2025-02-21@14:24:10 GMT
إجمالي نتائج البحث: 762
«dala biliyan»:
(اخبار جدید در صفحه یک)
Kamfanin kula da sufurin layin dogo na kasar Sin, ya ce jarin manyan kadarori da kasar ta zuba a bangaren layin dogo ya kai yuan biliyan 43.9, kwatankwacin dala biliyan 6.12, a watan Janairun bana. A cewar kamfanin, adadin ya karu da kaso 3.7 bisa dari idan aka kwatantan da makamancin lokacin a bara. A wannan lokaci, an gudanar da manyan ayyuka, ciki har inganta layin dogo mai saurin tafiya tsakanin biranen Chengdu da Chongqing. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya rantsar da sabon Sakataren Gwamnatin Kano, Umar Farouk Ibrahim. An dai rantsar da sabon Sakataren Gwamnatin ne a wani ƙwarya-ƙwaryan biki da aka gudanar ofishin gwamnan. ’Yan bindiga sun kashe fasto a Gombe An shiga nuna wa juna yatsa tsakanin Hamas da Isra’ila Aminiya ta ruwaito cewa, Kwamishinan Shari’a kuma Babban Lauyan Gwamnatin Kano, Barista Haruna Isa Dederi ne ya ba shi rantsuwar kama aikin. Naɗin sabon Sakataren Gwamnatin na zuwa ne watanni biyu bayan sauke Dokta Abdullahi Baffa Bichi daga muƙamin da wasu kwamishinoni 5 da shugaban Ma’aikatan Fadar Gwamnan. Wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan na Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ta ce an zaɓi sabon Sakataren Gwamnatin ne...
’Yan bindiga sun kashe wani fasto, Rabaran Bala Galadima yayin harin da suka kai garin Lubo da ke Ƙaramar Hukumar Yamaltu Deba a Jihar Gombe. Aminiya ta ruwaito cewa, ’yan bindigar sun kuma yi fashin kuɗi har Naira dubu 300 a yayin harin da suka kai cikin dare wayewar gari Lahadi. Wani mazaunin garin ya bayyana cewa maharan, waɗanda sun kai takwas, sun kai farmakin ne da misalin karfe 1 zuwa 3 na dare, inda suka firgita jama’a da harbe-harbe kafin su kutsa cikin gidan wani mutum mai suna Musa Puma. Majiyar ta ce maharan sun rutsa matar gidan da bindiga inda suka karbi kuɗi naira dubu dari 300 tare da yin garkuwa da ɗaya daga cikin ’ya’yansu da kuma...
Sama Da Masu Amfani Da Kayayyakin Laturoni Miliyan 20 Ne Suka Nemi Tallafin Musayar Kayan Laturoni
Hamas ta sanar da yanke shawarar jinkirta sakin fursunonin Isra’ila nan gaba har sai abin da hali ya yi. Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da ƙungiyar gwagwarmaya ta Falasɗinu ta fitar tana mai cewa an ɗauki matakin ne a matsayin mayar da martani ga keta yarjejeniyar tsagaita wuta da Isra’ila ta yi. Dalilin da na ziyarci Obasanjo — Atiku Gwamnan Zamfara ya gindaya sharaɗin sulhu da ’yan bindiga Sanarwar da ɓangaren sojin Hamas ɗin ya fitar ta ce “fiye da mako uku, shugabacin ƙungiyar na bibiyar yadda maƙiya suka gaza cika ka’idojin yarjejeniyar da suka cimma. “Karya wannan ƙa’ida, har da jinkirta dawowar waɗanda suka rasa muhallansu zuwa Arewacin Gaza, inda ake fakon su tare da harbin su, da...
A yau Litinin, kasar Sin ta sanar da sabbin ka’idojin kyautata kare sirrikan jama’a yayin kare tsaron al’umma. Firaministan kasar Sin Li Qiang ne ya rattaba hannu kan wata dokar majalisar gudanarwar kasar, domin fitar da ka’idojin, wadanda za su fara aiki daga ranar 1 ga watan Afrilu. Ka’idojin na da nufin tafiyar da harkokin da suka shafi kula da tsare-tsaren kyamarorin da aka kafa domin tsaron al’umma da kare sirrika da hakkoki da muradu da ma bayanan daidaikun mutane. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)
3. Wallafa labarin a kasan wannan sanarwar a ɓangaren tsokaci. 4. Wallafa labarin a shafinka na sada zumunta na facebook tare da makala #tak na #GasarLabarunSoyayya #LeadershipHausa #GasarLeadership 5. A kiyaye ƙa’idojin Rubutun Hausa da kuma amfani da daidaitacciyar Hausa da aka amince a yi amfani da ita a hukumance. 6. Ka tabbatar ka sanya lambar wayarka da sanya adireshinka na Imel a kasan labarin da ka kawo, ka kuma turo mana ta Imel dinmu na: [email protected] Za a rufe karɓar gajerun labaran a ranar Alhamis mai zuwa 13/02/2025 da karfe 12, na rana.
Sai dai yadda gwamnatin Trump ta sanar da rufe USAID ya ba da damar tona asirinta, kuma tabbas tarihi zai tabbatar da cewa, gaskiya na hannun wadanda ke kokarin samar da ci gaba da kiyaye hadin gwiwar cin moriyar juna da ma wadanda ke kokarin tabbatar da makomar dan Adam ta bai daya.
Tsohon Mataimakin Shugaban Nijeriya, Atiku Abubakar, ya bayyana dalilin ziyarar da ya kai wa tsohon Shugaban Kasa Olusegun Obasanjo a wannan Litinin ɗin. Aminiya ta ruwaito cewa, da misalin ƙarfe 12:36 na yau Litinin ce tawagar da Atikun ya jagoranta ta isa gidan tsohon Shugaban Ƙasar da ke Abeokuta, babban birnin Jihar Ogun. Gwamnan Zamfara ya gindaya sharaɗin sulhu da ’yan bindiga Gwamna Sule ya naɗa Kwamishinoni 16 a Nasarawa Tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya samu rakiyar tsohon gwamnan Jihar Kuros Riba, Liyel Imoke da takwaransa na Sakkwato, Sanata Aminu Tambuwal haɗi da ɗan Majalisar Dattawa mai wakiltar Bauchi ta Tsakiya, Sanata Abdul Ningi. Bayanai sun ce an shafe tsawon sa’a ɗaya da rabi ana ganawar wadda aka yi ta...
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa, kasar Iran ba zata taba zama don tattaunawa da kasar Amurka ba a dai-dai lokacin take kara takurawa kasar da takunkuman tattalin arziki ba. Tashar talabijin ta Presstva nan Tehran ta nakalto ministan yana fadar haka bikin ciki shekaru 46 da samun nasarar juyin juya halin musulunci a kasar a yau litinin, a birnin Hamedan. Imam Khumaini (q) ne ya jagoranci kasar zuwa ga nasara a shekara 1979, Juyin juya halin da ya kawo karshen Sarautar Muhammad Reza sha Pahlavi. Ministan ya kara da cewa Jagoran juyin juya halin musulunci ya rika ya bayyana matsayin gwamnatin kasar Iran kan wannan batun, sannan abinda ya fada shi ne duk wani mai...
Yanzu-Yanzu: Ƴan Bindiga Sun Sace Iyali 3 A Filato

Iran Zata Ci Gaba Da Kare Shirinta Na Makamashin Nukliya Da Duk Karfin Da Take Da Shi: Ali Shamkahani
Babban mai bawa jagoran juyin juya halin musulunci shawara kan al-amuran siyasa Ali Shamkhani ya bayyana cewa gwamnatin kasar Iran za ta ci gaba da kare shirinta na makamashin Nukliya na zaman lafiya da duk karfin da take da shi. Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Ali Shamkhani ya na fadar haka, a lokacinda ya ziyarci wata kasuwar baje koli, inda cibiyar makamashin Nukliya ta kasar Iran (AEOI) ta ke baje kolin irin ci gaban da ta samu a wannan fasahar a yau litinin a nan Tehran. Babban mai bawa jagora shawara a kan al-amuran siyasa ya kara da cewa, gwamnatin JMI za ta ci gaba da kare duk abinda zai amfani mutanen kasar Iran, ko da...
Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal Dare, ya bayyana cewa sharaɗinsa na sulhu da ’yan bindiga shi ne kawai su daina kashe-kashe su zubar da makamai sannan su miƙa wuya. A baya dai Gwamna Dare ya sha nanata cewa ba zai yi sulhu da ’yan fashin daji ba. Gwamna Sule ya naɗa Kwamishinoni 16 a Nasarawa Atiku da Obasanjo suna ganawar sirri Ko a watan Yulin 2024, sai da wani mai magana da yawunsa, Alhaji Faruk Ahmad, ya bayyana cewa babu wani matsin lamba da zai sa gwamnatinsu ta yi sulhu da ’yan ta’addan. Ya kuma jaddada cewa mataki ɗaya da gwamnatin ta ɗauka wanda kuma yana haifar da ɗa mai ido shi ne yaƙar ’yan bindigar amma babu batun sulhu. Sai...
Sam Nujoma, dan gwagwarmaya neman yencin kasar Namibiya karkashin gwamnatin wariyar launin fata ta Afrika ta kudu, ya rasu a jiya Lahadi kamar yanda gwamnatin kasar ta Namibi a ta bada sanarwa. Shugaban kasar ta Namibia mai ci, Nangola Mbumba ya ce tsohon shugaban kasar ya na jinya a as wani asbiti a babban birnin kasar Windhoek na kimani makonni 3 amma rai yayi halinsa a daren Asabar da ta gabata ya na dan shekara 95. Shafin yanar gizo na Labarai ‘Africanews’ ya bayyana cewa kasar Namibia ta sami yencin kanta ne daga hannun gwamnatin wariya ta Afirka ta kudu a shekara 1990. Sannan Nujoma ya zama shugaban kasar na farko na tsawon shekaru 15. Sannan aka zabi shugaba mai...
