAHCON ta sanar da tsawaita wa’adin karɓar kuɗin aikin Hajjin bana. NAHCON ta ce daga yanzu zuwa 10 ga watan Fabrairu ƙofa a buɗe take ta ci gaba da karɓar kuɗin kujera ga maniyyatan da ke son sauke farali a bana. Jami’ar ABU da ke Zariya ta yi sabon shugaba An soma rigimar haraji tsakanin China da Amurka Ana iya tuna cewa, da misalin ƙarfe goma sha biyun daren ranar Juma’a 31 ga watan Janairun 2025, ne wa’adin biyan kuɗin kujerun aikin hajjin bana ya cika. Sai dai cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Hukumar NAHCON ta ƙasa, Fatima Sanda Usara ta fitar, ta ce tsawaita wa’adin wata dama ce ga maniyyatan da ba...
Kasar Afirka Ta Kudu ta ga yadda Palasdinawa suka jajirce wajen kare kansu daga HKI ne, ya sa ta gurfanar da HKI a gaban kutun ICC don kawo karshen kissan kiyashin da yahudawan suke masu. Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya kara da cewa, kasar Afirka ta gudu dai tana dade tana goyon bayan masu gwagwarmayan neman yencinsu a duniya daga ciki da da kasar Falasdinu da aka mamaye. Har ila yau da kuma ganin tarihin da kasar take da shi, na yaki da wariyar launin fata a kasar, duk sun hadu sun karfafa ta wajen daukar wannan matakin kan HKI. Jakadan kasar Afirka ta kudu a nan Tehran, Francis Moloi ne ya fadawa kamfanin dillancin labaran ‘Iran...
Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya ta sanar da naɗa sabon shugabanta, Farfesa Adamu Ahmed. Majalisar Gudanarwar jami’ar ce ta zaɓi Farfesa Adamu Ahmed a matsayin wanda zai maye gurbin Farfesa Kabir Bala. An soma rigimar haraji tsakanin China da Amurka Dalilin da farashin citta ya yi tashin gwauron zabo An sanar da zaɓen Farfesa Adamu da misalin ƙarfe 6:15 na safiyar wannan Larabar a yayin zaman Majalisar Gudanarwar jami’ar wanda Mahmud Yayale Ahmed CFR ya jagoranta. Farfesa Adamu Ahmed dai malami ne a sashen nazarin tsara birane na jami’ar ta ABU. Ya taɓa riƙe muƙamin Darektan Cibiyar Bunƙasa Jami’ar kuma a yanzu shi ne Uban Jami’ar Ilimi ta Tarayya da ke Kano.
An kuma samu labarin cewa ɗalibin ya rasa mahaifinsa a wasu shekarun baya, lamarin da ya mahaifiyarsa wadda tsohuwar malamar makaranta ce ta ci gaba da ɗaukar nauyin karatunsa tun daga lokacin. Rahotanni sun nuna cewa matsalarsa ta ƙara tsananta tun bayan dawowarsa makaranta a bara, inda abokan karatunsa suka tara kuɗi domin biya masa kuɗin makaranta da kuma siya masa kayan abinci. Duk da cewa jami’ar ba ta fitar da sanarwa a hukumance ba, amma wani babban jami’i a makarantar, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya tabbatar da faruwar lamarin a ranar Talata, yana mai bayyana hakan a matsayin abin mamaki da ya jefa jami’ar cikin jimami.
A yayin da farashin buhu daya na danyar citta da ke a matsayin iri ya yi tashin gwauron zabon da ba a taɓa ganin irin sa ba, inda ake sayar da shi a kan Naira 210,000 kowane buhu, shi kuwa busasshen buhun citta ana sayar da shi ne daga Naira dubu 500,000 zuwa Naira 550,000 a yankin Kudancin Jihar Kaduna da aka fi noman ta a Nijeriya. Hakan ba ya rasa nasaba da matsalar kwayoyin cutar da suka lahanta mafi yawan cittar da aka noma a 2024, wanda ya yi sanadiyyar karancin irin cittan da kuma hauhawar farashin taki da magunguna da sauran ayyukan noman cittar. Hausawa sun yi bikin cika shekara 153 da zama a garin Owerri DAGA LARABA:...