An yi wa dubban mutane gwajin lafiya kyauta a Indonesiya don kauce wa mutuwa da wuri. Za a yi gwajin ga ɗaukacin ‘ƴan kasar ne a ranar murnar bikin haihuwarsu, domin cika alkawarin da shugaba Prabowo Subianto ya yi lokacin yaƙin neman zaɓe. Jarirai da ƙananan yara da kuma tsofaffi na cikin waɗanda za a fara yi wa gwajin. A watan da ya gabata, gwamnatin mista Prabowo ta fara bai wa miliyoyin yara ƴan makaranta da kuma mata masu ciki abinci kyauta domin rage rashin abinci mai gina jiki da ke shafar yaro ɗaya cikin biyar a Indonesia.
Gwamna Abdullahi Sule na Jihar Nasarawa ya miƙa wa Majalisar Dokokin jihar sunayen zaɓaɓɓun kwamishinoni 16 domin tabbatarwa. Shugaban Majalisar, Danladi Jatau ne ya bayyana hakan yayin zaman majalisar da ya gudana ranar Litinin a birnin Lafiya. Atiku da Obasanjo suna ganawar sirri Ɗalibi ya kashe abokin karatunsu da gatari a Nasarawa Aminiya ta ruwaito cewa, daga cikin sabbin kwamishinonin da gwamnan ya zaɓa har da tsohon Shugaban Masu Rinjayen a majalisar dokokin jihar, Umar Tanko-Tunga da wani tsohon mamba a majalisar, Mohammed Agah-Muluku. Kakakin Majalisar ya buƙaci kowane ɗaya daga cikin zaɓaɓɓun kwamishinonin da su gabatar da kwafi 30 na duk bayanansu daga yanzu zuwa ranar Alhamis tare neman su hallara a gaban majalsiar a ranar Litinin ta makon...
Sojojin Najeriya sun tarwatsa babbar maɓoyar ƙasurgumin ɗan Bello Turji da ke ƙauyen Garin Fakai a Jihar Zamfara. Wanann nasarar zai gurgunta harkokin ƙasurgumin ɗan ta’addan, wanda a halin yanzu ke wasan ɓuya da jami’an tsaro. Ƙauyen Fakai shi ne babbar mafakar Bello Turji, ɗan ta’addan da ke addabar yankin Zamfara da sassan Jihar Sakkwato. Dakarun rundunar Tsatsa Daji III, sun kuma ƙwato tarin makamai a yankin bayan ’yan ta’addann sun cika bujensu da iska. ’Yan daba sun ƙona gine-ginen makaranta a Binuwai ’Yan gida daya sun yi wa ma’aurata dukan kawo wuka a Kano Sojojin sun yi wannan nasara ne a yayin samamen da suka kai bayan samun bayanan sirri, inda daga bisani suka karasa zuwa mafakar ’yan ta’addan...
Sanarwar ta kuma bayyana cewa wannan ziyara ta gwamnan, za ta ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin gwamnatin jihar Zamfara da Bankin na Duniya. Cikin jawabin sa a wurin, Gwamna Dauda Lawal ya jaddada ƙudirin gwamnatin sa na ƙarfafa dangantakar ta Bankin Duniyar. “Ina so in fara da nuna godiya ta ga Bankin Duniya game da tallafin da ya ke bayarwa a jihar mu. Mun jingina da manufofin Bankin Duniya wajen inganta rayuwar al’ummar mu kawar da talauci da ci gaban ayyukan inganta rayuwa. “Muna sane da ƙalubalen da muka fuskanta, wanda ya shafi gudanar da ayyukan ci gaba a jihar Zamfara, musamman waɗanda suka samu matsala wajen aiwatarwa, sakamakon yanayin da aka shiga. Amma, lallai babu shakka muna...
Wani ɗalibi a Kwalejin Kimiyya da Ƙere-kere ta Tarayya da ke Jihar Nasarawa ya yi wa abokin karatunsa kisan gilla ta hanyar amfani da wuƙa da gatari. Rundunar ’Yan Sanda Jihar Nasarawa ta ce ɗalibin da ya yi kisan gillar ɗan ajin ND2 a Fannin Aikin Banki da Hadahadar Kuɗaɗe ne a Kwalejin kuma yana hannunta, yana amsa tambayoyi. Ta bayyana cewa ya amsa laifin tare da shaida wa masu bincike cewa ya yi amfani da wuƙa da kuma gatari wajen halaka abokin nasa a gidan da suke haya bayan wata hatsaniya a tsakaninsu. Kakakin rundunar, Rahman Nansel, ya bayyana cewa jami’an rundunar sun kai ɗauki ne bayan matar da ɗaliban ke haya a gidanta, Mercy-Bassey, ta sanar da rundunar...
Sojojin Najeriya sun tarwatsa babbar maɓoyar ƙasurgumin ɗan Bello Turji da ke ƙauyen Garin Fakai a Jihar Zamfara. Wanann nasarar zai gurgunta harkokin ƙasurgumin ɗan ta’addan, wanda a halin yanzu ke wasan ɓuya da jami’an tsaro. Ƙauyen Fakai shi ne babbar mafakar Bello Turji, ɗan ta’addan da ke addabar yankin Zamfara da sassan Jihar Sakkwato. Dakarun rundunar Tsatsa Daji III, sun kuma ƙwato tarin makamai a yankin bayan ’yan ta’addann sun cika bujensu da iska. ’Yan daba sun ƙona gine-ginen makaranta a Binuwai ’Yan gida daya sun yi wa ma’aurata dukan kawo wuka a Kano Sojojin sun yi wannan nasara ne a yayin samamen da suka kai bayan samun bayanan sirri, inda daga bisani suka karasa zuwa mafakar ’yan ta’addan...
Wasu ’yan daba sun gine-ginen makaranta a yankin Okpoga da ke Karamar Hukumar Okpogwu da ke Jihar. Ɓata-garin sun ƙona gine-ginen ne a Makarantar Sakandaren Central UBE da ke Ogwu-Okpoga da kuma Makarantar Ƙaramar Sakandare s ake Obossa. Wani shaida ya bayyana wa wakilinmu cewa a makon da ya gabata ne ’yan daban suka yi wannan aika-aika. Shaidan wanda bai amince a bayyana sunansa ba, ya yi zargin wata manufar siyasa ce ta sa ’yan daban suka cinna wa gine-ginen wuta. Ya bayyana damuwa kan yawaitar irin wannan aika-aika a ’yan kwanakin nan. Kokarinmu ma ji daga kakakin ’yan sanda ta Jihar Binuwai, Catherine Aneneh, bai yi nasara ba, saboda mun kira ta a waya ba ta shiga ba. ’Yan...

Kasafin 2025: Kar A Yi Sakaci Macizai Da Birai Su Haɗiye Dala Biliyan 1.07 Da Aka Ware Wa Kiwon Lafiya – Atiku
Ya kuma yi kira da a samar da tsari na gaskiya da rikon amana don bin diddigin yadda ake kashe kudaden da aka ware domin amfanin jama’a.
Ma’aikatar harkokin wajen Masar ta sanar cewa, kasar za ta karbi bakuncin taron gaggawa na kasashen Larabawa a ranar 27 ga watan Fabrairun nan, domin tunkarar al’amura na baya-bayan nan da suka shafi batun Falasdinu da zirin Gaza. Sanarwar ta ce, an yanke shawarar gudanar da taron ne bayan muhimman shawarwarin da Masar ta yi da kasashen Larabawa, ciki har da Falasdinu da ta bukaci gudanar da taron, tare da hadin gwiwar Bahrain. A wani labarin kuma, kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC ta yi kakkausar suka kan munanan kalamai da kuma rashin da’a da firaministan Isra’ila ya yi na yin kira da a kafa kasar Falasdinu a kasar Saudiyya. A ranar Alhamis, ne Netanyahu ya ba da shawara...
Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Kano ya ba al’ummar yankin Sheka awa 24 su kawo wa rundunar sunayen manyan ’yan daban da ke addabar yankin. Rundunar ta ba da wannan wa’adin ne bayan matsalar ’yan daba ta ya ƙi ci ta ƙi cinyewa a yankin da ke Ƙaramar Hukumar Kumbotso. A yayin wani zama na musamman da kwamishinan rundunar ta yi da al’ummar yankin ne aka ba su wannan sanarwar. Kwamishinan ’yan sandan, wanda ya samu wakilci DPO na yankin Dakata, ACP Yusha’u Mus’ud, ya ce muddin al’umma ba su taimaka da bayanan jagororin ’yan daban ba, ta ɓata-garin an kama su ba, babu yadda za a yi ɓata-garin su daina addabar yankin. Ɗan fashi ya yi wa ɗaliban jami’a uku...
Abubuwan da ke faruwa a siyasar jihar a baya-bayan nan sun nuna cewa El-Rufai da Gwamna Sani suna takun saka. A watan Yunin 2024 ne Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta ba da shawarar a binciki El-Rufai kan zargin karkatar da kudaden al’umma. Amma da yake magana a yayin tattaunawar, Bello ya ce, “Babu daya daga cikinsu (Sani da El-Rufai) da ya ba ni labarin rikicin; amma na fahimci cewa, komai ya wuce.” Da aka tambaye shi ko zai iya sasanta mahaifinsa da Sani, Bello ya ce, “Ba aikina ba ne. Aikina shi ne in mayar da hankali wajen taimaka wa al’ummar mazabar Kaduna ta Arewa.”
Fira Ministan Isra’ila, Banjamin Netanyahu, ya gurfana a kotu kan zargin aikata zamba da karbar cin hanci da rashawa. An gurfanar da Mista Netanyahu ne daomin ya amsa tambayoyi a shari’ar da aka jima ana zargin sa da aikata manyan laifuka uku na cin hanci da cin amana. Masu gabatar da kara na zargin sa da aikata laifukan da suka hada da karbar cin hanci da zamba da kuma cin amana. Laifukan sun hada da sa da daga kafar harajin Dala miliyan 500 ga kamfanin sadarwa na Bezeq Telecom domin kamfanin ya tallata shi da matarsa Sara a wani shafin yada labarai. Ɗan fashi ya yi wa ɗaliban jami’a uku fyaɗe ’Yan sanda na neman ’yan bola-jari ruwa a jallo...
Fira Ministan Isra’ila, Banjamin Netanyahu, zai gurfana a kotu kan zargin aikata zamaba da karbar cin hanci da rashawa. Za a gurfanar da Mista Netanyahu ne daomin ya amsa tambayoyi a shari’ar da aka jima ana zargin sa da aikata manyan laifuka uku na cin hanci da cin amana. Masu gabatar da kara na zargin sa da aikata laifukan da suka hada da karbar cin hanci da zamba da kuma cin amana. Laifukan sun hada da sa da daga kafar harajin Dala miliyan 500 ga kamfanin sadarwa na Bezeq Telecom domin kamfanin ya tallata shi da matarsa Sara a wani shafin yada labarai. Ɗan fashi ya yi wa ɗaliban jami’a uku fyaɗe ’Yan sanda na neman ’yan bola-jari ruwa a...
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya ce Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta yi kokarin dakile duk wani makirce-makircen da makiya ke kitsawa. Shugaban na Iran ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi ga dimbin jama’a da suka halarci bikin cika shekaru 46 da samun nasarar juyin juya halin Musulunci a shekara ta 1979 a birnin Tehran yau Litinin. Shugaba Pezeshkian Ya soki ikirarin shugaban Amurka Donald Trump na baya-bayan nan na cewa yana son tattaunawa da Iran yayin da a lokaci guda ya ba da umarnin kakaba wa Iran takunkumi kan man da take fitarwa zuwa sifiri.” Trump ya yi ikirarin cewa Iran na kawo cikas ga tsaron yankin amma “Isra’ila ce, tare da goyon bayan Amurka,...
Kotu ta tsare wani ɗan fashi da ya yi wa ɗalibai mata uku na Jami’ar Jihar Kwara fyaɗe. Matashin da dubunsa ta cika yi wa ɗaliban fyade ne a yayin wani fashi a ɗakunan kwanan ɗalibai mata a cikin dare. Ya yi musu wannan aika-aika tare da yunƙurin kisa ne a daƙinsu kwanan ɗalibai mata da ke wajen harabar jami’ar a yankin Malete a ranar 2 ga watan Disamba, 2024. A yayin gurfanar da matashin a gaban Kotun Majiatare ta Jihar Kwara da ke birnin Ilorin, an tuhume shi da yin amfani da makami wajen yi wa ɗaliban munanan raunuka, tare da yi musu fyaɗe da kuma sace wayoyin iPhone 13 PronMax da iPhone 11 Pro Max. ’Yan sanda na...
’Yan sanda a Babban Birnin Tarayya Abuja sun buƙaci al’umma su kawo musu rahoton duk wanda aka ga yana sana’ar bola-jari a cikin gari. Kwamishinan ’Yan Sanda na Abuja, Disu Olatunji, ne ya sanar da haka bayan taron Majalisar Tsaro ta Babban Birnin Tarayya wanda Minista Ezenwo Nyesom Wike ya jagoranta. Idan ba a manta ba, a ranar 13 ga watan Janairu, 2025 ne Hukumar Babban Birnin Tarayya ta haramta ayyukan ’yan bola-jari a cikin faɗin birnin. Umarnin ya taƙaita ayyukansu ga kan juji da ke ya yankunan da suke wajen birnin. A lokacin zaman ne aka dakatar da ayyukan ’yan gwangwan na tsawon makonni biyu, saboda zargin alaƙarsu da ’yan bola-jari. NAJERIYA A YAU: Shin Har Yanzu Akwai Masu...
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba Akan karkasa mutane gida-gida a bisa mizanin tattalin arziki, musamman a tsarin jari-hujja, inda ke da mawadata da kuma matalauta. A tsakanin al’umma kuma akwai ajin mutane masu matsakaicin samu waɗanda ake kira “Middle Class”. Akan sanya mutane a wannan aji ne galibi bisa la’akari da aiki ko sana’ar da suke yi, da kuɗin da suke samu, da matakin ilimin da suka kai, da ma matsayinsu a tsakanin al’umma. Sai dai a baya-bayan nan irin wadannan muntane sun bi sahun matalauta wajen korafi game da yadda suke dandana kudarsu saboda tsadar rayuwa. NAJERIYA A YAU: Dalilin Faɗuwar Farashin Tumatur A Kasuwa DAGA LARABA: Yadda Al’adun Aure A Ƙasar Hausa Suka Koma ‘Event Centre’...
Iran tana gudanar da bukukuwan zagayowar nasarar juyin juya halin Musulunci yau tsawon shekaru 46 tare da samun nasarori da kalubale A yau Litinin ne, al’ummar Iran suke gudanar da bukukuwan tunawa da cika shekaru 46 da samun nasarar juyin juya halin Musulunci a kasar, wanda marigayi Imam Ruhollah Khomeini (Yardan Allah ta tabbata a gare shi) ya jagoranta, a cikin wadannan shekaru da dama, juyin juya halin Musulunci ya fuskanci makirce-makirce masu yawa da cikas, kuma ya samu gagarumar nasara, mafi muhimmanci daga cikinsu shi ne hambarar da gwamnatin sarki Shah da kasashen yammacin duniya suke goya masa baya, kamar yadda Iran bayan samun nasarar juyin juya halin Musulunci ta yi nasarar kafa gwamnati da samar da ginshikanta da...

Ministan Mai Na Iran Ya Ce: Hana Iran Fitar Da Man Fetur Zuwa Kasuwannin Duniya Mafarki Ne Na Shugaban Amurka
Siyasar tsananata matsin lamba kan Iran ta gaza cimma buri kuma hana fitar da man da Iran ke fitarwa mafarki ne da ba zai tabbata ba Ministan mai na kasar Iran Mohsen Paknejad ya bayyana matsayar matsin lamba da Amurka ke yi kan fitar da man kasar Iran a matsayin siyasa ta nuna gazawa, yana mai cewa: Hana fitar da man fetur din Jamhuriyar Musulunci ta Iran zuwa wajen kasar, mafarki ne da ba zai taba wanzuwa ba. Ministan mai na Iran Mohsen Paknejad a matsayin mayar da martani ga furucin Trump ta sake dawo da tsananta siyasar matsin lamba da nufin gurgunta harkar tattalin arzikin Iran ta hanyar hana ta fitar da man fetur, a jiya Lahadi ya bayyana...

Kwamnadan Rundunar Sojin Ruwan IRGC Ya Ce: Suna Iya Rufe Mashigar Hormuz Amma Ba Za Yi Hakan Ba Yanzu
Kwamandan rundunar sojojin ruwa na dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran ya bayyana cewa: Za su iya rufe mashigar Hormuz, amma ba za yi hakan a yanzu ba Kwamandan rundunar sojojin ruwa na dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran Birgediya Janar Ali Reza Tangsiri ya yi bayani kan irin fitattun abubuwan da jirgin ruwan da Iran ta kera mai suna Shahid Bahman Baqiri, inda ya ce; Wannan jirgi shi ne nau’i daya tilo saboda babu wata kasa a yankin yammacin Asiya da ke da makamancinsa. Birgediya Janar Tangsiri ya bayyana a cikin shirin ”Labarin juyin juya hali” a tashar Al-Alam cewa: Bayan sanarwar da Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya fitar dangane...

Kwamandan Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Ya Ce: Hamas Ta Yi Rawar Gani Wajen Kare Kanta
Kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran ya jaddada cewa: Kungiyar Hamas duk da iyakantaccen kayan yakinta ta kalubalanci gwamnatin ‘yan sahayoniyya Kwamandan dakarun kasa na Dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran Birgediya Janar Morteza Miryan ya jaddada cewa: Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ta kalubalanci gwamnatin mamayar ‘yan sahayoniyya da suke samun goyon bayan Amurka da kasashen Yamma duk da iyakantaccen kayan yakin da ta mallaka na kare kai. Birgediya Janar Miryan ya ce a cikin jawabinsa a wajen bikin tunawa da shahidan harin “Wal-Fajir 8” da aka gudanar a lokacin tunawa da shahidan lardin Alborz da ke yammacin birnin Tehran: A lokacin yakin da aka yi na shekara ta 1980 zuwa shekara ta 1988),...
Yanzu haka, an kara tura manyan injuna domin gudanar da aikin ceto a wurin da zaftarewar kasa ta auku a lardin Sichaun na kasar Sin. Da farko za su kwashe duwatsu da kasa da suka lullube wurin, kuma da zarar an ga alamun gini, za a sanar da ma’aikatan dake wurin domin kara bincike. Zuwa karfe 11:00 na safiyar yau agogon Beijing, an tabbatar da kasa ta binne gidaje 10 da wata masana’ata 1, sanadiyyar zaftarewar kasar, wadda ta auku a gundumar Junlian ta birnin Yibin na lardin Sichuan. Haka kuma, mutum 1 ya rasa ransa yayin da 28 suka bata. Zuwa yanzu dai, ana ci gaba da gudanar da aikin ceto. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)
Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya gana da tsohon ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola, a birnin Legas. Kwankwaso ya bayyana a shafinsa na X cewa sun tattauna kan batutuwan da suka shafi siyasa da makomar dimokuradiyya a Najeriya. Aisha Binani ce ta lashe zaɓen Adamawa, ina da ƙwararan hujjoji – Ari Ɗan sanda ya rataye kansa har lahira a Neja Wannan ganawa na zuwa ne a daidai lokacin da jam’iyyun adawa ke kira ga haɗin kai domin fuskantar zaɓen 2027. A watan Oktoban 2024, jam’iyyar APC a Jihar Osun ya dakatar da Aregbesola bisa zargin cin amanar jam’iyya da sukar shugabannin jam’iyyar, ciki har da Shugaba Bola Tinubu da tsohon gwamnan...
An bude atisayen soja kan teku bisa hadin gwiwar wasu kasashe a birnin Karachi na kasar Pakistan, a ranar 7 ga wata. Asitayen sojan da kasar Pakistan ta tsara ya samu halartar jiragen ruwan soja daga kasashe sama da guda 10, wadanda suka hada da Sin, da Indonesiya, da Japan, da Italiya, da Malasiya, da kuma Amurka da dai sauransu. Haka kuma, sauran kasashe sama da guda 40 sun tura masu sa ido wajen atisayen. An raba atisayen sojan zuwa matakai guda biyu. Mataki na farko shi ne tsakanin ranaku 7 zuwa 9 ga watan Fabrairu, inda za a yi atisayen soja kan tashar jiragen ruwa, da tattaunawa kan atisayen, da tattaunawa kan ayyukan musamman tsakanin bangarori daban daban da...