Jaridar Politico ta buga wani rahoton dake cewa sojojin kasar Ukiraniya suna fuskantar matsin lamba mai yawa, da kuma rashin kwararrun mayaka. Wannan matsin lambar da sojojin kasar suke fuskanta ya sa ana tunanin mayar da sojojin sama zuwa na kasa da tura su filin daga. Har ila yau jaridar ta ambaci yadda sojojin da suke guduwa daga filin yaki suna karuwa. Jaridar ta kuma kara da cewa; Babban hafsan hafsoshin kasar ta Ukiraniya ya bayar da umarnin a dauki sojojin sama 5000 a mayar da su na kasa. Da akwai tsoron cewa kasar ta Ukiraniya tana rashin kwararrun sojojinta, da ba za ta iya maye gurbinsu a cikin sauki ba idan har aka tura su zuwa filin daga. A...
Rahotanni sun ambaci cewa bayan ficewar sojan Faransa na karshe daga sansanin Abaci dake gabacin kasar Chadi,kasar Turkiya tana shirin maye gurbinta. Wata majiyar kasar Turkiya ta shaidawa wata kafar labaru ta Afirka cewa, Ankara tana shirin girke jiragen yaki marasa matuki a cikin sansanin dake kan iyaka da kasar Libya akokarin da take yi na cike gurbin da Faransa ta bari, da zummar tabbatar da kanta a cikin wanann yankin na Afirka. Gwamnatin Chadi ta bai wa Turkiya sansanin na Abaci a karkashin yarjejeniyar da kasashen biyu su ka cimmawa a tsakiyar watan da ya gabata,bayan doguwar tattaunawa da aka yi a tsakanin jami’an gwmanatocin kasashen biyu. Haka nan kuma rahoton ya ce, kasar Turkiya ta bai wa gwamnatin...
Kungiyar kare hakkin bil’adama ta “Amnesty International” ta kira yi Amurka da ta kama Fira ministan “Isra’ila” Benjamin Netanyahu da yake ziyarar aiki a kasar. A wasu jerin sakwanni da kungiyar ta kare hakkin bil’adama ta duniya ta wallafa a shafinta na X, ta bayyana cewa; Yadda Amurka ta karbi bakuncin Benjamin Netanyahu alhali ana zarginsa da manyan laifuka, yana nuni da cewa ta raina kotun ta kasa da kasa. Har ila yau kungiyar kare hakkin bil’adama ta kasa da kasa ta kuma kara da cewa; Gwamnatin da ta gabata ta Amurka a karkashin Joe Biden ta yi watsi da duk wani yunkuri na shimfida adalci a duniya, kuma shi ma shugaba Trump abinda yake yi kenan a yanzu. Wannan...
Kungiyar Hizbullah ta fitar da wani bayani a jiya Talata da ta yi Allawadai da takuhkumin da kasar Australia ta kakaba wa babban sakatarenta Sheikh Na’im Kassim. Bayanin na kungiyar Hizbullah ya kunshi cewa; Matakin, yana sake nuni ne da hakikanin fuskar wannan kasa da a kowace rana take tabbatar da cewa, ita makami a hannun Amurka da Isra’ila. Hizbullah ta kuma bayyana matakin da cewa na zalunci ne wanda bai jingina da kowane irin dalili na shari’a da halayyar kwarai ba, yana nuni ne kai tsaye da cewa; Suna goyon bayan HKI ne da kuma kare laifukan da take tafkawa da ta’addancinta, tare da yin kira cewa kamata a yi ace kasar ta Australia da ta dauki matakai ne...
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba A da akan kwashe kwanaki ana bukukuwan aure a ƙasar Hausa, kama daga kamu, zuwa sa lalle, yinin biki da zaman ajo zuwa buɗar kai da sayen baki. Sai dai waɗannan al’adu sannu a hankali suna ta gushewa. Ko mene ne dalilin wannan sauyin? NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Noma Ba Tare Da Kashe Kuɗi Da Yawa Ba DAGA LARABA: Dalilan Da Mutane Suke Son Haihuwar Maza Fiye Da Mata Wannan ne batun da shirin Daga Laraba zai duba a wannan makon. Domin sauke shirin, latsa nan
Hukumar kula da aikin Hajji ta kasa NAHCON ta sanar da a ci gaba da yi wa maniyyata rajista har zuwa ranar Litinin 10 ga watan Fabrairu, 2025. A daren Talata 4 ga watan ne hukumar ta amince da kara lokacin a taron da ta yi da shugabannin hukumomin alhazai na jihohi. Wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar Jin Dadin Alhazzai ta Jihar Kaduna Yunusa Mohammed Abdullahi ya fitar, ya ce shugaban hukumar Malam Salihu S. Abubakar ya yi kira ga maniyyatan jihar ta Kaduna da su yi amfani da wannan damar wajen yin rajista ta hanyar tuntubar jami’anmu da ke kananan hukumomi don su cika kudadensu, ko karbar sabuwar telar banki don su biya kafin a...