Wani Mataimakin Sufeton ’Yan Sanda (ASP), Shafi’u Bawa, da ke aiki da Rundunar 61 Police Mobile Force a Kontagora da ke Jihar Neja, ya hallaka kansa har lahira. Wani jami’in dan sanda ya shaida wa Aminiya cewa, lamarin ya faru ne a ranar Asabar. Gwamnatin Kano ta dakatar da wani fim mai suna Zarmalulu Aisha Binani ce ta lashe zaɓen Adamawa, ina da ƙwararan hujjoji – Ari An tsinci gawarsa rataye a cikin dakinsa. Majiyoyi sun ce mahaifinsa, Malam Usman Bawa ne, ya fara gano abin da ya faru sannan ya kai rahoton lamarin zuwa ofishin ’yan sanda da ke Kontagora. Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar lamarin. Ya ce: “A ranar 8...
A rana Juma’a da ta gabata, aka kaddamar da gasar wasannin kankara ta nahiyar Asiya karo na 9, a birnin Harbin na lardin Heilongjiang na kasar Sin. Wannan gasa ta kasance babbar gasar wasannin kankara ta kasa da kasa karo na 2 da Sin ta karbi bakuncinta, biyo bayan gasar wasannin Olympics na lokacin sanyi da ta gudana a birnin Beijing na Sin, a shekarar 2022. An ce, gasar wasannin kankara ta wannan karo ta samu halartar ‘yan wasa fiye da 1270 da suka zo daga kasashe da yankuna 34 dake nahiyar Asiya, alkaluman da suka kai matsayin koli a tarihi. Inda har wasu kasashen da ba sa samun yanayi mai sanyi da muhalli mai kankara a cikin gida, kamarsu...
An bayyana cewa Iran ce kasar ta 10 a duniya wajen samar da wutar lantarki, da yawan megawati dubu 94 da 846. Manajan da yake kula da tsara manyan ayyuka a ma’aikatar makamashi ta Iran, Behruz Muradi ya bayyana cewa, shekru 46 da su ka gabata, wato a lokacin juyin juya halin musulunci, yawan megawatin da Iran take samarwa ya yi kasa da wanda ake da shi a yanzu har sau hudu. Manajan ya kuma kara da cewa wutar lantarki da ake da ita a Iran da karfin tsarin da take da shi, tana taka rawa mai muhimmanci wajen gina tattalin arzikin kasar. Haka nan kuma ya ce, da akwai kyakkyawan tsarin da ake da shi ya samar da cigaba...
Shugaban kasar Namibia dake kan gado Nangolo Mbumba ne ya sanar a yau Lahadi cewa, jagoran samun ‘yacin kasar Sam Nujoma ya rasu a jiya Asabar da dare, bayan da aka kwantar da shi a wani asibitin babban birnin kasar Windhoek. Sanarwar da shugaban kasar ta Namibia mai ci a yanzu, ya fitar ya bayyana mutuwar Nujoma da cewa; ginshikin da aka kafa kasar akansa ya girgiza. Sam Nujoma ya jagoranci fadan sama wa kasar ta Namibia ‘yanci daga mulkin nuna wariyar launin fata na Afirka ta kudu, a shekarar 1990, sannan kuma ya jagoranci kasar na tsawon shekaru 15. A lokacin da yake a raye, al’ummar kasar ta Namibia suna girmama shi matuka a matsayin wanda ya jagoranci fadan...
Shugaban kasar Iran Mas’ud Fizishkiyan ya yi kira da a kafa kawancen duniya da dukkanin kasashen musulmi za su shiga ciki, domin taimakawa mutanen Gaza, da sake gina yanki, tare da cewa, kasashen musulmi kadai za su iya sake gina yankin na Gaza tare da dawo da rayuwa a cikinsa. A ganawar da ya yi da mambobin majalisar jagoranci ta kungiyar Hamas, anan Tehran ya yi jinjina ga shahidan kawancen gwagwarmaya, ya kuma yi murna akan nasarar da ‘yan gwgawarmaya su ka samu akan ‘yan sahayoniya. Shugaban kasar ta Iran ya kara da cewa; Nasarorin da mutanen na Gaza su ka samu, sun hana makiya ‘yan sahayoniya cimma manufofin da su ka shata, duk da cewa adadin shahidan da aka...
14– Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa Shirin wanda yake kawo maku kissoshi wadanda suka zo cikin alkur’ani mai girma ko cikin wasu littafan wadanda suka hada da littafin Dastane rastan na shahid Aya. Murtadha muttahhari, ko cikin littafin Mathnawi na maulana jalaluddeen ,Rumi, ko kuma cikin wasu littafan. Da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu. ///… Madalla, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata, mun ci gaba da kawo maku sirar Imam Alhassan (s) Jikan manzon All..(s) sannan limami na 2 daga cikin limamai masu tsarki daga iyalan gidan manzon All..(s) kuma da na farko ga Fitima(s) diyar manzon All..(s)....
A ranar Lahadi ne mahukuntan kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars suka bayar da sanarwar dakatar da mai koyarwa, Usman Abdallah mako uku, sakamakon rashin kokarin kungiyar a baya bayan nan a bana da kuma nuna halin rashin hakuri ga magoya bayan kungiyar a lokacin da aka tashi daga wasan da kungiyar ta tashi canjaras da kungiyar Bayelsa United a filin wasa na Sani Abacha dake kofar mata a Kano. A wata sanarwa da aka fitar a shafin sada zumunta na facebook, kungiyar ta ce kociyan ya nuna halin rashin da’a, bayan tashi ba ci a wasa da Bayelsa ba kuma halayyar da ya nunawa magoya baya ba ta dace ba saboda a matsayinsa na mai koyarwa dole ne sai...
A’a ba ni da aure amma in sha Allah ina sa ran yi. Malama Khadija kina da wata sana’a ne ko kuma karatu kike yi? Eh ina da Diploma a Cibil Law, sai Degree a Islamic Studies,.kuma ni cikakkiyar ‘yar kasuwa ce,.na Fara sana’a a 2016 Wane irin kasuwanci kike yi ma ana dame-dame kike sayarwa? Mhm, gaskiya ina kasuwanci da yawa kamar sarrafa dinki, kayan dandano da goge-goge da sarrafa dukiya Me ya ja hankalinki da har kike sha’awar wannan sana’ar? Ni dai gaskiya ban yadda da rayuwa akan dogaro da wani ba, rayuwata ita ce, kuma na fi yarda da in samu abu na kaina ba sai na je roko ba ko kuma sai na...
Wakilin Jagoran juyin juya halin Musulunci a kasar Iraki ya ce: Juyin juya halin Musulunci ya gabatar da wani sabon samfuri na hadin kan al’umma Ayatullah Mojtaba Hosseini, wakilin Jagoran juyin juya halin Musulunci a kasar Iraki ya bayyana muhimmancin hadin kan al’ummar musulmi da kuma nauyin da ya rataya a wuyan musulmi na daidaiku da na al’umma dangane da manufofin juyin juya halin Musulunci, yana mai cewa: juyin juya halin Musulunci ya gabatar da wani sabon salo na hadin kan al’ummar musulmi. A jawabin da ya gabatar na zagayowar samun nasarar juyin juya halin Musulunci a Iran da aka gudanar a tsohon gidan da Imam Khumaini (r.a) da ya zaune a birnin Najaf, Ayatullah Husaini ya jaddada muhimmancin hadin...
Falasdinawa sun fitar da martanin farko mai gauni kan kalaman fira ministan ‘yan mamayar Isra’ila dangane da furucinsa ga Saudiyya Kungiyar ‘yantar da Falasdinu ta yi Allah wadai da kalaman da fira ministan mamayar Isra’ila Benjamin Netanyahu ya yi game da kafa kasar Falasdinu a cikin kasar Saudiyya. Sakataren kwamitin zartarwa na kungiyar ‘yantar da Falasdinu Hussein Al-Sheikh ya bayyana cewa: Suna yin Allah wadai da matakin da mahukuntan yahudawan sahayoniyya suka dauka na kai cin mutunci da raina kimar masarautar Saudiyya da ‘yancinta, wanda suka yi kira da a kafa kasar Falasdinu a kasar Saudiyya, kuma wannan furuci na Rashin tunani ya yi cin karo da dokokin kasa da kasa da yarjejeniyar kasa da kasa. Ya kara da cewa:...
Sojojin mamayar Isra’ila sun fara janyewa daga yankin Netzarim da ke tsakiyar Zirin Gaza Kafofin yada labaran haramtacciyar kasar Isra’ila sun tabbatar da cewa: Sojojin mamayar Isra’ila za su fara ficewa daga yankin Netzarim da ke tsakiyar Zirin Gaza a daren jiya. Jaridar Yedioth Ahronoth ta haramtacciyar kasar Isra’ila ta watsa rahoton cewa: Rundunar sojin mamayar Isra’ila ta ba da umarnin ficewa daga yankin Netzarim da ke tsakiyar Gaza a wani bangare na aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin kungiyar Hamas da gwamnatin mamayar Isra’ila a yankin. Jaridar ta bayyana cewa: Runduna ta 162 ta sojojin mamayar ta sake matsawa zuwa kusa da kan iyaka da kuma janyewa daga yankin Netzarim na nufin cewa, babu sojojin mamayar Isra’ila a arewacin...
Babban taron Alkur’ani na farko a Nijeriya da za a yi a Abuja na daga cikin batutuwa da suka ɗaukar hankali a ’yan kwanakin nan. Yanzu bai wuce makonni biyu a gudanar da taron a ranar 22 ga watan Fabrairun da muke ciki ba, inda za a tara mahaddata Al-Kur’ani daga sassan Nijeriya. Me ya sa ake musayar yawu tsakanin APC da PDP? Katsina ta zama cibiyar haɗin kan ƙabilun ƙasa a Arewa — Gwamna Radda Sai dai har yanzu ana ta diga ayar tambaya kan tushen taron da masu dauki nauyin mutum 30,000, mahaddata da masu zayyanar kalmomin Al-Kur’ani. Kungiyar Jama’atu Izalatil Bidi’a Wa Ikamatis Sunnah (JIBWIS), wadda aka fi sani da Izala, ce ke jagorantar shirya taron, amma...
Ga wasu manyan ‘yan kwallo da tauraronsu ke haskawa a duniya, wadanda asalin ‘yan Nijeriya ne, wato ko dai iyayensu baki daya ko wani daga cikin iyayen ‘yan Nijeriya ne. Jamal Musiala (Jamus) Matashin dan wasa Jamal Musiala, wanda aka haifa a ranar 26 ga Fabrairun shekarar 2003, fitaccen dan kwallon kasar Jamus ne da kungiyar kwallon kafa ta Bayern Munich ta Jamus din kuma yana cikin matasan ‘yan kwallon da suke tashe a duniya a yanzu saboda ba za ka lissafa matasan ‘yan wasa guda biyar ba a duniya ba tare da ka saka sunansa ba. An haife shi ne a garin Stuttgart da ke Jamus, amma mahaifinsa mai suna Daniel Richard asalin can Nijeriya ne, wanda ya...
Duk da cewa akwai sauran lokaci kafin babban zaben 2027, ana ci gaba da musayar yawu kan shirye-shiryen manyan ‘yan siyasa da ke hamayya da gwamnatin Bola Ahmed Tinubu, inda suke tarurruka tare da tuntuɓar juna kan yadda za su kayar da Jam’iyyar APC mai mulki a Zaɓen 2027. Fadar Shugaban kasa ta mayar da martani kan kalaman da wasu daga cikin ‘ya’yan jam’iyyun adawa da na cikin gidanta suke yi, inda suka zarge ta da sauka daga kan turbar da jam’iyyar take. Katsina ta zama cibiyar haɗin kan ƙabilun ƙasa a Arewa — Gwamna Radda Ta kashe saurayinta saboda ya gaisa da tsohuwar abokiyar karatunsa Fadar Shugaban kasa na mayar da martani ne bayan wani taro da jagororin hamayya...
A zamanin baya, duk da cewa fina-finan nanaye sun fi karbuwa a wajen mutane, amma haka muke kokartawa wajen ganin an shigar da wata koyarwa ta addinin musulinci ko kuma wani abu mai amfani da zai amfanar da al’umma ta wani bangare, amma yanzu duk an daina wannan, masu shirya fina-finai na amfani da labarai masu tsafta da amfanarwa, ba tare da da sanya wakoki ko makamantansu a ciki ba, in ji Malam. “Dalili kuwa shi ne, yanzu ‘ya’yan mutunci da arziki su ne ke yin harkar, sannan kuma su ne suke samun arzikin duniya da na lahira, akwai lokacin da har mata masu zaman kansu din, sai da muka daina samun su idan zamu yi fim, amma yanzu wannan...
A Nijar an yi bikin cika shekaru 46 da samun nasarar juyin juya halin Musulunci a Iran a Yamai babban birnin kasar, bikin da ya samu halartar ‘yan siyasa da jakadu da jami’an diflomasiyya da ‘yan jarida. Manyan baki da suka halarci bikin sun hada da ministan harkokin wajen Nijar, magajin garin Yamai da kuma wakili na musamman na Firaministan Nijar. A yayin wannan biki, jakadan Jamhuriyar Musulunci ta Iran a Nijar Ali Tiztak ya gabatar da jawabi, inda ya yi ishara da irin nasarorin da Tehran ta samu cikin shekaru arba’in da suka gabata. Ali Tiztak ya ci gaba da cewa, duk da takunkumin zalinci da kalubalen da Jamhuriyar Musulunci ta Iran take fuskanta tun ranar farko bayan nasarar...
Wani matashi ɗan kasar Argentina mai shekara 23 ya rasa ransa a sakamakon daɓa masa wuƙa da budurwarsa ta yi saboda kawai ya gaisa da wata mata a kan titi. Kishi madaidaici zai iya zama abu mai masu alaka da juna, amma mafi yawanci na iya wuce kima! Abba ya naɗa sabon Sakataren Gwamnatin Kano Shigo da hatsi daga ƙetare ya karya farashinsa a Neja Idan aka dubi labarin Mariano Grinspun, ɗan shekara 23 daga González Catán, wani birni a lardin Buenos Aires na Argentina, wanda budurwarsa mai tsananin kishi ta caka masa wuka wanda ya yi sanadiyya mutuwarsa bayan ya gaisa da wata tsohuwar abokiyar karatunsa a titi, za a ga abin akwai ban mamaki. Abin ya faru ne...
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya naɗa Umar Farouk Ibrahim a matsayin sabon Sakataren Gwamnatin Kano. Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwar da Kakakin Gwamnatin Kano, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a yammacin ranar Asabar. Shigo da hatsi daga ƙetare ya karya farashinsa a Neja Ya yi wa kansa keji don daina shan sigari Sanarwar ta ce naɗin sabon Sakataren Gwamnatin zai fara aiki ne a hukumance daga ranar Litinin mai zuwa 10, ga Fabarairun 2025. Sanarwar ta ce an naɗa sabon Sakataren Gwamnatin wanda ya shafe sama da shekaru talatin yana aikin gwamnati la’akari da ƙwarewar aiki da yake da ita a hukumomi da ma’aikatu daban-daban na wajen ganin an cimma muradin gwamnati mai ci na ciyar da Jihar...
“Ina so na fara da godiya ga Bankin Duniya kan tallafin da yake ci gaba da bai wa jiharmu. Mun daidaita manufofin ci gabanmu da manufar Bankin Duniya na kawar da talauci da inganta ci gaba mai dorewa.” “Mun kuma lura da kalubalen tsaro da a baya suka yi tasiri wajen aiwatar da ayyuka a jihar Zamfara, musamman wadanda suka kawo cikas ga cimma burin da aka sanya a gaba. Duk da haka, muna samun ci gaba yayin da ake fuskantar ƙalubalen, kuma abubuwa suna komawa daidai.” “Mun inganta matakan tsaro ta hanyar kwararan matakai da jihar ta dauka na inganta tsaro da kara daukar matakan dakile barazanar tsaro.” “Gwamnatinmu ta dukufa wajen tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi ta...
Kasuwannin hatsi a Jihar Neja suna fama da matsalar faduwar farashi amfanin gona, sakamakon shigo da hatsi daga kasashen makwabta kamar Chadi da Ghana da Jamhuriyar Benin da Burkina Faso. Wannan yanayi ya haifar da yawan kaya, wanda ke shafar manoma da ‘yan kasuwa da masu samar da kayayyaki a yankin. Ya yi wa kansa keji don daina shan sigari Amurka ta dakatar da bai wa Afirka ta Kudu tallafi Manoman da suka tara hatsi don cin riba sun shiga damuwa saboda shaguna da kasuwanni sun cika da buhunhunan hatsi, amma babu masaya. Wasu daga cikin manoma da ’yan kasuwa sun bayyana wa wakilinmu cewa, wannan yanayi ya rikitar da harkar kasuwanci, inda suke fama da karancin riba saboda farashin...
Ibrahim Yucel ya shafe shekaru 20 yana zukar taba sosai a lokacin da ya yanke shawarar ci gaba da zuka sosai. Jarabar son kowane irin abu ba shi da kyau, kuma zukar taba tana cikin mafi muni. Amurka ta dakatar da bai wa Afirka ta Kudu tallafi Yadda rikicin shugabanci ya janyo rufe babban masallacin gari Barin shan taba yana da matukar wahala, yana bukatar jajircewa da sadaukarwa. Duk da gagarumin kokarin da suke yi, kadan ne kawai na masu zukar sigari suka sami nasarar shawo kan jarabar son da suke yi mata. Kimanin shekara 11 da suka gabata, labarin wani mutum na kokarin daina shan taba ya shahara a talabijin da sauran kafafen yada labarai lokacin da ya saka...
A daren ranar 6 ga wannan wata, an gudanar da wani biki mai taken “Bikin Bazara Namu” a cibiyar hukumar bunksa ilmi da kimiyya da fasaha da al’adu ta MDD, wato UNESCO dake birnin Paris na kasar Faransa, wanda babban rukunin Sin dake hukumar, da gidan talabijin na lardin Henan na kasar Sin suka karbi bakuncin gudanar da shi, don murnar cewa, Bikin Bazara na al’ummar kasar Sin ya shiga cikin jerin bukukuwan al’adun gargajiya da bil’adama ya yi gado a duniya. Babbar wakiliyar Sin dake hukumar UNESCO, Yang Xinyu ta bayyana cewa, an yi wannan shagali ne don murnar bikin gargajiya na al’ummar kasar Sin don more al’adu tare da sassan duniya, da kara matsa kaimi ga yin hadin...
Mai magana da yawun rundunar ‘ƴansandan jihar, Abubakar Sadiq ya ce; tuni jami’ansu sun je unguwar da gidan yake amma kafin su karasa tuni ‘ƴan bindigar sun tafi da Janar Tsigan. Sai dai ya bayyana cewar jami’an tsaro suna aiki ba dare ba rana tare da haɗin guiwa da masu ruwa da tsaki domin kamo ‘yan bindigar. A wani ci gaban kuma, rundunar ‘ƴansandan jihar ta Katsina ta kama wasu mutane 45 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban a jihar.
Mata a Karamar Hukumar Danja suna kira ga Gwamnatin Jihar Katsina da ta gyara hanyar Tsangamawa a Babban Rafi saboda yawan rasuwar mata masu juna biyu da jariransu. Sun yi wannan kira ne a yayin wani taron gaggawa da manyan jiga-jigan al’umma suka shirya domin tattauna matsalar da ta dade tana addabar jama’a – hanyar Tsangamawa. Hanyar Tsangamawa da ke Babban Rafi, Karamar Hukumar Danja, Jihar Katsina, ta haddasa mutuwar mata masu juna biyu da jariransu, musamman a lokacin damina. Duk da yawan koke da rokon gwamnati, har yanzu ba a dauki matakin gyara hanyar ba. A wata hira da suka yi da Radio Nigeria, wasu daga cikin matan yankin sun bayyana cewa mata masu...