Kungiyar masu fama da cutar daji ta Najeriya reshen jihar Kano, ta yi kira ga gwamnatin jihar da ta bullo da tallafin kula da cutar a dukkan asibitocin gwamnati. Shugaban kungiyar Salisu Yusuf ne ya yi wannan kira a yayin wani taron manema labarai na bikin ranar cutar Daji ta duniya tta shekarar 025. Ya bukaci gwamnati da ta hada gwajin cutar Kansa, da jiyya, da kula da lafiyar jiki a cikin shirinta na ba da tallafin iwon lafiya. Acewarsa matakin zai rage wa majinyata matsalar kudi, musamman wadanda suka fito daga iyalai masu karamin karfi. Bugu da kari, kungiyar ta bukaci da a saka masu fama da cutar ta Daji da wadanda suka warke daga cutar a cikin shirin...
Masana kimiyyar kasar Sin sun kirkiro wani sabon samfurin kirkirarriyar basira ta fasahar AI domin yin hasashen zuwan mahaukaciyar guguwa, wanda hakan ya ba da sabuwar fa’ida da kara haskaka hanyoyin inganta shirin tunkarar bala’o’i a duniya. A kwanan baya, masu bincike daga cibiyar nazarin teku a kwalejin kimiyya ta kasar Sin sun wallafa wannan binciken a cikin mujallar da ke wallafa harkokin kimiyya ta kasar Amurka, watau “Proceedings of the National Academy of Sciences.” (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)
Rundunar ‘Yan Sanda a Jihar Kebbi, ta kama wasu bakin haure 165 tare da mika su ga hukumar kula da shige da fice ta kasa shiyar jihar domin gudanar da bincike. A wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, SP Nafiu Abubakar ya fitar kuma ya mikawa gidan rediyon Najeriya a jihar Kebbi, ya ce, bisa rahoton bayanan sirri, an gano sama da mutum dari biyu a wani katafaren gida mai dakuna uku da ke unguwar Kuwait a cikin birnin Birnin Kebbi. Sanarwar ta ce, tawagar jami’an ‘yan sanda da ke sashin binciken manyan laifuka (SCID) ce ta kai samame unguwar, inda suka yi nasarar cafke mutane dari da sittin da biyar (165). Ya bayyana cewa,...
Shugaban Majalisar Wakilai Dr Abbas Tajuddeen, ya bayyana kaduwarsa bisa rasuwar fitaccen dan kasuwa kuma mai taimakon jama’a, Alhaji Bala Abdulwahab da ke Zariya, wanda aka fi sani da Albabello. A wata sanarwa da mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yada labarai Malam Musa Abdullahi Krishi ya fitar, Dakta Abbas Tajuddeen, ya ce masarautar Zazzau da jihar Kaduna sun yi rashin babban dan kasuwa wanda ya sadaukar da rayuwarsa gaba daya wajen yi wa al’umma hidima. Shugaban majalisar ya jaddada cewa, Albabello, ta hanyar sahihancinsa na kasuwanci, ya samar da ayyukan yi ga dubban jama’a a Zariya da ma fadin kasar nan, ta hanyar amfani da rassan kamfaninsa daban-daban. Ya ci gaba da cewa Albabello, ya kuma...
Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi II, ya yi kira da zauna lafiya kuma a bai wa zukata haƙuri biyo bayan ƙazamin rikicin mallakar fili da aka yi tsakanin mazauna da kuma Jami’ar Bayero da ke Kanon. Sarkin ya yi wannan kira ne yayin da ziyarci unguwar Rimin Auzinawa da Rimin Zakara da ke Ƙaramar Hukumar Ungogo a ranar Talatar nan, inda ya jajanta wa iyalan waɗanda lamarin ya rutsa da su. Za a kashe Naira biliyan 4.8 wajen yaƙi da cutar HIV a Nijeriya — Ministan Lafiya Ma’auratan da aurensu ya mutu sau 12 a shekara 43 “Dole ne mu yi wa waɗanda suka rasu a addu’a sannan mu jajanta wa iyalan waɗanda lamarin ya shafa. Muna fatan wannan...
Ministan ya kara da cewa, za a kaddamar da kashin farko na gyaran madatsar ruwan a tsakanin watan Fabrairu zuwa Yulin 2025. Ya kuma kara jaddada muhimmancin wannan aiki na tabbatar da cewa ba a samu ambaliyar ruwa a jihar Borno a shekarar 2025 ba.
Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya soki ’yan siyasar da ke sukar gwamnatin Shugaban Bola Tinubu da cewa suna yi ne kawai domin neman mulki. Uba Sani ya bayyana cewa ’yan siyasar da ke yawan sukan Tinubu a baya-bayan nan ba su da wani abin da za magance matsalolin Najeriyar da suke suka shugaban kasan a kai. Ya kara da cewa masu sukan Tinubun su ne suke ta yabon shugaban kasar, amma yanzu da mulki ya bar hannunsu suka dawo suna zagin sa. A cewarsa, babu mutum daya a cikin taron masu kushe Tinubun da ke da nagartar da ta fi shugaban kasar, yana mai jaddada cewa Tinubu ya yi yaki kai da fata kuma har yanzu yana kare muradun...
Babban wakilin kasar Sin a MDD Fu Cong, ya gudanar da taron manema labarai a hedkwatar MDD dake birnin New York, jiya Litinin bisa agogon birnin, domin gabatar da muhimman tsare-tsare na wa’adin shugabancin kasar Sin a kwamitin sulhu, na wannan wata. A cewar Fu Cong, a yayin wa’adin shugabancin kwamitin sulhu na MDD a watan nan, kasar Sin za ta mai da hankali kan ra’ayoyin bangarori daban-daban da gudanar da tsarin mulkin duniya, da kula da halin da ake ciki a yankin Gabas ta Tsakiya da kuma yanayin da ake ciki a wasu kasashen Afirka. Da aka tambaye shi game da samfurin kirkirarriyar basira ta DeepSeek, wanda wani kamfanin kula da fasahohin kirkirarriyar basira na kasar Sin ya fitar,...
Majalisar Zartarwa ta ware naira biliyan 4.8 domin yaƙi da yaɗuwar cutar HIV a Nijeriya. Wannan na daga cikin matsayar da aka cimma a taron Majalisar Zartarwa da ya gudana a ranar Litinin kamar yadda Ministan Lafiya, Farfesa Muhammad Ali Pate ya tabbatar. Ma’auratan da aurensu ya mutu sau 12 a shekara 43 Dalilin da Tinubu ya ƙi amincewa da ƙudirin kafa Jami’ar Ilimi a Adamawa Ministan ya ce wannan yana daga cikin manufofin gwamnatin na inganta kiwon lafiya a matakin farko. A cewarsa, an tsara kashe kuɗaɗen ne a fannin ɗaukar ma’aikatan lafiya da ba su horo domin samun ƙwarewa da kuma tabbatar da an bayar da kulawar da ta dace domin hana yaɗuwar cutar HIV a sassan ƙasar....
Haruna, mazaunin Unguwar Kanawa Dutse Abba, an rahoto cewa, ya jagoranci ‘yan bindiga uku – Shago Yaro, Tanimu Ayuba, da kuma Lamido Dantajiri zuwa gidan dansa, Alhaji Anas da misalin karfe 1 na dare, inda suka tarar ba ya gida, amma suka yi awon gaba da matansa biyu, ‘ya’yansa uku, kaninsa, da matar kaninsa. An tsare Iyalin har tsawon kwanaki 60 a tsakanin dajin Buruku da Sabo Birni. Da yake tabbatar da rawar da ya taka a wannan aika-aika, Haruna ya ce, “Ni manomi ne kuma dan banga. Gaskiya ni ne na kai ‘yan bindiga gidan Alhaji Anas. Anas dana ne – dan yayata. Na san daya daga cikin ‘yan fashin da ya ce in nuna musu gidan...
Gwamnatin Jihar Jigawa ta ce za ta karfafa kyakkyawar alakar da ke tsakaninta da asusun horar da ma’aikata ITF. Shugaban ma’aikata na jihar Alhaji Muhammad K Dagaceri ya bayyana haka a lokacin da ya karbi bakuncin shugaban asusun horas da ma’aikata na yankin arewa maso yamma, Malam Aminu Abdu a ofishinsa. A cewarsa, gwamnatin jihar tana sane da muhimmancin da asusun ke da shi, musamman ga ma’aikatan da aka horas da su domin samun kwarewa a fanninsu. Dagaceri, ya tabbatar wa shugaban asusun cewa, gwamnatin jihar za ta ci gaba da bayar da dukkan goyon baya da hadin kai ga sabon ofishin na ITF da aka kafa a yankin Jigawa. Tun da farko, Shugaban Asusun na Arewa maso...