Jagoran juyin juya halin musulunci a nan Iran ya gana ta tawagar shoura ta kungiyar Hamas a safiyar yau Asabar a nan Tehran inda ya bayyana cewa mayakan kungiyar sun sami nasara a kan Amurka da HKI a yakin da suka dora masu na tsawon watanni 15. Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Imam Sayyid Aliyul Khaminae yana cewa tsagaita wuta da aka samu bayan wannan lokaci mai tsawo na fafatawa yayi dai-dai. Tawagar shuraa ta Hamas din dai sun hada da shugaban riko na kungiyar Khalil Al-Hayya, shugaban majalisar shoora ta kungiyar Muhammad Ismail Darwish da sauransu. Jagoran ya kara da cewa nasarar da mutanen Gaza suka samu a kan Amurka da kawayenta misdaki nan a...

MDD Ta Ce Masu Fama Da Cutar HIV/AIDS Miliyon 6 Ne Zasu Mutu Saboda Janyewar Amurka Daga Tallafawa Hukumar UNAIDS
Hukuma mai kula da samar da magungunan HIV/AIDS ko (UNAISD) ta MDD ta bada sanarwan cewa mai yuwa mutane kimani miliyon 6 ne zasu mutu a duk fadin duniya a cikin shekaru 4 masu zuwa saboda rashin samun tallafin Amurka a cikin shirin. Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto bayyana cewa, a ranarsa ta farko na kama aiki a matsayin shugaban kasan Amurka, ya dakatar da dukkan tallafin da Amurka take bayarwa a duniya na tsawon kwanaki 90. Labarin ya nakalto shugaban shirin samar da magunguna HIV/AIDS Christine Stegling tana cewa, duk tare da cewa Amurka ta ci gaba da tallafawa HIV/AIDS na wucin gadi, amma suna ganin cewa da wuya hakan ya ci gaba don tun...
Kotun hukunta manya-manyan laifuka ta kasa da kasa ICC ta yi allawadai da takunkuman da gwamnatin Amurka ta dorawa kotun, ta kuma kara da cewa zata ci gaba da aikinta na tabbatar da adalci a duniya kamar yadda ta saba. Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa kotun ICC kotu ce wacce take karban koke-koke na mutane da kasashe a duk fadin duniya, amma wacce gwamnatin Amurka ta ke son takaita ikonta don tallafawa HKI a yakin da take fafatawa da Falasdinawa wadanda ta mamaye kasarsu fiye da shekaru 76 da suka gabata. A ranar Alhamis da ta gabata ce shugaban kasar Amurka Donal Trump ya sanya hannu a kan wata doka wacce ta dorawa kotun ta...
Firay Ministan HKI Banyamin Natanyahu ya bawa kasar Saudiya Shawara samarwa Falasdinawa kasa daga cikin hamada mai girma da take da shi. Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Natanyahu yana fadar haka wa wata tashar talabijin ta HH a safiyar yau Asabar. Amma a maida martani ga Natanyahu, dan majalisar dokokin kasar Burtania a jam’iyyar Larbor Afzal Khan yace, wannan shawarar ta Natanyahu tabbaci ne na laifin fitta mutane daga kasarsu da karfi, don kawai ya na son a kwace zirin gaza daga Falasdinawa. Falasdinawa basa bukatan karin kasa suna son yenci ne a kasarsu. Inji dan majalisar dokoki Kim Johnson na jam’iyyar Lebour.. Kafin haka dai sarki Saman bin Abbdul azizi na kasar Saudiya yace ba...

Thomas Bach Ya Bai Wa Cmg Izinin Sarrafa Watsa Labarun Gasar Olympics Ta Lokacin Hunturu Ta Milan Ta 2026
Albarkacin bikin bude gasar wasannin motsa jiki ta lokacin hunturu ta Asiya karo na 9 dake gudana a birnin Harbin na Sin, shugaban kwamitin shirya gasar Olympics ta kasa da kasa, Thomas Bach ya ziyarci cibiyar yada labarai ta gasar a jiya Juma’a, kuma ya yi hadin kai da shugaban rukunin gidajen rediyo da talibijin mallakin kasar Sin, wato CMG, Shen Haixiong, don bai wa runkunin na CMG damar tsarawa da kuma sarrafa watsa labarun gasar Olympics ta lokacin hunturu ta Milan da Cortina d’Ampezzo ta shekarar 2026. Shen Haixiong ya ce, gasar wasannin motsa jiki ta lokacin hunturu ta Asiya da ake shiryawa a birnin Harbin, wata kasaitaciyyar gasa ce ta kasa da kasa da Sin ta shirya bayan...
Xi: Kasar Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Da IOC Don Inganta Wasannin Olympic Na Duniya
A bayan nan ne mahukunta a Ƙaramar Hukumar Agege, a ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ƙaramar Hukumar Agege, Alhaji Ganiyu Kola Egunjobi suka kulle babban masallacin Hausawa na garin, biyo bayan wani rikici da ke da alaƙa da na limanci ya ɓarke a masallacin a ranar Juma’a makon jiya. Rikicin na zuwa ne bayan rasuwar babban limamin garin Agege, Shaikh Sharif Habib Abdul-Majid, wanda ya rasu kwanaki biyu gabanin aukuwar lamarin. Yadda Kano ke samar da madarar Naira biliyan 2.2 An dakatar da dagaci kan zargin saran maraya da adda A wani bidiyo da ya karade kafafen sada zumunta na zamani, an ga masallata a cikin masallacin suna kai wa junansu duka, wadanda suka haɗar da ɓangarori uku. Waɗanda suka bai wa...
Yadda ake amfani da shi: Za ku dinga shafa zumar a gabanku, ku barta na tsawon mintuna 30, sai ku wanke da ruwan dumi, sannan ku shafa Man Zaitun. Za ku dinga yin haka safe da yamma kafin kwanciya. Sannan ku dinga dafa ‘ya’yan hulba na tsawon mintuna 10 da ruwan da bai wuce kofi daya ba, sai ku dora shi a wuta ya dan tafasa bayan kun sauke shi sai ku tsiyaye shi sai ku sa masa zuma cokali uku, za ki yi wannan hadin shima safe da yamma. Sai kuma maganin kurajen da kaikayin gaba: Kai tsaye ana cewa sanyin mara shi ne yake jawo wannan matsala, amma abin da ya kamata mu sani shi ne...
Madara muhimmin abinci ne da ake bukata domin samun sinadarai masu ginawa da ƙara ƙarfi da lafiyar jiki. Bincike ya nuna cewa mutane biliyan shida ne ke shan madara a duniya, wanda ya sa shan madarar saniya da kiwon dabbobi ya zama wani vangare na rayuwar ɗan adam. Dubban mata Fulani suna samun kuɗaɗen shiga ta hanyar sayar da madara ga ɗaiɗaikun mutane ko jama’a ko ’yan kasuwa, waɗanda suke sha ko sarrafa shi domin amfanin kasuwanci. Lura da muhimmancin madara ga rayuwar ɗan Adam da kuma ƙoƙarin rage haɗarin da ke tattare da shan ta, Hukumar Haɓaka Noma da Kiwon Dabbobi ta Jihar Kano (KSADP) ta zuba jarin Dala miliyan 8.03 don gina cibiyoyi 100 na tattara madara...
Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, ya sha alwashin gyara wa da faɗaɗa sansanin horas da matasan maus yi wa ƙsa hidima (NYSC) na dindindin a jihar. Da yake karɓar babban Daraktan NYSC, Birgediya Janar Yusha’u Ahmed a Maiduguri, Zulum ya ce gwamnatinsa za ta gaggauta gina sansanin dindindin domin karɓar ƙarin ‘yan bautar ƙasa. Ya kuma yaba da gudunmawar da likitoci da malaman kimiyya ke bayarwa a makarantu. Sin Ta Yi Bikin Tunawa Da Wadanda Aka Hallaka Yayin Kisan Kiyashin Birnin Nanjing Tinubu Ya Amince Da Naira Biliyan 80 Domin Sake Gina Madatsar Ruwa Ta Alau Da Ke Borno Shugaban NYSC ya gode wa gwamnatin Borno bisa tallafin da take bai wa ‘yan bautar ƙasa, ciki har da alawus na...

Aikin Gina Babbar Mayankar Dabbobi Zai Taimaka Wajen Kara Samar Da Wadataccen Nama A Nijeriya – Minista
A cewar Maiha, kafa wajen bayar da horo da kamfanin na ABIS ya yi, zai cike gibin da ake da shi a fannin kiwo da kuma bayar da gudunmawa wajen kara habaka tattalin arzikin fannin. Ministan ya kara da cewa, bayar da ingantaccen horo a fannin bunkasa kiwo, zai taimaka wajen samar da wadataccen abinci da kara samar da ayyukan yi ga ‘yan kasar, musamman ma matasa. Maiha, ya kuma bai wa kamfanin na ABIS tabbacin cewa, ma’aikatarsa, za ta bai wai kamfanin goyon bayan da ya dace, domin samar da kwararru a fannin bunkasa kiwon kasar. Da yake yin tsokaci kan jajircewa da mayar da hankali na kamfanin na ABIS, Maiha ya bukaci kamfanin ya yi hadaka da ma’aikatarsa,...
Dubban masu zanga-zanga ne suka fito kan titunan kasar Jordan da kasar Iraki domin yin Allah wadai da shirin shugaban Amurka Donald Trump na korar Falasdinawa daga yankin Gaza. Masu zanga-zanga a Amman babban birnin kasar Jordan, da kuma wasu garuruwan kasar Larabawa, sun yi zanga-zangar nuna adawa da shirin na tilastawa mazauna zirin Gaza kaura. A Jodan an gabatar da wani sabon daftarin doka a majalisar dokokin kasar da zai haramta tilastawa Falasdinawa komawa Jordan. An kuma gudanar da zanga-zangar adawa da shirin a Bagadaza babban birnin kasar Iraki, baya ga Masar inda aka yi irin wannan zanga-zangar. Yayin ganawarsa da firayi ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu a ranar Alhamis, Trump ya bayyana shirinsa na kwace yankin Gaza na Falasdinu...