An shawarci gwamnonin jihohin Arewa da su yi koyi da gwamnatin jihar Neja wajen magance matsalolin rikicin makiyaya da manoma a yankin domin samun ci gaba mai dorewa. Shugaban kungiyar Miyetti Allah ta kasa MACBAN, Dokta Baba Usman Ngelzarman ne ya bayar da wannan shawarar a wajen wani taro na musamman na karramawa tare da tabbatar da lakabin gargajiya ga wasu fitattun Fulani guda biyu a jihar Neja, da aka gudanar a fadar Sarkin Minna. Dokta Baba Usman Ngelzarman ya bayyana cewa, hanyar da Gwamna Mohammed Umar Bago na Jihar Neja ya bi na samar da sakamako mai kyau, ta yadda za a rage yawan rikicin makiyaya da manoma a jihar abin a yaba ne matuka. A cewarsa hakan ya...
Daminar Bana: NiMet Ta Yi Hasashen Jinkirin Saukar Ruwan Sama A Jihohin Arewa
Babban mai ba da shawara kan harkokin siyasa ga Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran ya jaddada cewa Iran za ta yi amfani da dukkan karfinta wajen kare shirinta na nukiliya cikin lumana. A yayin wata ziyara da ya kai wani baje kolin da ke nuna sabbin nasarorin da aka samu a masana’antar nukiliya a hukumar makamashin nukiliya ta Iran (AEOI) a ranar Litinin din nan, Ali Shamkhani ya sake nanata gaskiyar shirin nukiliyar Iran da kuma yadda kasar ke bin ka’idojin kasa da kasa. “Iran ba ta taba neman makaman nukiliya ba kuma ba za ta taba yin hakan ba,” in ji shi. “Duk da haka, tana kare hakkinta da dukkan karfinta.” Shamkhani ya ci gaba da cewa:...
Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas, ta sanar da fara shawarwarin tsagaita wuta a mataki na biyu tsakaninta da Isra’ila. Kakakin Abdul Latif al-Qanou ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da ya fitar a kafar sadarwar zamani. A cikin wata sanarwa da ta fitar a tashar ta Telegram mai magana da yawun kungiyar Abdel Latif al-Qanoua ya zargi Isra’ila da “jinkirta aiwatar da ka’idojin jinƙai a yarjejeniyar tsagaita wuta da kuma dakatar da aiwatar da hukuncin kisa.” Ya ce har yanzu kungiyar Falasdinu ta damu da batutuwa da dama da suka hada da matsuguni ga mutanen Gaza, da kuma kayan agaji da kuma kokarin sake gina yankin. Al-Qanou ya kuma zargi Isra’ila da “katse” ka’idojin jin kai da ke...
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Labanon ta shigar da sabon korafi kan yahudawan sahyuniya gaban kwamitin sulhu na MDD, inda ta yi Allah wadai da hare-haren baya-bayan nan da yahudawan sahyuniya suka kai kan kasar Labanon, da kuma keta hurimun ikon kasar, da keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta da aka cimma yau fiye da watanni biyu. Wannan korafin, wanda aka mika ta hannun wakilcin Dindindin na Labanon a Majalisar Dinkin Duniya a birnin New York, ya jibanci yadda Isra’ila ta ci gaba da keta yarjejeniyar tun daga ranar 27 ga Nuwamba, 2024 ranar da tsagaita bude wuta ta fara aiki har zuwa yau Talata 4 ga Fabrairu. Lebanon Ta yi Allah wadai da ci gaba da kai hare-hare ta kasa da...
Sakamakon sanarwar da Amurka ta fitar kwanan baya a kan kara haraji na kashi 10 cikin dari a kan daukacin kayayyakin kasar Sin da ake kaiwa kasar tare da kafa hujja da wasu batutuwa irin su maganin Fentanyl, a yau Talata, ma’aikatar cinikayya da takwararta ta kudi ta kasar Sin sun fitar da wata sanarwa cewa, Sin ta dauki matakan mayar da martani a kan Amurka tare da fara aiwatarwa. Matakan da suka jibanci lamarin sun hada da cewa, da farko, kasar Sin za ta sanya harajin kashi 10% zuwa 15% kan wasu kayayyakin da ake shigowa da su daga Amurka, daga ranar 10 ga Fabrairu. Sannan na biyu, kasar Sin ta yanke shawarar shigar da rukunin kamfanonin US PVH...
Da yake tabbatar da harin, wani mazaunin T/wada Garmadi, Rumaya Kwassam, Mista Joel Ahada, ya yi Allah wadai da wannan danyen aikin, yana mai bayyana hakan a matsayin rashin mutunta hakkin dan Adam da kare lafiyar mazauna karkara. Kokarin jin ta bakin jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar Kaduna, DSP Mansir Hassan, ya ci tura har zuwa lokacin hada wannan rahoto.
Wasu ma’aurata ’yan kasar Australia da suka yi aure kuma suka sake rabuwa da juna har sau 12 a cikin shekaru 43 da suka gabata, a yanzu ana gudanar da bincike a kan zargin zamba tsakaninsu. ’Yan sanda a birnin Vienna na kasar Australia a halin yanzu suna gudanar da bincike a kan wani lamari mai ban mamaki, inda wasu ma’aurata da suka yi aure sannan suka rabu har sau 12 a tsawon shekaru 43, domin yin amfani da wata doka da ta ba su damar karbar makudan kudade. Dalilin da Tinubu ya ƙi amincewa da ƙudirin kafa Jami’ar Ilimi a Adamawa Don namen mulki ’yan siyasa ke sukan Tinubu —Gwamnan Kaduna Ana zargin tsofaffin ma’auratan da laifin kitsa kowace...
Shugaba Bola Tinubu ya ƙi rattaba hannu kan ƙudirin kafa Jami’ar Ilimi ta Tarayya a Numan da ke Jihar Adamawa. Hakan na ƙunshe cikin wata wasiƙa da ya aike wa Kakakin Majalisar Wakilai, Tajuddeen Abbas wadda mataimakinsa, Benjamin Kalu ya karanta a yayin zaman majalisar na yau Talata. Alakarmu da El-Rufai na nan babu matsala —Uba Sani HOTUNA: Hatsarin tirela ya yi ajalin mutum 4, shanu 15 da awaki 20 a Neja Wasiƙar shugaban ta kare matakin da ya ɗauka na ƙin amincewa bisa la’akari da tanadin da sashe na 22 da ke cikin ƙudirin kafa jami’ar ya yi. Ya yi bayanin cewa sashen ya yi tanadin cewa filin da za a gina jami’ar zai kasance a ƙarƙashin ikon Gwamnatin...
Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya soki ’yan siyasar da ke sukar gwamnatin Shugaban Bola Tinubu da cewa suna yi ne kawai domin neman mulki. Uba Sani ya bayyana cewa ’yan siyasar da ke yawan sukan Tinubu a baya-bayan nan ba su da wani abin da za magance matsalolin Najeriyar da suke suka shugaban kasan a kai. Ya kara da cewa masu sukan Tinubun su ne suke ta yabon shugaban kasar, amma yanzu da mulki ya bar hannunsu suka dawo suna zagin sa. A cewarsa, babu mutum daya a cikin taron masu kushe Tinubun da ke da nagartar da ta fi shugaban kasar, yana mai jaddada cewa Tinubu ya yi yaki kai da fata kuma har yanzu yana kare muradun...
Gwamna Uba Sani na Jihar Kaduna, ya ce babu wata matsala tsakaninsa da tsohon uban gidansa kuma magabacinsa Malam Nasir El-Rufai. Uba sani ya ce babu kamshin gaskiya a maganganun da ke yawa cewa shi da tsohon gwamnan El-Rufai suna zaman doya da manja. Ya bayyana haka ne a yayin hirar da kafar tala bijin ta TVC ta yi da shi a ranar Litinin, inda ya ce “alakarmu tana nan yadda ta ke, babu wata matsala, kamar yadda ake rade-radi.” Am fara tunanin cewa dangantaka ta yi tsami tsakanin Uba da El-Rufai ne bayan da gwamnati mai cin ya yi zargin Gwamnatin El-Rufai da barin masa bashin biliyoyin Naira da kuma karkatar da wasu kudade. Yau Majalisar za ta ci...
Kafafen watsa labarun HKI sun ambaci cewa, an kashe sojoji 2 a yankin kusa da Tubas dake Arewacin yammacin kogin Jordan. Kafafen watsa labarun sun kuma ce, maharin ya isa wani shinge na soja dake kusa da Tayasir, ya kuma boye a cikin hasumiyar da masu tsaro ke zama a ciki, sannan ya bude wa sojoji wuta daga sama. Har ila yau maharin ya yi bata-kashi da sojojin da suke a wajen, sai dai a karshe sun ci karfinsa, da hakan ya yi shahadarsa. A bayanin da kungiyar Hamas ta fitar ta jininawa maharin tare da cewa, abinda hakan yake nufi shi ne cewa hare-haren da ‘yan sahayoniya suke kai wa ba za su tafi haka kawai ba tare da...