Su tsare tsaren anyi shirin tabbatar dukkan makarantu masu zaman kan su da na gwamnati za su fara amfani da tsarin a watan Janairu 2025. Sai dai kuma watan Janairu ya wuce ba tare da samun wani ci gab aba dangane da lamarin. Rahoto ya nuna har yanzu da akwai sauran Rina a Kaba, domin kuwa da akwai karancin makarantu wadanda basu da irin kayan da za ayiu amfani da su wajen aiwatar da sabon tsarin,da kuma yadda za a horar da Malamai, hakan ta sa aka bar masu ruwa da tsaki cikin shakku ko sabon tsarin ilimin za afara amfani da shi. Sabon tsarin ilimin an yi niyyar fara amfanni da shi inda za a koyar da yaddaake sabbin...
Jagoran juyin juya halin Musulunci ya bayyana cewa: Idan Amurka ta yi barazana ga tsaron kasar Iran, to lallai Iran ta kalubalance ta Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya jaddada cewa: Tattaunawa da Amurka ba wayo ba ce, kuma ba hikima ba ce, kuma gogewa ta tabbatar da hakan. Yayin ganawarsa da tawagar kwamandojin sojojin sama da na sararin samaniya na sojojin Jamhuriyar Musulunci ta Iran, Jagoran juyin juya halin Musuluncin ya jaddada cewa: Idan Amurkawa suka yi barazana wa Iran, to lallai za su fuskanci mayar da martani, idan kuma suka aiwatar da wannan barazanar, to za su fuskanci mayar da martani Iran mai gauni, kamar yadda idan suka kawo hari kan kasar Iran, za...
Manyan jami’an kasar Jordan sun gargadi Amurka cewa: Idan ta janyo hargitsi a Jordan, to zai mamaye dukkan kasashen yankin gaba daya Shugaban majalisar dattijan kasar Jordan Faisal Al-Fayez ya jaddada a ranar Juma’a cewa: Ana daukar kasarsa a matsayin ginshikin zaman lafiya a yankin Gabas ta Tsakiya, yana mai cewa; Duk wani hargitsin da zai iya faruwa a kasar, zai shafi kasashen yankin baki daya, yana mai jaddada cewa: Kasashen yamma, musamman Amurka, suna da cikakkiyar masaniya game da wannan lamari. Al-Fayez ya bayyana cewa, a cikin hirarsa da tashar talabijin ta masarautar Jordan kan manyan kalubale da kasarsa ta fuskanta a baya, amma ta yi galaba a kansu da karfi da kuma tsayin daka, tare da dogaro da...
A cikin daren nan aka dawo da wutar lantarki a Jihar Kaduna. Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Kaduna (Kaduna Electric) ya dawo da wutar be bayan kwanaki babu ita. An dauke wutar ne sakamakon yajin aiki da ma’aikatansa suka shiga tsawon kwana biyar. Kaduna Electric ne ke ba da wutar lantarki a Jihar Kaduna, Sokoto, Zamfara da Kebbi. Ma’aikaran sun janye yajin aikin ne bayan Gwamnan Jihar Kaduna Uba Sani ya shiga tsakaninsu da kamfanin.
Babban jami’in gudanarwa na kamfanin EDR Takale Uma, ya bayyana a ranar Alhamis cewa, kamfanin layin dogo na Ethio-Djibouti (EDR), yana samun ci gaba mai kyau, tare da kara karfinsa na jigilar kayayyaki zuwa kasashen waje. Uma ya bayyana a shafinsa na X cewa, “Tare da karin kan jiragen kasa da taragu, yanzu mun samu damar baiwa karin wurare hidima, mun fadada zirga-zirga daga Indode da Adama zuwa Mojo, Dire Dawa, da kuma wurin ajiye kaya na Sabata.” Uma ya kara da cewa, EDR yana maye gurbin tsoffin kayayyakin aiki da sabbi, da kuma gyara wadanda suka lalace, kana ya kara yawan jiragensa daga jiragen kasa takwas zuwa 21 da taragu 892 zuwa 935. Yana mai cewa “Jajicewar da muka...
An yabawa Gwamna Uba Sani saboda tsabtace harkokin hajji da kuma naɗa kwararru don jagorantar Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kaduna. Shugaban Kungiyar Yan Jaridu ta Kasa reshen Jihar Kaduna, Alhaji AbdulGafaar Alabelewe, ne yayi yabo yayin da jami’an kungiyar suka kai ziyarar ban girma ga hukumar. NUJ ta kuma bayyana naɗin Malam Salihu S. Abubakar a matsayin Shugaban Hukumar a matsayin wanda ya dace da mukami, inda suka jaddada cewa gaskiyarsa da bin doka da na da matukar muhimmanci wajen ci gaban hukumar. Alhaji AbdulGafaar ya ce hukumar ta samu nasarori masu yawa a lokacin hajjin da ya gabata, ciki har da maidawa kowane mahajjaci dala 50 daga kudin hadaya da suka biya a Najeriya. Ya kuma...
Masana’antar kera kayayyakin laturonin sadarwa ta kasar Sin ta samu ci gaba mai sauri a shekarar 2024, inda karin darajar manyan kamfanoni a fannin ya karu da kashi 11.8 cikin dari bisa ta shekarar 2023, kamar yadda bayanai suka nuna a hukumance a jiya Alhamis. Adadin kudaden shiga na manyan kamfanoni na wannan fanni ya karu da kashi 7.3 cikin dari a bara, idan aka kwatanta da shekarar 2023 zuwa yuan triliyan 16.19 kimanin dalar Amurka tiriliyan 2.26. a cewar bayanai daga ma’aikatar masana’antu da fasahar sadarwa ta kasar Sin. Hakazalika, alkaluman da aka fitar sun nuna cewa, a wannan lokaci, adadin ribar da wadannan kamfanoni suka samu ya karu da kashi 3.4 cikin dari bisa ta shekarar 2023 zuwa...
“Kowannen masu hada-hadar musayar kudade da aka san da zamansu da suka biya kudinsu na sake sabunta lasisinsu na 2025, an shawarce su da su rubuta zuwa ga Daraktan sashen kudi da tsare da sanya ido na Bankin, domin su karbi kudansu, da aka dakatar da biyan kudi, zuwa cikin asusunsu.” Inji Takardar Takardar ta bayar da tabbacin cewa, Bankin na CBN, har yanzu a tsaye yake akan kafarsawajen ganin ya samar da daidaito da bin ka’ida, musamman wajen gann ana gudanar da hada-hadar musayar kudade na waje a kasuwar musayar kudi.
Xi Da Mai Dakinsa Sun Shirya Liyafar Maraba Da Manyan Baki A Birnin Harbin
“Wannan sauye-sauyen an yi su ne, bisa manufar bin ka’idar shigar cikin Tashar, musamman domin a dakile satar hanyar shiga cikin Tashar ga manyan motocin da ba su gabatar da takardun shedar ka’idar shiga cikin Tashar ba.” Acewar Sanarwar. Kazalika, Hukumar ta NPA, ta bayar da umranin da a gaggauta wanzr da sauyin, biyo bayan sauya wadannan sabbin matakan da Hukumar ta yi, wanda za su fara aiki a cikin watan Fabirairun 2025. “Bisa wannan sauyin, daga yanzu daukacin manyan motocin da suka tunkaro domin shiga cikin Tashar, dole su kasance suna sanye da lambar manyan motocin, domin bin ka’idojin da Hukumar ta gindaya.” Inji Sanawar. “Dole ne manyan motocin su manna kwafin takardun shedar bayar bayar da kariya wato...
Wasu ’yan bindiga sun yi garkuwa da wasu ’yan mata shida masu shekaru tsakanin 15 zuwa 17 a yankin unguwar Pandogari da ke Ƙaramar hukumar Rafi ta Jihar Neja. Mazauna garin sun shaida wa Aminiya cewa, da tsakar daren Laraba ne ’yan bindigar suka kaiwa unguwarsu hari inda suka kashe wani ɗan banga mai suna Aliyu Aminu tare da yin garkuwa da ’yan matan. ’Yan fashin teku sun sace jirgin fasinja mutum 11 sun ɓace a Ribas Jirgin Amurka ɗauke da mutum 10 ya ɓace Mazauna yankin sun ce, maharan da suke da yawa sun shiga cikin unguwar ne daga yankin Birnin Gwari, ta Kwalejin fasaha ta Mamman Kontagora da ke Pandogari. Majiyoyi sun ce an kai ’yan matan da...
Bayanin da babban bankin kasar ta Najeriya ya fitar, ya bayyana cewa an sami wannan koma bayan ne a cikin makwanni uku da su ka gabata. Bayanin na babban bankin na Najeriya ya ci gaba da cewa, kudaden ajiyar Najeriya na waje da a cikin watan Disamba sun kai dala biliya 40,887, sun ragu, sun zama dala biliyan $39.723 daga ranar 31 ga watan Janairu 2025. An bayyana koma bayan ne a kudaden waje na ajiya da babban bankin kasar yake da su, da ya kamata ace a ranar 4 ga watan Febrairu ne za a fitar da kididdiga akan halin da kudaden wajen suke ciki,amma ba a yi ba. Bugu da kari wannanbayanin ya fito ne daga kamfanin dake...
Kotun manyan laifuka a kasar Tunisiya ta daure Shugaban kungiyar al-Nahdha ta masu kishin musulunci Rashid al-Ganushi, zaman kurkuku na tsawon shekaru 20. Haka nan kuma an daure wata ‘yar Jarida Shahrizad Ukkasha wacce take wajen kasar, zaman kurkuku na tsawon shekaru 22. Wata ‘yar jaridar da ita ma ta sami hukuncin dauri, ita ce Shuza Bilhaj, wacce za ta yi zaman kurkuku na tsawon shekaru5. Shi kuwa tsohon minista Lutfi Zaitun an yanke masa hukuncin zaman kurkuku na shekaru 35, sai kuwa mai magana da yawun ma’aikatar harkokin cikin gida Muhammad Ali al-Aruri, shekaru 13 a gidan kaso. Yayin da tsohon shugaban gwamnatin kasar Hisham al-Mashishi zai yi zaman shekaru 35 a gidan kurkuku. Tun a watan Disamba na...