Jeremy Corbyn Ya Bukaci Ganin An Hukunta Isra’ila Da Masu Ba Ta Makamai Akan Kisan Kiyashin Falasdinawa
Tsohon shugaban jam’iyyar “ Labour” ta Birtaniya Jeremy Corbyn ya yi kira da a hukunta Isra’ila, da masu daukar nauyinta akan kisan kiyashin da ta yi tun bayan ranar 7 ga watan Okotoba 2023. Cobyn ya rubuta a shafinsa na X cewa; A cikin bayan nan ne zurfin barnar da Isra’ila ta yi, yake kara bayyana, don haka wajibi ne jami’anta su fuskanci shari’a akan kowane rai daya da aka yi asararsa. Cobyn ya ci gaba da cewa; Duk wanda ma ya rika aikewa da makamai yana sane da cewa za a yi amfani da su a yi kisan kiyashi, shi ma a hukunta shi.” A cikin watanni shida da su ka gabata Birtaniya ta sayar wa da HKI makamai...
Ministocin harkokin wajen 5 na kasashen larabawa tare da hadin gwiwar jami’an Falasdinawa sun rubuta wa ministan harkokin wajen Amurka Marco Antonio Rubio wasiki da a ciki suke nuna kin amincewa da shirin korar Falasdinawa zuwa wajen Falasdinu. Kasashen da su ka rubuta wasikar sun kunshi Saudiyya, HDL, Katar, Masar da Jordan, sai kuma mai bai wa shugaban gwamnatin Falasdinu shawara Husain Sheikh, sun kuma mika wannan wasikar ne ga mataimakin ministan harkokin wajen kasar ta Amurka mai kula da yankin gabas mai nisa. A ranar 25 ga watan Janairu da ya shude, shugaban kasar Amurka ya gabatar da shawarar cewa kasashen Masar da Jordan su karbi bakuncin Falasdinawa daga Gaza. Tare da cewa Trump din ya ce zaman na...
Gwamnan Kaduna Ɗan Amshin Shata Ne Ga Tinubu Saboda Tallafin ₦150bn — El-Rufai

Kungiyar Hamas Ta Bayyana Cewa A Shirye Take Ta Fara Tattaunawa, Marhala Ta Biyu Na Tsagaita Wuta A Gaza
Kungiyar Hamas wacce take iko da yanin zirin gaza ta bada sanarwan cewa a shirye take, masu shiga tsakanin, wato kasar Masar ta fara tattaunawa marhala ta biyu na tattaunawar tsagaita wuta a Gaza. Tashar talabijin ta Almayadeen ta kasar Lebanon ta nakalto kamfanin dillancin laran AFP na kasar Faransa yana fadar haka. Ya kuma kara da cewa, wani jami’in kungiyar wanda baya son a bayyana sunansa ya ce kungiyar a shirye take a fara tattaunawar.. A wannan tattaunawa dai ana saran za’a fayyace filla-filla kan yadda al-amura zasu kasance a nan gaba a zirin gaza. Labarin ya kara da cewa jami’an Hamas sun bayyana haka ne a ranar da aka yi musayar fursinoni da HKI a garin Khan Yunus....
Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Aston Villa ta kammala ɗaukar tsohon ɗan wasan Real Madrid Marco Asensio daga ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta PSG a matsayin aro zuwa ƙarshen kakar wasa ta bana. Asensio wanda ya bar Real Madrid a shekarar 2023 ya na ɗaya daga matasan ƴan wasa da tauraruwarsu ke haskawa a harkar ƙwallon ƙafa a yanzu. PSG Na Neman Dauko Lamine Yamal Daga Barcelona A Kan Yuro Miliyan 200 Wannan Ita Ce Shekarata Ta Karshe A PSG —Mbappe Aston Villa ta wallafa a shafinta na kafar sadarwa cewa Asensio ya rattaɓa hannun komawa ƙungiyar a matsayin aro daga PSG har zuwa ƙarshen kakar wasa ta bana. Asensio ne ɗan wasa na biyu da Villa ta ɗauka aro bayan Marcus...

Sojojin Iran Sun Fara Atisayen Soje Karu Na Biyu Mafi Yawa A Bangaren Garkuwan Sararin Samaniyar Kasar
Sojojin JMI sun bada sanarwan fara isayen soje karo na biyu a yankun tsakiya da kuma kudancin kasarTashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa za’a fara wannan atisayen ne a yau Talata 04 ga watan Fabrairu, kuma atisayen zai fi maida hankali ne a kan garkuwan tsaron kasar , wanda kuma ya kasance daga cikin shirye-shiryen kasar na shirin kare sararin samaniyar kasar ta sama. Labarin ya kara da cewa a wannan karom ma sojojin Iran da kuma dakarun juyin juya halin musulunci zasu yi atisayen hadin giwa ne don gwada karfin sojojin kasar da kuma IRGC na kare sararin samaniyar kasar. Kafin haka dai sojojin sun gwada karfinsu a bangarori daban daban na sojojin kasar don...