Wanda ya jagoranci sallar juma’a a yau anan birnin Tehran, Hajjatul-Islam Kazim Saddiki, ya bayyana cewa: Trump yana yin baraza da tsoratarwa da cewa zai rage karfin da Iran take da shi a fagen fasahar Nukiliya da kuma matsayin da take da shi a cikin wannan yankin na yammacin Asiya, sai dai kuma ya kamata ya fahimci cewa kamar yadda shugaban da ya gabace shi ya yi kuskuren lissafi, to shi ma haka yake yi.” Limamin na Tehran ya kuma ce,Kamar yadda shugaban Amurka da ya gabaci Trump bai sami nasara akan Iran ba, shi ma haka ba zai cimma manufarsa ba. Hajjtul-Islam Siddiki ya kuma kara da cewa; Bai kamata ace muna kallon cewa ta hanyar abubuwa na zahiri...

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Kaddamar Da Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Lokacin Hunturu Ta Asiya Karo Na 9
An kaddamar da gasar wasannin motsa jiki ta lokacin hunturu ta nahiyar Asiya karo na 9 a yau 7 ga wata da dare, a birnin Harbin dake lardin Heilongjiang na kasar Sin, inda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya halarci bikin tare da kaddamar da gasar a hukumance. (Zainab Zhang)
Ma’aikata a Jihar Alaska da ke Amurka sun bazama neman wani ƙaramin jirgin sama na kasuwanci a ranar Juma’a da ya ɓace ɗauke da mutum 10. Kamar yadda hukumomin yankin suka ce, a wani sabon afkuwar da ya afku ta jirgin Amurka. Magungunan Jabu: ’Yan majalisa sun nemi yin hukuncin ɗaurin rai da rai Lakurawa sun kashe mutum 1 sun jikkata 6 a Kebbi Rundunar ’yan sandan Jihar Alaska ta sanar da cewa, jirgin samfurin Cessna Caraɓan mai fasinjoji tara da matuƙin jirgi ɗaya ne, an samu rahoton ne ranar Alhamis. Jirgin da ya tashi daga Unalakleet zuwa Nome da ƙarfe 4:00 na yamma agogon Alaska (0100 GMT) da ya ɓace. Biranen biyu suna da nisan mil 146 (kilomita 235)...
Kazalika, a Arewacin Nijeriya, Robar Tumatir mai nauyin kilo 25 yanzu, ana sanar da ita kan Naira 6,500. Shugabar kungiyar masu noman Tumatair da sarrafa shi ta kasa, Rabiu Zuntu ta sanar da cewa, an samu girbin Tumatir mai yawan gaske, duba da cewa; yanzu ana cikin watan Fabrairu, lokacin da ake samun yawaitarsa. A cewar tata, tarin yawan nasa ne ya sa aka samu faduwar farashinsa a kasuwanni, wannan dalili ne ma ya sanya, don gudun kada manoman su yi asara; suke sayar da shi kan farashi mai sauki. “Daga watannin Janairu, Fabrairu zuwa Maris; ana samun kwantan Tumatir, yanzu kuma muna da injinoni masu kyau na sarrafa Tumatirin, wanda hakan zai sa a samu raguwar farashin”, in ji...
Majalisar Wakilan Tarayya ta buƙaci babban lauyan gwamnatin tarayya da ya gabatar da gyare-gyare ga dokokin da ake da su da nufin zartar da hukunci mai tsauri da suka haɗa da ɗaurin rai da rai ga waɗanda ke da hannu wajen sarrafawa da shigo da magungunan jabu. Da kuma gaggarumin tara ga ’yan kasuwar da aka samu da laifin yin mu’amala da jabun kayayyaki. ’Yan bindiga sun mamaye masallaci da awon gaba da masallata a Sakkwato Lakurawa sun kashe mutum 1 sun jikkata 6 a Kebbi Hakan ya biyo bayan wani ƙuduri kan muhimmancinsa ga jama’a da ɗan majalisa, Tolani Shagaya ya gabatar a zauren majalisar a ranar Alhamis. Ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta kafa dokar ta-ɓaci kan...
“Babban shugaban sojoji da Babban mashawarcin shugaban kasa kan harkokin tsaro (NSA) suna aiki ba dare ko rana wajen tabbatar da wannan matakin, kamar yadda kuke gani muna sanya kumaji ga dukkanin rundunoni. “Sannan, an janye takunkumin hako ma’adinai a Zamfara, sannan wannan dalilin ne ya sanya muke ganawa a yau domin duba dukkanin bangarorin, inda muke da matsalar tsaro sosai sai mu ga yadda za mu kwato ayyukan,” Badaru ya shaida.
Wasu da ake kyautata zaton ’yan bindiga ne sun yi garkuwa da wasu masallata a wani masallaci a unguwar Bushe da ke Ƙaramar hukumar Sabon Birni ta Jihar Sakkwato. Waɗanda da ake zargin ’yan bindiga ne sun kai farmaki masallacin ne da asubahin ranar Alhamis a yayin da masu ibada ke yin Sallar Subhi da asuba. Lakurawa sun kashe mutum 1 sun jikkata 6 a Kebbi Yadda bom din Boko Haram ya kashe mutane a hanyar kasuwa a Adamawa Aƙalla masallata 10 da suka haɗa da Limamin ne aka ce an yi awan gaba da su a yayin harin. Jaridar Punch ta ruwaito DSP Ahmed Rufa’i, kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Sakkwato ya tabbatar da faruwar lamarin a ranar Juma’a....
Mayaƙan Lakurawa sun kashe farar hula ɗaya tare da jikkata wasu shida a yankin Gulma da ke Karamar Hukumar Argungua Jihar Kebbi. Da misalin ƙarfe 11 na dare ne maharan suka suka wa yankin yayin da mazauna suke tsaka da barci a ranar Alhamis suna harbe harbe-harbe. Shugaban Ƙaramar Hukumar Argungu, Aliyu Sani Gulma, ya bayyana cewa waɗanda maharan suka yi raunin harbi suna samun kulawa a Asibitin Tarayya da ke Birnin Kebbi, babban birnin jihar.
Sanarwar ta ci gaba da cewa, “A ci gaba da kokarin da rundunar ‘yansandan Jihar Imo ke yi na dakile ayyukan ta’addanci a jihar, jami’an shalkwatar sashen Okigwe tare da hadin gwiwar mazauna unguwar Ogii a ranar 3/02/2025, sun kama wasu mutum uku da aka samu da kokon mutum, kaza da fararen kaya a kan titin Okigwe-Umuahia Edpressigwe. “Mutum ukun da aka kama—Patrick Okoere, Ifeanyichukwu Anyaemeka, da Chukwuemeka Onyekachi 20—ana kan bincike a halin yanzu. Yayin da ake yi masa tambayoyi, Patrick ya bayyana cewa kawun nasa, Osunta Oko, ya nemi ya sayo kokon kan mutum. Ya yi ikirarin cewa ya same shi ne a bakin kogi a kan babbar hanyar Okigwe-Umuahia, yankin da rundunar ke samun labarin sace-sacen mutane....
Majalisar wakilai ta umarci kwamitocin sadarwa da harkokin cikin gida da su binciki haɗa lambar shaidar zama ɗan ƙasa (NIN) da layukan waya ba tare da izini ba da kamfanonin sadarwa ke yi. Wannan mataki ya biyo bayan ƙudirin da ‘yan majalisa Patrick Umoh da Julius Ihonvbere suka gabatar, inda aka buƙaci hukumar NCC ta ɗauki mataki kan duk wani kamfanin sadarwa da aka samu da laifi, tare da NIMC ta tabbatar da sahihancin haɗa bayanan NIN. Ana Shirin Kiranye Ga Ɗan Majalisar Da Ya Bar Kwankwasiyya Trump Ya Hana Maza Masu Sauyin Jinsi Shiga Wasannin Mata Umoh ya ce wannan mataki na iya haifar da damuwa ga ‘yan ƙasa, tare da jefa su cikin hatsarin satar bayanai, da damfara,...
Bama-bamai da mayakan Boko Haram suka binne sun kashe mutane biyu a hanyarsu ta zuwa kasuwa a Jihar Adamawa. Kakakin ’yan sanda a jihar Borno, ASP Kenneth Daso, ya ce mutane shida ne a cikin motar a lokacin motar da ta taka bam din a ranar Talatar bayan ta taso daga Karamar Hukumar Hawul ta Borno zuwa Kasuwar Garkida ta jihar Adamawa. “Ana zargin cewa ’yan Boko Haram ne suka dasa bama-baman, kuma motar da ke jigilar mutanen kauyen zuwa kasuwa a Garkida ta taka ta kuma ta fashe. “Wani dan shekara 25 ya mutu nan take, amma sauran fasinjojin an garzaya da su asibiti domin yi musu magani,” inji shi. Shugaban karamar hukuma ya biya wa al’ummarsa kudin wutar...
Sako daga Zara Murtala Ina mika sakon gaisuwata ga Iyayena da yayyena da kannena ‘yan uwana mata da maza wadanda muka yi makaranta tare da su, al’ummar Musulmi baki daya duk ina yi muku fatan alkhairi tare da fatan an yi Juma’a lafiya, Allah ya maimaita mana, ina gaida mijina tare da yi masa fatan alkhairi da fatan an yi Sallah Juma’a lafiya. Sako daga Nana Asma’u Musa Assalaikum alaikum Ina yi wa kowa fatan alkhairi tare da fatan an yi Sallar Juma’a lafiya Allah ya maimaita mana. Ina gaida iyaye na ina musu fatan alkhairi da fatan sun yi Sallar Juma’a lafiya Allah ya maimaita mana. Sannan kuma ina gaida ‘yan uwana yayyena da kannena da fatan,...
Majalisar Karamar Hukumar Jibiya a Jihar Kastina ta biya wa al’ummarta kudin wutar lantarki a kowane wata. Shugaban Hukumar, Alhaji Bishir Sabi’u na cewa nan gaba za a kammala aikin layin da aka ware musu na musamman na Kamfanin Wutar Lantarki ta Kasa (TCN). Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito shi yana cewa karamar hukumar ta riga ta hada garin Jibia da layi na musamman na TCN domin garin ya rika samun wutar yadda ya kamata. Ya ce, “duk da cewa an yi gwajin wutar, amma ba a riga an kammala aikin layin na TCN ba, kuma da ya fara aiki, al’ummar garin za su fara samun wutar lantarki tsawon awa 24.” ’Yan sanda sun sa dokar hana yawon...