Wani Tsohon Ma’aikacin MDD Ya Yi Kira Ga Amurkawa Su Dawo Daga Rakiyar Gwamnatin Amurka Da Natanyahu
Tshohon daractan hukumar kare hakkin bil’ada ta MDD Craig Mokhiber ya yi kira ga Amurkawa su dawo daga rakiyar gwamnatin Trump da kuma firai ministan HKI Benyamin Natanyahu, mashayin jinin Falasdiwa, a dai dai lokacinda yake ziyararsa ta farko zuwa kasar Amurka tun bayan da Trump ya sake dawowa fadar White House. Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Craig Mokhiber ya na fadar haka a shafinsa na X a jiya litinin, ya kuma kara da cewa, irin tarban da gwamnatin Trump ta bawa Natanyahu, da kuma yadda wasu yan majalisar dokokin kasar suka himmatu, ya nuna cewa babu bambanci a tsakanin gwamnatin Joe Biden da kuma Trump idan an yi maganar dangantar Amurka da HKI. Yace dukaninsu...
HKI tana son aiwatar da wani shiri don kara yawan yahudawa a kasar, a dai dai lokacinda take fama da karancin yahudawa a kasar. Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta ce a baya dai gwamnatin yahudawan suna son kara yawan yahudawa musamman a yankin yamma da kogin Jordan, ammam har yanzun shirin baya tafiyar kamar yadda take so. Labarin ya kara da cewa yawan Palasdinawa a cikin kasar Palasdinu da aka mamaye wata barazana ce babba ga gwamnatin kasar. Banda haka a cikin yakin watanni 15 da ta fafata da Mutanen yankin Gaza, wasu yahudawa sun fice daga kasar kuma da dama daga cikinsu sun sha alwashin ba za su sake dawowa kasarba. Wasu kuma sun kai...
Babbar Kotun Jihar Kano ta yanke wa wasu mutum biyar hukuncin kisa ta hanyar rataya saboda laifin lashe wata dattijuwa mai shekara 67, kan zargin ta da maita. Kotun ya yanke musu hukuncin kisa ne a ranar Litinin bayan samun su da laifin kiran dattijuwar mai suna Ɗahare Abubakar, mayya sannan suka daɓa mata wuka har lahira. Mai Shari’a Usman Maido, ya bayyana cewa masu gabatar da ka to sun gabatar da gamsassun hujjoji da suka tabbatar da laifin wadanda aka gurfanar. Waɗanda kana yanke wa hukuncin kisan su ne Da’luta Ibrahim, Abdulaziz Yahaya, Faisal Yahaya, Ibrahim Abdu da Ayuba Abdulrahman. Mai gari ya tsere bayan mazauna sun cinna wa gidansa wuta a Kano Rikicin rusau ya yi ajalin mutum...
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba Mutanen da ke da sha’awar shiga harkar noma don sama wa kansu abin da za su ci ko kuma don samun kuɗaɗen shiga na fuskantar ƙalubale. Wannan ƙalubale ya haɗa da ƙarancin ilimin noman, da na irin shuka, da rashin gonaki da dai sauran su. NAJERIYA A YAU: Dalilin Da Za Mu Kashe Biliyan N2.5 Kan Auren Zawarawa —Gwamnatin Kano DAGA LARABA: Dalilan Da Mutane Suke Son Haihuwar Maza Fiye Da Mata Shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan wannan batu tare da samar da hanyoyin noma ba tare da kashe kuɗi masu yawa ba. Domin sauke shirin, latsa nan
An yi kiyasin adadin tafiye-tafiyen fasinjoji tsakanin yankuna zai kai biliyan 4.8 a duk fadin kasar Sin daga ranar 14 ga watan Janairu zuwa ta 2 ga watan Febrairu, wato rabin farko na kwanaki 40 na zirga-zirgar bikin bazara. Adadin ya nuna karuwar kashi 7.2 cikin dari bisa makamancin lokaci na bara, a cewar tawagar aiki ta musamman da aka kafa don saukake ayyukan da suka shafi zirga-zirgar bikin bazara, wanda aka fi sani da chunyun. Hukumar FCTA Ta Rufe Asibitin Da Ke Aiki Ba Bisa Ka’ida Ba A Kuje Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Athletico Madrid Da Getafe Zirga-zirgar fasinjoji ya karu tun daga ranar 30 ga watan Janairu, inda adadin tafiye-tafiyen ya zarce miliyan 300 a...